← Book details Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 84

Sashe 48

Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

dariya yayi yace ni banda matsala kawaidai kituran sauran kudina ni kuma zan sallameta
tsaki tayi tana katse kiran tazauna bakin gado tana share zufan da takaryo mata se tsinema JJ take

Juyawa aysha tayi tafita batare datace komai ba tanufi bangarensu

Haduwa tayi da jamilu zai fita aiki fadawa tayi kan jikinsa tana kuka

Rikota yayi atsorace yana tambayar meyafaru

Cikin kuka tagayamasa duk abunda yafaru da tafiyar AK wurin asma'u

zama yayi kan kujerar Palo yana cire hularsa yace ina bazai yuba gaskiya haka kawai muna gani munaji Abu zai rikice mana wallahi natsani yarinyarnan ga dukkan alamu AK yafara sonta

Sadiya dashigowarta kenan palon tace yana fara kulata kuma zata fara zazzago Ya'ya daga nan kuma muntashi aiki daga karshe ayi waje damu

Kallon aysha yayi yana fadin kinsan Wanda sarah tabama aikin
gyada kai tayi tana share kwalla

murmushin mugunta yayi yace jeki satomun numbansa amma karki bari tagane

Fita tayi cike dajin dadi tanufi dakin sarah da dubara tasamu tadauki numban JJ tadawo bangarensu

Karban numban uncle jamilu yayi yakira bugu biyu yadaga yana fadin waye ne

Canza murya jamilu yayi yafara fadin

Sunana basiru nasan sarah tabaka aiki akan kasace khadeeja bai mistake kasaci yayarta yanzu kuma tace maka kasaki yarinyar yin haka kuma hadari ne babba awajanka

Katseshi yayi dafadin to malam basiru kake ko wa ??
abunda kakira ka gayamun kenan ?

Dariya uncle jamilu yayi irin tasu tamanya sannan yace JJ nima fa dan ahnnu ne saboda haka aiki zanbaka

bansan konawa sarah tabaka ba amma zan linkamaka konawane ka kashemun yarinyar kafin AK yaje wurin

Dariya JJ yayi yana hura sigari yace angama yallabai irinku mukeso masu bamu aiki kai tsaye

dariya jamilu yayi yace kardamu JJ yanzu zakaji alert narabin kudinka sauran kuma ina ganin gawarta zakagansu

cike da farin ciki JJ yagayamasa kudin da account numban daza'a turamasa kudin sannan suakayi sallama nan take ya dibi yaransa suka nufi dajin da asma'u take

kallonsa aysha tayi da mamki tace dady meyasa kace sunanka basiru

Dariya yayi yace yarinya ai awannan harkar wawayene kawai ke fadan sunansu nagaskiya kinga yanzu koda wani Abu yafaru yansanda suka tuhumeshi zaice basiru ne yasashi to waye basiru??

Dariya sukasa gaba daya cike da farin cikin burinsu yakusa cika

gudu AK yake amota kamar zai tashi sama yana mamkin nisan dayayi amma har yanzu arrow din baidaina nuna hanya ba seda yakai inda motarsa bazata Shiga ba yayi parking dinta yafara tafiya akafa yana ma Ahmad kuatancen inda yake

Yayi nisa sosai adajin ahmad yakirasa awaya yace gaskiya ya jirasu gasunan zuwa sun isko motarsa awani wuri shi sam bai yarda da .....

Hello hello AK yafarayi dan baiji karshen maganar ahmad ba
Jin shiru yasa yadago wayar yaduba zaro ido yayi ganin wayar amace yakunna kuma taki tashi

Hannu yadora akai yana fadin namutu ni Abidi yanzu taya su ahmad zasu San inda nake cikin wannan dajin

Jiyayi kamar yakoma wurin motarsa se kuma ya tuna baisan halin da chitti take cikiba

Kallon agogon yayi sannan yayi shahada yabi hanyar dayake nuna masa

har yamma tayi amma AK baikaiba har yafara sarewa da lamarin yana tsinema agogon ahmad shikadai se magana yake gashi ya gaji fatanshi daya allah d
Sa ba banzan agogo bane wannan yabi ta karyan turawa zai kashe kansa

jin karan agogon yakaru yasa yayi saurin kallonsa dariya yayi cike da farinciki yanufi inda yanuna mai baiyi tafiya mai nisa ba yahango runfar du JJ kuma nan agogon ya nuna masa

Cikin aljihu yasaka agogon cikin sanda da dabara yakarasa wurin kwance suke suna bacci suduka bayan sunsha giya sun bugu

ahankali yake takawa har yatsallekesu yashiga runfar can gefe ya hangota azaune tacusa kai aguywa tana kuka saurin karasawa yayi wurinta yana murmushi cikin rada yace chitti!!!

kamar amafarki taji muryansa saurin dagowa tayi dan ganin koda gaskene
zagayowa yayi tabayanta ya kuance mata daurin kamar jira take tafada jikinsa tana fashewa da kuka rungumeta yayi nadan lokaci sannan cikin rada yace kinga tashi mutafi idan munbar nan wajan se kiyi kukan

dariya tayi ta tashi tana fadin ya akyi kazo nan Jan hannunta yayi yana mata alama tayi shiru

suna fitowa sukaga ba yaran JJ awurin zaiyi magana kenan yaji ansamai bindiga abayan wuyansa cikin muryan mashaya JJ yace sannu da kokari AK

hannayansa yadaga sama yana juyowa ahankali itama asma'u tayi yanda taga yayi atsorace jikinta se rawa yake

kara saita bindigarsa yayi yana dariyar keta yace kayi Babban kuskure daka shigo gonata doka tace idan har nakama mutum yayi kokarin guduwa to kisa ne hukuncinsa saboda haka

saita asma'u yayi da bindigarsa yana dariya yace kiyi addu'ar karshe yan mata

saurin shiga gabanta AK yayi yana kallon JJ yace

dakata dan allah kayi hakuri kabarta ta tafi lafina ne nizaka kashe ba itaba katausaya mata mana mace ce fa mezaka samu idan ka kasheta tukunna ma akan wane dalili ka kamata kafada konawa kake so zan baka amma kabarta ta tafi

Kallon yaransa yayi suka kwashe da dariya seda sukayi mai isarsu sannan yasaita bindigar kan AK yana fadin to ai kaima ba kyaleka zanyiba tunda har kaganni kuma kaga mabuyata to dele kamutu

janyo hannunsa asma'u tayi tadora bindigar kan goshinta cikin kakkawsar murya tace zaka iya kasheshi amma sedai kafara kasheni tukkuna

saurin janyota AK yayi tafado jikinsa yana fadin chitti mekikeyi hakane

Dariya JJ yayi yana kallon yaransa yace haba tundazu ina mamakin meyasa AK zai sadaukar da rayiwarsa yashigo wannan dajin saboda wata yarinya Ashe masoyane hahahhaha

juyowa yayi yana kallonsu yace Romeo da Juliette banada isashshen lokaci kuazabi wazan fara kashewa acikinku ko kuma ni nazaba

Shiru suakyi suna kallon juna hawaye nabin kuncin asma'u tana tuna halin da iyayensu zasu shiga idan suka ga gawarsu atare

Shima AK abunda yake tunani kenan

Dariya JJ yayi ya umarci yaranshi dasu rike mashi AK shikuma yasaita bindigarsa kan asma'u

Sam bata damu da bindigar ba hankalin nakan AK dake kokarin kwace kansa daga yaran yana rokon JJ dayarabu da ita

kallon juna suke lokaci guda suna tuna rayuwar dasukayi abaya hawaye nazuba akan kuncinta amma da murmushi afuskanta tana kallon AK

kallonta yake shima baisan lokacinda hawaye ya zubo mashi ba cikin rawar murya yace JJ dan allah na rokeka kabarta ta tafi idan ma zaka kasheta dan allah kafara kasheni tukkuna I can't watch her dying

dafe goshi JJ yayi yana kallon AK yace

aK kamun shiru ni idan ina aiki banason hayaniya

Kallon yaransa yayi yace gayu gaskiya tunda nake bantaba kashe masoya ba kuma gaskiya bazan iya barinsu sutafi ba dole ne su mutu ya za'ayi

dariya sukasa dayan yace oga to mezai hana kabani bindigar nagama musu aiki

Shiru yayi nadan lokaci sannan ya tuntsire da dariyar mugunta yace gawata dabara

Bishiyar kusa dasu yanuna musu yana fadin kudauramun yagiya ajikin waccan bishiyar zamuga idan dagaske bazai iya ganinta tana mutuwa ba

Nan take suka daura yagiya kamar yadda yace hannayensu yasa suka daure sannan suka nufi wurin bishiyar dasu

duk yanda AK yayi kokarin kwace kansa amma abun yagagara sarkin yawa yafi sarkin karfi ga bindiga ahannunsu ita dai asma'u tuni ta saduda tagama sallamawa kawai mutuwa zasuyi to meyasa zata dami kanta

Banda kuka ba abunda take se rokonsu take surabu da AK sukasheta amma ko kallonta basuyi ba

har dare yayi ahmad nayawo da yansanda adajin amma sun rasa ta inda zasu nemesu gashi wayan AK akashe ba yanda baiyi da yan Saddan ba akan suci gaba da nemansu amma sunki wai dare yayi bazasuyita shiga cikin daji ba zasu koma idan sun shirya zasu zo aci gaba da nemansu

Bayanda ya iya haka yahakura jiki asanyaye yakoma gashi khadeeja se kiranshi take tana tambayar yagansu sedai yabata hakuri yace zasu gansu

acan gida kuwa gaba daya hankalinsu yakara tashi ganin ahmad yadawo batare dasu AK ba Umma ma seda ahmad yakira doctor yamata alluran bacci gudun kar ciwonta yatashi Abba kuma tuni yafada amasallaci atayasu da addu'a

Khadeeja kwa banda kuka ba abunda take da kyar ahmad ya lallasheta tayi shiru

Haka ma bangaren grany da inna ameena abinci da kyar sukeci dan gaba daya gidan ba dadi

Ita kanta Sarah tashiga damuwar rashin AK dan tasan JJ bayada mutunci zai iya hadasu gaba daya yakashe gashi tana kiransa baya dauka daga karshema yayi blocking numberta

Aysha ma tadamu ganin AK baidawo ba amma da jamilu yakira JJ seyacemasa AK baijeba asma'u kuma yakasheta kawai yajira gawarta nanan zuwa

Se alokacin hankalinsu ya kwanta sukaci gaba da nuna fake damuwansu akan rashin dawowarsu

kama asma'u sukayi suka ratayeta ajikin yagiyar ga hannayenta adaure
Dai cikin yaran yana rike da kafafunta wanda daga yasakesu wuyanta zai sarke ajikin yagiyar

Kuka AK yake kamar karamin yaro bashiri yasa karfinsa gabadaya yakwace kansa aguje yakarasa wurinta yana kuka yana rokonsu dan allah sukwanceta

dariya sukasa gaba daya suna kallonsu

yaron dake rike da ita yace oga nagaji pah yasin zan saketa

karasowa JJ yayi kusan AK yana fadin zaka iya taimakonta ai dasauran dan lokacinda yaragemuku kafin wahala takarasaku

durkusawa AK yayi akan guywowinsa aka Dora kafafuwan asma'u akan kafadunsa tayi tsaye

Dariya sukayi dai cikin yaran yace oga kana ganin zai iya juran daukanta kuwa

"To ai hikimar abun kenan shi dakanshi zai kasheta idan kuma bai kasheta ba ita zata kasheshi
Haka zamu barsu su kwana har gobe idan basu mutu ba dasafe zamu kashesu kafin mu barnan

juyawa sukayi suka koma gefe guda suka fara shan giyarsu suna fira

Hawaye ne ke zuba akan kuncin asma'u kamar anbude panpo har suna diga sama kan AK

ahankali yadago kansa yana lekenta yace chitti yayyafi akene kece asama zaki fini sani naji Abu nadiga akaina

Cikin muryan kuka tace ABI why did u come

"aw abunda ma zakice kenan maimakon kigode mun nazo taimakonki shine zaki ce meyasa nazo ko

"To yanzu me zuwannaka ya anfanar ni bantsira ba gashi zamu mutu gaba daya

murmushi yayi yace bazaki mutu ba chitti kafin Nazo nan wurin seda nabiya wurin Umma namata alkawarin zan maidaki gida to koda zan rasa raina insha allahu se kinkoma gida karkidamu
Chapter 48 · 0% Book details