← Book details Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 56 OF 84

Sashe 56

Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kallonsa asma'u tayi da gefen ido tana wani malalacin murmushi tace ohh kenan dama akwai masu neman dukiyar bani kadai bace

Zaunawa yayi yana share zufa dan se alokacin yagane subutar baki yayi

Tashi tayi tsaye tana kallon AK tace AK I know it hurts amma ya zakayi se hakuri karike wa innan takardun awajanka original din yana wajena idan kuma bakayarda ba zaka iya kai abun kotu I am ready for it

tana kainan taja akwatinta tayi bangarensu tana fadin I need to have some rest dan allah duk mai magana yajira zuwa gobe dasafe

Baki bude suka bita da kallo har tahaye sama sannan suka jiyo suna kallon juna tafa hannu inna ameena tafarayi tana salati tace oh ni ya'su jama'a kutayani ganin wannan abin al'ajabi

Zaunawa grany tayi rike da wayarta tana Neman numban Umma tace nidai gaskiya wannan Abu ya dauremun kai bari mu kira ummarta inmu tamana wasa da hankali ta rainamu ai bazata ma uwarta ba ko?

Umma nadauka tasanar da ita asma'u tadawo cike da mamaki tace grany asma'u fa kika ce

Tabe baki grany tayi tace aha'ab ai se kuzo kuga ikon allah

Shidai AK tunda ya zauna bai tashi ba ganin abun yake kamar almara wai chitti ta malakke dukiyarsa kuma wai karya take bata sonsa dafe Kansa yayi aransa yana fadin inna lillahi wa inna ilaihiraji'un

ba'afi minti talatin su Umma da khadeeja suka shigo gidan cike da farin ciki tanufo grany tana fadin grany ina asma'un take dagaske asma'u tadawo ina aka ganta

Shan gabanta aysha tayi tana fadin Umma yarki ba bata tayi ba kuma ba wani Abu yasameta ba tafiya tayi har na tsawon wata daya batare da sanninku ba

Cike da mamaki Umma take kallon mutanan palon dasukayi cirko cirko suna kallonta

Juyowa tayi tana kallon aysha tace tafiya kuma kamar ya ina taje

dariya aysha tayi tana tafa hannu tace ke uwarta baki sani ba taya za'ayi ni insani

Juyo da ita khadeeja tayi ahasale tace ke kisan abunda zai rika fitowa da bakinki kar kimanta da mahaifiyata kike magana

kwace hannunta tayi tana fadin ohhh Ashe dai ba dadi to awurin yayarki nakoya

Dawo da kallonta tayi kan Umma tana girgiza kai tace Umma dama tarbiyar da kike ikrarin kin bama yarki kenan kullun kina yabonta she is nice she have a good heart yarki diamond yarki gold to yau munga asalin wacece ita

katseta Umma tayi dafadin ke karki mun rashin kunya kinji ko

karasawa tayi wurin grany tazauna tana fadin grany wai meke faruwa ne ya naganku haka

ajiyar zuciya grany tasauke tashiga bata labarin abunda yafaru

Juyowa tayi tana kallon AK cike da mamaki tace kun tabbata asma'u ce kuwa dukiya fa kukace asma'u dako kudinta ma bai dameta ba bare har takai ga malakke wannan dumbin dukiya kuma wai ta mijinta kai gaskiya.....

Katseta uncle jamilu yayi yana share zufa yace to karya zamu maki kenan badai kinyi karatu ba to ga takardunan ahannun AK duba ki gani kuma wallahi bazata sabu idan shi ya kyaleta to ni bazan barta ba haka kawai shekara nawa ina ......

saurin taboshi sadiya tayi tana mai alama ya iya bakinsa

gyaran murya yayi yace ummm shekara nawa yayi yana wahala har yatara wannan dukiyar shine lokaci guda zata rabashi da ita kuma mubarta haka kawai

Umma dai har yanzu bata gamsu da bayaninsu ba nan take ta aika dai cikin ma'aikatan yakira mata asma'u

Seda tadauki tsawon lokaci sannan ta fito wannan karan idonta yayi jajir daganinta kasan taci kuka

Tunda daga nesa Umma da khadeeja suka saki baki da hanci suna kallonta har ta iso palon ta tsaya cak tana kallonsu

Saurin karasowa khadeeja tayi ta rungumeta tana kuka tace ammah ina kika shiga mukayita nemanki bamu ganki ba meyasa zaki tafi kibarmu kin kwsan halin da muka shiga na rashinki duba kiga yanda Umma tadawo kullun batada lafiya saboda tunaninki

Shiru tayi batace komai ba tana kallon Umma sama da kasa

ahankali Umma takaraso wurinta tana kallon shigarta da mamaki tace asma'u meyasameki haka ya kuma naganki da wannan shigar ina kika tafi batare da kinsanar damu ba

Kauda kai tayi batare datace komai ba

riko kafadunta Umma tayi tana kureta da ido tace asma'u meke damunki ne anya kuwa lafiyarki kalau ko dai abunda grany tafadamun dagaskene wai kin.....

Katseta tayi dafadin Umma kinsan dai grany bazata maki karya bako to dagaskene

Shocking.....😱

Kallon kallon aka fara tsakanin mutanen palon banda AK da ko dagowa baiyiba bare ya kallesu

Kallon khadeeja Umma tayi sannan takalli asma'u tana so tayi magana amma takasa

Riko hannunta khadeeja tayi cikin rawar murya tace ammah meyake damunki ne ....Umma ...kike ..yima magana haka kai tsaye

juyowa asma'u saitin Umma amma kanta akasa dan takasa hada ido da ita cikin dakewa tace Umma wannan fa ba wani Abu bane kawai dukiyar na mallaka amma kuma ni bance zan koresu daga gidan ba kawai dai.....

Hannu Umma tadaga zata mareta khadeeja ta rikota tana fadin a'a Umma kibarta kawai ni na tabbata akwai abunda yake damunta amma ko za'a akasheni bazan yarda cikin hayyacinta take ba something is wrong with her

Nuna ta Umma tayi da yatsa cikin kakkausar murya tace to wallahi bari kiji idan ma hauka kike ko kwaya kika sha to kisani ni nafi karfin ki tozartani nabaki nan da gobe ki mayar masa da dukiyarsa inba haka ba kuwa sedai kinemi wata uwar ba niba .....

tana kainan ta juya afusace tafita daga gidan khadeeja nabiye da ita

juyawa asma'u tayi aguje ta koma bangarensu tana shiga ta turo kofar hade da sulalewa awurin tafashe da wani irin kuka mai ban tausayi kuka take sosai har nunfashinta nadaukewa seda tayi mai isarta sannan ta tashi tana dafe kai ta wuce daki jacket dinta ta cire tarike ahannu ta tsaya gaban dressing mirror tana karema kanta kallo wasu sababbin hawaye nazubowa daga idonta tajima atsaye kafin ta wuce bathroom tayo alwala tazo ta zunbula hijabinta tayi sallah tajima azaune tana adduo'inta kafin ta tashi takoma kan gado tazauna tafara aiki a laptop dinta

bayan fitar Umma uncle jamilu ya mike afusace yanufi bangarensa sadiya da aysha sukabi bayansa

Daga nan kowa ya watse jiki asanyaye wasu kuma naji kamar su mutu dan bakin ciki

AK natashi wurin ahmad yanufa ya zayyane masa duk abunda yafaru

Dafari bai yardaba seda AK yanuna masa takardun sannan ya tabbatar cewa dagaskene cike da mamaki yace ammah har yanzu abun yana dauremun kai I mean...... why will she do that ?

ajiyar zuciya AK yasauke yana kuantar da Kansa kan kujere yace bansan meyasa tayi hakan ba amma I am sure she is hiding something tabbas ba banza ba chitti bazata taba yaudarar wani bama bare ni kawai dai dalilinta nayin hakan ne bansaniba

"To yanzu miye abun yi

"Ba wani abunyi ahmad ko ina akaje tafimu gaskiya saboda akwai sa hannuna akan takardun so banida ikon dazan kwato dukiyata amma abunda yafi bani haushi shine gaba daya komai yakoma kan sunanta hatta kudina na bank da da komai nawa ya daina aiki lokaci guda tamaidani fakiri wallahi yanzu dubu dari kawai nake magani itama a ranar da ta tafi nacirota zan yi wani Abu da ita namanta

Tagumi ahmad yayi cike da al'ajabi yana nazarin wannan al'amari amma shi kanshi bai yarda cewa asma'u zatayi haka ba yana zargin akwai abunda take boyewa ba banza ba

Tashi AK yayi yanufi hanyar fita yana fadin muje muyi sallah daga can muje wurin su Umma mudubata I know she must be worried

awurin Umma suka wuni ranan suna kuantar mata da hankali sannan suka tabbatar mata da cewa akwai dalilin dayasa asma'u ta kwace dukiyar AK ba banza ba kawai dai subita ayanda tazo asannu zasu gane dalilinta nayin hakan
[19/07, 17:05] Hubbey Frd Ameena Kn: AK yana zaune office din ahmad kamar kullum wayarsa ce ahannunsa yana dannawa

tsaki ahmad yayi cike da takaici yace

Friend wai meke damunka ne kwana biyu gaba daya kacanza kafita hayyacinka bakada aiki sedanna waya sekace wani bakauye

Baidago ya kallesa ba bare yasa ran zai tankasa

Karasowa yayi wurinsa yazauna cikin sassanyar murya yace

Base kafada ni nasan akwai abunda yake damunka idan kana ganin bai zama dole nasani ba fine u can keep it to ur self amma dan allah karage wannan damuwar tana damuna

murmushi yayi yana ci gaba da kallon wayarsa bai ce komai

Dafe kai ahmad yayi yana salati sannan yadago yana fadin wai dan asma'u tace tana sonka ne kake wannan abun

Girgiza kai yayi har yanzu dai yana kallon wayarsa se murmushinsa da yakaru har ana ganin fararan hakoransa

Cike da takaici ahmad ya kwace wayar yana fadin wai uban me kake kallo awayar nan ne dayake......

Cak ya tsayada maganarsa yana kallon photon asma'u dake kan screen din wayar da alama bacci ma take yadauketa photon yayi kyew sosai ga Zara zarn eyelashes dinta dasuka kwanta da dan karamin lips dinta da yayi kamar tasa pink lipstick kanta ba dan kwali gashinta duk ya bazu akan pilo sauran kuma akan fuskarta

Juyowa ahmad yayi da mamaki yana kallonsa baki bude yama kasa magana

Se can yayi yar dariya mai sauti cike dafarin ciki yace ohh my god friend are u in love ?

Hannunsa yasa yadan daki goshinsa kadan yana fadin I was so stupid ya akayi nakasa gane halin da kake ciki tun tuni

hannu AK yamika mai batare dayace komai ba ahmad yabasa wayarsa yana fadin friend kace wani Abu mana ur silent is killing me

tashi yayi yafita daga office din yana rike dawayarsa gam ahannunsa baiko kalli ahmad ba bare yayi magana

Da kallo ahmad yabisa rike da baki yace ohhh ikon allah kaikuma haka soyayyar tazo maka ni har ma kabani tausayi

komawa yayi yazauna kan kujerarsa yana Neman numban khadeeja dan yamata albishir

tafiya asma'u keyi akan hanya tana rangaji da kyar take daga kafarta hawayenta kuma har basa bare tana ganin hanya da kyew bata damu da sharesu ba dan gaba daya jikinta ya mutu lokaci guda maganganun da taji suna dawomata
Chapter 56 · 0% Book details