← Book details Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 84

Sashe 34

Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

I am sorry friend naso na hakura na auri sarah amma bazan iya jure ganin asma'u amatsayin matarka ba gaskiya idan dai kanaso na auri sarah to se kasaki asma'u tukunnan ...
Ur friend ahmad

Runtse ido yayi cike da takaici yace wai yaushe ahmad yazama hakane dama wannan ce wasikar dayake maganar ko nagani

Dafashi aysha tayi tana fadin AK to kasaki asma'un mana tunda yace hakan ne kawai zaisa ya auri sarah

Harara ya watsamata bashiri tayi shiru tana ja dabaya

Tambayarta yayi ina asma'u zataje
Tana fadamai ya dauki makullin motarsa yafita

Khadeeja na isa ahmad yatareta da damuwa yace deeja meyasa kike wahalar danine

Daure fuska tayi tace ko ni kake wahalar daniba kasan bazaka cikamun alkawari ba meyasa ka dauka akan wane dalili kafasa auren sarah

Ahasale yace wai khadeeja meyake damun kine meyasa kike takura zuciyarki kihanata abunda takeso kawai dan kifarantama wasu

Itama ahasale tace ni bantakurawa zuciyata ba Tarzan kawaidai sonka ne nadaina yi kakasa ganewa ada nasoka amma yanzu bana sonka saboda kai kajefa yayata ahalin da take ciki yanzu

Zaiyi magana kenan asma'u ta iso

Karasawa yayi wurinta yana fadin yawwa asma'u dan allh kima khadeeja magana tagane abunda nake kuatanta mata munason junanmu meyasa zamu takura kanmu

Daga inda khadeeja take tace bana sonka ni kuma bazan aureka ba

Janshi gefe Asma'u tayi cikin sassanyar murya tace ahmad meyasa zakamun haka seda nace karkaje ko ina amma bakajiba yanzu miye anfanin abunda kayi

Shafa kansa yayi yana runtse ido yace aunty kigane nibazan auri sarah ba naji da kunnena tana fadin daga na aureta AK zai sakeki to mezai sa na aureta

"Ahmad kamanta dawannan zanji dashi amma sarah tana mutuwar sonka ahmad kar kaso kaga halin da tashiga lokacinda ka tafi she lost her mind bcoz of u
Meyasa bazaka tausayamata ba

Zaiyi magana kenan sukaji karan rufe mota dakarfi

Juyowa sukayi atare dan ganin waye AK suka gani yana nufosu kamar mayinwacin zaki

Yana zuwa ya cakumi wuyan ahmad yahada shi da mota yana fadin how dare u ahmad kawai dan kaga ina kyaleka bakajin kunya kana kebewa da matar aure
Me kanwata tamaka kake wulakantata dame wannan tafita

Riko hannunshi asma'u tayi tana kuka tace ABI please stop it

Katsaya muyi magana atsanake kar....

Bata karasa ba yasaki ahmad ya riko kafadunta da karfi cikin kakkawsar murya yace maganar me zamuyi dawa zanyi maganar da matar da kecin amanar aurenta ko abokin da kecin amanar amininsa

Kawai dan kinga ina ragamaki
To na kyaleki ne saboda ina tunanin zargin da muke maki ba gaskiya bane amma yanzu nagane kuskurena

Sakinta yayi yana fadin shikenan bari nahutar daku base kuntsaya labe labe zan sawwake maki kawai kowa yahuta
Sarah kuma ba ahmad kadai bane namiji bare tamutu ba aure

ai khadeeja najin haka tayo kukan kura tacafki kafan AK tana kuka tace Yaya dan Allah kar karabu da yayata wallahi ba ita ahmad kesoba ni yakeso kawai Baku fahimci abunda bane amma dani ahmad ke soayayya ba ammah ba dan Allah kar kasaketa takarashe maganar tana fashewa da kuka

Cak ya tsaya yana kallon ahmad da mamaki yanuna khadeeja yana fadin yanzu ahmad wannan yar karamar yarinyar kakeso mekagani ajikin wannan dayabirgeka

Matsowa ahmad yayi yadago khadeeja daga kafan AK fuska ahade yake kallon AK yace

Eh ita nakeso AK kuma ita zan aura shi so nagaskiya ba yabukatar girma ko shekaru kafin afara shi amma bazaka fahimci hakan ba se ranar da kafada irin halin da nake ciki

Kana bani mamaki yanda kacanza lokaci guda ada kana son duk abunda nakeso amma ayanzu kai kake kokarin hanani abunda nakeso

Nagaji da boye boye AK zan fito nagayama kowa wacce nakeso idan aka takura ni kuma wallahi se indauketa mugudu

haba katsaya karamar kanwarka tana juyaka kamar remote control abunda takeso shikake yi kayi kokarin koyamata yanda zata nemi Abu dakanta saboda ba kullun kuke tare ba

Yana kainan yaja hannun khadeeja yatafi yana fadin ga asma'u nan kayi abunda kaga dama da ita amma kasan ka tanadi amsar da zakaba iyayenta dakuma grany

Kuka khadeeja tafara tana kokarin kwace kanta tana kiran asma'u amma yaki sakinta seda suka shiga mota yatada aguje yabar wurin shikanshi titi kawai yakebi aguje kamar zai tashi sama amma baisan inda zashiba
Da kallo AK kebin motar har tabacemai sannan yashiga motarsa yabar wurin

Durkushewa asma'u tayi awurin tana wani irin kuka mai ban tausayi tasan shikenan yanzu kowa zaisan abunda yake faruwa AK zai rabu da ita ga ummanta nafama da ciwon zuciya tun rasuwar abbansu yanzu idan taji tasan tabbas bazata ita jurewa ba ga abba da inna wane hali zasu shiga

Seda tayi kukanta mai isarta sannan tawuce gida

AK na isa gida bangaren grany yanufa yasanar da ita zancan ahmad kanwar asma'u yakeso kuma yafasa auren sarah

Lallashinshi tayi tana kuantar mai dahankali

Yaso yagayamata komai amma ganin bata cikin koshin lafiya yasa ya barshi akan idan taji sauki zai gayamata komai sannan yabata hakuri akan zai sawwakema asma'u tunda ba son junansu suke ba

Tana isa gida tazauna apalo hade da dafe kai tana tunanin ina ahmad zai kai khadeeja dan ba hanyar gida taga yanufa ba

jin anfizgota dakarfi yasa tadago atsorace dan ganin waye

Sarah tagani atsaye tana huci ga idanunta dasuka kunbura sunyi ja

hannunta tafara ja tana fadin dan ubanki ko mayyace ke yau sekinbar gidan nan

Fizge hannunta tayi tana fadin ke baki isa kifitar dani ba sekibari Wanda yakawoni yafitar dani dakanshi

Dariya aysha tayi tana tafa hannu tace kaji wani karfin hali to albishirinki AK da kansa yabamu izinin fitar dake daga gidan nan kije kijira takardarki zata biyoki daga baya

Hannunta tazo kamawa tayi saurin kawcewa tana fadin base kunfitar dani ba nizan fita dakaina
Sannan takalli sarah tace ke kuma kinba mata kunya wallahi kina ba kanki wahala kina hauka akan namijin da baimasan kinayi ba yayanki yana kokarin hadaki da Wanda kike so amma ke kinzama silar rabashi da amininsa kindaga mai hankali kin hanashi sukuni shame on u

Tana kainan ta juya tafita daga gidan tana sharan kwalla
[18/07, 15:05] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚
👨‍👧 _DOMUN KANWATA_ 👩‍👧

Na( *Maryam Mhd*)

1⃣0⃣0⃣

Tafe take akan hanya tana kuka tunaninta daya ummanta mezata ce mata wane hali zata shiga idan taganta awannan daren wai ankorota daga gidan mijinta

Amma yata iya yazama dole ummanta taji amma tasan dubarun dazata mata yanda abun bazai daga mata hankali sosai ba

Gudu ahmad yake amotar kamar zai bar gari se kuka khadeeja ke masa amma bai saurareta ba sunyi nisa sosai

Mai yakare amotar gashi ba kowa akan hanyar

Bude motar yayi yafita yana rufo kofar dakarfi

Fitowa khadeeja tayi cike da masifa tashiga gabansa tana fadin meyasa katsaya ai na dauka garin zamu bari what is wrong with u Tarzan

ahasale yace karki kara cemun Tarzan Duk bake kika sakani ahalin da nake ciki ba miye laifina

dan nasoki ko kuma dan nakasa saka son sarah araina

Wallahi da ina da hali da nacire sonki na saka nata koba komai nasan tana sona

Kuma da itace bazata taba hakura dani dan wasu ba koda kwa AK ne dakanshi

juyawa tayi tana fadin to kaje ka aureta mana tunda kasan tana sonka meyasa zaka daukoni ka kawoni nan

Binta yayi da kallo yakasa cewa komai seda yaga tayi nisa sannan yabi bayanta yana kiranta

Banza tayi dashi tana tafiya seda taga tafara shiga daji tsoro yakamata ta tsaya

Karasowa yayi cikin sigar lallashi yace deeja wai meyasa kin cika rigima ne kinga nan wurin baida kyew kizo mukoma can ko zamu samu wani ya tsammana mai mukoma gida nasan yanzu anfara nemanki

Kamar tafashe da kuka tace bani wayarka inkira Umma

"Wayana tafadi dazu awurin da AK ya iskomu
Ina taki wayar

"Ba caji

Juyawa yayi yanufi mota yana fadin
OK muje in munsamu mai se kiyi caji amota

Bin bayansa tayi suka dawo

Bude motar yayi suka zauna shi agaba ita abaya amma kofofin motar abude

Kuka tafara tana fadin yanzu gashi kajamun nasan ana nemana agida ni damuwata ma bansan wane hali yayata take ciki ba

Handkerchief yamika mata yace dan allah kidaina wannan kukan kinga wurin nan ba kyew ne dashiba kar ki tona mana asiri

Cikin kukan tace matsoraci kawai...

Dariya yayi yace ahaka kika gani kina so ba

Kauda kai tayi tace ni allah bana sonka

Shiru yayi baice komai ba yana sauke ajiyar zuciya

Grany ce tace AK ya kira mata asma'u zasuyi magana

Bayan ya fito ya dudduba ko ina baiganta ba yazo wurin su sarah dake zaune Palo yana tambayar asma'u bata dawo bane

Da mamaki aysha tace lafiya kake nemanta

zama yayi yana fadin Kawai dai grany ke nemanta

Kauda kai Sarah tayi tace mun koreta

What ???

Yafada yana kallon bangaran grany

Aysha tace bakaso mukayi hakan bane ko kafara damuwa da ita ne

harara ya watsamata yana fadin
come on shut up dallah !!

meyasa zaku koreta awannan lokacin ba kwa tunanin grany ne kunsan bata jin dadi dawanne kuke so taji

To kumasani ba ita ahmad kesoba kanwarta khadeeja itace budurwansa

Azabure sarah tamike tana fadin Yaya kasan me kake fada kuwa khadeeja fa kace

"Kwarai khadeeja da ita suke soyayya ahmad dakansa yafadamun kuma nagansu tare da khadeeja akan idona yadauketa suka tafi kawai kin gansu tare ne ke kuma kikayi tunanin itace yakeso nan yakwashe yanda sukayi yagayamusu
Yakare maganar dafadin
Yanzu gashi kun koreta me kukeso nagayama grany

riko hannunsa aysha tayi tana fadin AK kayi hakuri amma aikin gama ya gama kawai kasan yanda zakayi da grany

Kuace hannunsa yayi yanufi bangarensa

Damamaki sarah ke kallon aysha ahasale tace amma dazu wace takarda kika bama AK ina kika sameta
Yama naga zancan bai baki mamaki ba hakan yana nufin kinsan da maganar kome

Sosa kai aysha tayi tana kame kame tace yi hakuri sarah nima se dazu nasani naji tsoron idan AK yasan gaskiya bazai rabu da asma'u bane shiyasa naboyemaku zancan amma kiyi hakuri

Tsaki sarah tayi tace karki kara mun irin haka banaso da kingayamun tun alokacin da nasan matakin da nadauka
Chapter 34 · 0% Book details