← Book details Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 33 OF 84

Sashe 33

Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Barin wurin asma'u tayi tana fadin sirrin ma'aurata ne baizama dole ke kiji ba

Da kallo tabita tanaji kamar ta kurma ihu

Gyada kai tayi tana cije lebe tace dole nadau mataki naga alama ina sake dabaki zan jini asalansa ....

Shigowar Ahmad da sauran abokanansu ne yakatsemata tunaninta nan take aka hau shewa ana murna banda ango dakana ganinsa kasan yana cikin damuwa

Tunda yashigo sarah takasa dauke idonta akansa tana ji ba macan da takaita Sa'a saboda ahmad daban ne yahadu iya haduwa

Dining suka nufa gaba daya suka fara cin abinci suna fira

Kitchen aysha taja sarah tana fadin amarsu zo mu dakko masu dambun naman da grany tace aba abokanan ango gift idan sunzo

Da kallo asma'u tabisu dan tasan wata gulmar zasuyi

Tashi ahmad yayi yanufi bangaren grany yazo wucewa kenan yaji suna magana

Aysha tace wallahi yau senakeji nafiki farin ciki mun kusa rabuwa da annoba

Dariya sarah tayi tace ai jira kawai nake adaura aure muyi waje da ita

Dariya sukayi suka tafa ...

Girgiza kai yayi yana fadin kai inaaaaa bazai yuwu ba bazan yi biyu babu ba

Narasa khadeeja kuma bukata bata biyaba auren asma'u yamutu

Wayanshi yaciro yana kiran khadeeja amma bata dauka

Fita yazoyi yahadu da asma'u zataje wurin khadeeja taga yatake

Shan gabansa tayi ta tareshi tana fadin ina kuma zakaje bayan lokaci yayi idan ma kana tunanin khadeeja ne to koma wurinta zanje yanzu

Zaiyi magana yaga sarah atsaye tana kallonsu

Runtse ido yayi yana cije lebe yajuya Yakoma ciki """"

Ur's.......
*MHD*

[18/07, 15:04] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚
👨‍👧 _DOMUN KANWATA_ 👩‍👧

Na ( *Maryam Mhd* )

( _nasadaukar dawannan page din gareki Aisha(anna) da kuma Dr Aisha tnx for ur support
Sa'ata da xee Allah yabar zumunci )_

9⃣5⃣

Bayan anci ansha AK yafara Neman ahmad amma bai gansa ba yakira wayarsa yafi akirga amma baidaga ba daga karshema ya kashe wayar baiyi tunanin wani Abu ba yaje yatambayi sarah ko yagayamata Inda zaije

tace bata ganshiba nan fa aka fara nemansa gashi kowa yataru amasallaci ana jiransu adaura aure

Hankali tashe yake kiran wayar ahmad amma akashe

Sarah dake gefenshi tana rusa kuka ta mike zunbur tana fadin ina asma'u

Juyowa sukayi shida aysha suna kallonta

Aysha tace kina nufin tasan inda yake

Bata bata amsa ba tafita aguje tasauka kasa tana kwalama asma'u kira

Amma bata ganta ba
Jan hannunta AK yayi yamaidata sama ganin yanda mutane ke kallonsu

Dakinsa yakaita yana fadin ki kuantar da hankalinki sarah nasan bai yi nisa ba kila wani uzuri ne yafitar dashi

Tureshi tayi tafada kan gado tana kuka tace Yaya duk laifinka ne kai kaja haka tafaru kasake mata dayawa ka aureta ne dan kahukunta ta amma kabiyemata kana mata wasa kana mata dariya kana fira da ita shiyasa tasamu damar yin haka yanzu gashi tarusa mun farin cikina kuma naganta tana ma ahmad magana dazu nasan ita tacanza mai ra'ayi yafasa aurena wallahi bazan barta ba sena kasheta

Ahasale yafita daga dakin yana banko kofar dakarfi

Aysha tazo binsa kenan tahango wata farar takarda akan dressing mirror har tawuce se kuma tadawo tadauki takardar ganin ansa

from ahmad to AK
Yasa tafaki idon sarah tafara karantawa kamar haka

Nasan lokacinda zakaga wannan takardar kana nemana friend
kayi hakuri naso na sadaukar da soyayyata na auri sarah amma daga baya na fuskanci hakan bashida wani anfani
Nadauka idan nahakura da wacce nakeso na aureta komai zai wuce amma naji da kunnena tana cewa zaka saki asma'u idan na aureta

Friend kayi hakuri naboye maka gaskiyar lamarin amma ni ba asma'u nakeso ba
KHADEEJA kanwarta ita ce budurwata da ita muke soyayya baku fahimci abun yanda yadace bane

I am really sorry amma bazan iya gyara daya nabata goma ba

Bazan iya auren sarah narabu da khadeeja ba

Kai kuma daga karshe karabu da asma'u

Nasan zaka ji haushi amma kayi hakuri

I am sorry but i can't

Ur friend ....ahmad

Zufa ce taji tana karyomata lokacinda tagama karanta wasikar cike da tashin hankali take fadin na shiga uku ni aysha yanzu dama ba asma'u bace budurwan ahmad

boye takardar tayi aranta tana fadin ai wallahi bazan bari kusan da wannan zancan ba dama can naga takeken asma'u tafara jan hankalin AK inaga inyaji gaskiyar maganar nasan bazai saketa ba

AK na sauka kasa ita kuma tashigo hannunta yaja dakarfi yanufi sama da ita
Yanayin da taganshi aciki ya tsoratata tana magana amma yayi banza da ita se fizganta yake da karfi har tana neman faduwa

Sadiya takalli ladidi tana fadin wai meyake faruwa ne

Dariya ladidi tayi tace ango ne ya gudu annemesa anrasa

Tashi tayi tanufi bangaren grany tana murmushin mugunta tace bari naje nagayama tsohuwar can Allah sa ma hawan jininta yatashi tamutu muhuta

Tana isa bangaren grany tafara kukan munafunci tana fadin grany munshiga uku za'akunyataki gaban baki

Daure fuska grany tayi tace kunya takare akanki meyafaru

Ahmad ya gudu yace yafasa auren sarah

Jiri ne yadibi grany inna ameena ta tarota tazaunar da ita kan kujera

Bayan wani dan lokaci tasauke ajiyar tana salati tace shikenan haka Allah yakaddara amma ahmad bai kyewta ba yasan bazaiyi auren nan ba meyasa bai fada tun wuri ba gashi yanzu muntara mutane mezamuce masu

Cike da takaici sadiya ke kallonta ahasale tace wai grany bakiji komai ba

Inna ameena tamaka mata harara tace to munafuka mai bakin labari me kike so taji

Juyawa tayi tana jan tsaki tabar wurin

AK na shiga daki ya wurga asma'u kan gado kusa da sarah cikin kakkausar murya yace daga ina kike ina ahmad

Cikin rawar murya tace meyafaru ...

Shako wuyanta sarah tayi tabaya tana fadin munafuka tambaya ma kike meyafaru ke baki ji kunya ba da aurenki amma kinabin wani wallahi se kinfadamun ina ahmad dina yake

Da kyar AK ya kwaceta a hannun sarah

Kallonta yake da rinannun idanuwansa yace tambayar ki nake ina ahmad kigayamun ko yanzu in cimaki mutunci abainan jama'a

Fashewa tayi da kuka tarikoshi tana fadin dan allah kayi hakuri wallahi bansan inda ahmad yakeba Ni yanzuma nashigo gidan nan ban San meyake faruwa

Nufota sarah tayi aguje tana fadin wallahi karya kike kinsan inda yake dazu batare naganku ba narantse idan baki fadi inda yake ba sena kasheki

Riko hannunta AK yayi sannan yakalli asma'u yana daka mata tsawa yace get out of my room

Fita tayi tana kara fashewa da kuka

Zaunar da sarah yayi bakin gado cikin sigar lallashi yace calm down sarah koma ina ahmad yake zan nemosa kuantar da hankalinki kar mutane sugane halin da ake ciki

Cikin sheshshekar kuka tace to Yaya adaura auren mana ai ba dole se yana nan ba

Girgiza kai yayi yana share mata hawaye yace ba yanda za'a daura aure batare da amincewarsa ba sarah kidan bani lokaci zansan abunyi

Kuantawa tayi akan gadon tana rera kukanta mai cin rai

Tsaye yayi yana kallonta nadan lokaci kafin yasauke nannauyar ajiyar zuciya yana fita daga dakin

Asma'u nafita takira wayar khadeeja tana tambayr ko taga ahmad

Da mamaki khadeeja tace a'a ammah bangansa ba meyafaru

" khadeeja ahmad bayanan annemesa anrasa kuma ana kiransa baya dagawa
ko yakiraki ne

" bansaniba naga kiranshi dazu amma bandauka ba nakashe wayar

" OK to ki kirashi yanzu muji ko zai daga

abangaren Momy ma Neman ahmad take har zata kira AK taji wayanta na ringing tana dubawa taga ahmad

Bayan tadauka tayi sallama

Cikin wata iriyar murya kaman mai shirin fashewa da kuka yace

Momy nafasa auren sarah khadeeja nakeso kuma ita zan aura kome zai faru yafaru nagama yanke hukunci

Murmushi Momy tayi tace
Ahmad kayanke hukuncin da yadace akurarren lokaci

amma ba komai haka allah yakaddara

Jin anturo kofa yasa ta ijiye wayar

AK ne yashigo cike da damuwa ko gaisawa basuyi ba yace Momy ina ahmad

"Banganshiba AK rabona dashi yatafi wurinka....

Bata karasa ba ya juya yabar palon

Yana fita ta kira Ahmad tace AK yazo nemansa

Kiran AK yayi awaya bugu biyu yadaga ahasale yace ai bandauka zaka iya kirana ba ahmad meyasa zaka mun haka meyasa kake so ka tozartani ne

Wai natambayeka miye laifin sarah da kake wulakanta ta

Cikin rawar murya ahmad yace AK katsaya kasaurare ni bakaga wasika...

Bai karasaba ya katseshi dafadin
Mezaka gayamun Wanda bansani ba
Bazaka iya auren sarah ba kanada wacce kake so
Soyayya soyayya

Koba abunda zaka gayamun kenan ba

To tsaya kaji zan iya yafe komai amma bana abunda yashafi familyna

Yana kainan yakatse wayar hade da dukan sitiyarin motar da karfe

Ahmad ma kuance yake acikin motar sa ga idonsa yayi ja kana ganinsa kasan yana cikin damuwa
Wayarsa ne yafara ringing yana dubawa yaga my flying bird

Saurin daukar wayar yayi yana fadin haba deeja meyasa zakiki daukar wayana kikasan mezan gayamaki

"Mezaka gayamun kwa banda kafasa auren sarah
Kasan halin da kajefa yayata aciki kuwa wannan shine sonda kake ikrarin kana mun ...

" deeja please dan allah kisaurareni inaso muhadu dake maganar bana waya bane

Shuru tayi nadan lokaci kana daga baya ta amince ya gayamata inda zasu hadu

Tana kashe wayar takira Asma'u tagayamata

Asma'u tace taje suhadu itama zata zo wurin suyi magana

Ganin magariba tagabato yasa akaba mutane hakuri akan anfasa taron bikin se wani lokaci

asma'u na idar da sallar magriba tafito danufin tafiya wurin su ahmad tahadu da aysha

Riko hannunta aysha tayi cikin sassanyar murya tace asma'u kiyi hakuri akan abunda yafaru kwanaki se yanzu nagane bakida laifi Ashe kanwarki ahmad keso bakeba yanzu gashi kina fuskantar matsala ta dalilin hakan

Murmushi Asma'u tayi tace bakomai nagode da kika fahimceni amma dan allah karki gayama kowa yanzu ma haka wurin ahmad zani narokeshi yadawo saboda nayarda sarah tana tsananin sonsa

Murmushi aysha tayi tace OK kunyi magana da ahmad yana ina

Batare da tunanin komai ba asma'u tagayamata inda zata sannan tawuce tana sauri

Da kallo aysha tabita tana murmushin mugunta sannan tanufi wurin AK da sarah dawata takarda ahannunta

Tana shiga Tamika ma AK takardar tana fadin gawannan nasamu adakinka kuma yanzu nahadu da asma'u zataje wurin ahmad

Karban takardar AK yayi yana karatawa afili kamar haka
Chapter 33 · 0% Book details