← Book details Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 84

Sashe 29

Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dariya AK yayi yace to jeka zanje wurin Momy kafin kagama

Dakallo ahmad yabisa har yafita sannan ya rintse ido hade da dafe kai yana tunanin anya yayi ma Kansa adalci Kuwa bayajin zai iya rayuwa batare da khadeeja ba

Cike da farin ciki AK yashigo gida yana kwalama sarah kira

Kap mutanan gidan nafalo azaune da mamaki suke kallonsa suna tambayar Meyafaru

Wurin sarah yanufa yana fadin sarah I have a surprise for u
Murmushi tayi tace miye
Nuna mata ahmad Dake tsaye bayansa yayi yana fadin nacika maki alkawarinki ga ahmad yadawo gareki yayarda zai aureki kuma nanda kuana biyu ka.....

Batajira yakarasa ba tanufi wurin ahmad tana tambayar da gaske yayarda zai aureta

Hakuri yaba grany dasauran mutanen gidan akan abunda yafaru kwanaki

Nan kowa yafara saka albarkacin bakinsa akan yarinyar data yaudari ahmad

grany tace wai Wace yarinya ce wannan

Duddubawa AK yayi baiga asma'u awurin ba sama yanufa yana kiran chitti

daidai falo sukaci karo Zai shiga ita kuma Zata fito

dafe kai yayi yana kallonta yace nagayamiki kina bukatar glasses amma baki yardaba something is wrong with u eyes

Sosa goshinta tayi tace alamu sun nuna kaine ke bukatar glasses saboda .....

Katseta yayi dafadin chitti muje kasa akwai abunda zan nuna maki

Kallon bayanta tayi dagefenta sannan takalleshi damamaki tace are u okay

Daure fuska yayi yace what??

tafa hannu tayi tana dariya tace naga alama matsalan ba a idonka takeba a kwakwalwa ne
Tunda kafara gane gane

Hannunta Yakama yajata zuwa kasa yana fadin

kece dai yau zakiyi mugun gani ur ex-boyfriend is getting married to my sister
Kusan ahmad yakaita yana murmushi yace gashi kafadamata taji da kunnenta zaka auri sarah

Grany tace meyasa zaice haka

Dariya yayi yace haba grany asma'u fa matata ce kuma Yaya awurin sarah so yakamata ahmad yasanar da ita zancan aurensu

Murmushi grany tayi tace taji dadi dayafara girmama asma'u amatsayin matarsa

Cikin sassanyar murya ahmad yace ma AK idan bazai damu ba yanaso yayi magana da asma'u in private

Take ur time...
Ak yafada yanama sarah alamar kar tace komai

Gefe suka koma tafara tambayarshi meyasa zai auri sarah bayan baya sonta ya khadeeja zatayi idan taji zancan zai yi aure

Hakuri yabata akan rashin cika mata alkawarin dayadauka zai auri khadeeja kuma yakula da ita

Amma zai auri sarah ne saboda khadeeja ....
Nan yabata labarin yanda sukayi da khadeeja

Kai ta girgiza cike da tausayin kanwarta tace ahmad nayi kuskure a aurena banaso kayi nadama irin yanda nayi kai namiji ne taya zaka zauna da macen da bakaso ina anfanin auren idan har bazakuyi farin cikiba

To asma'u yazanyi khadeeja tadaina kulani tace sena auri sarah ko zan shekara ina kwatantama AK matsalar dake cikin aurennan bayarda zaiyi ba

I am doing it for my deeja and nothing can stop me

Yana kainan yajuya Yakoma wurin AK

Kusa da asma'u AK ya matso cikin rada yace
chitti this time ur magic doesn't work on ahmad
I feel sorry for u

Wane kalan magic kuma anya kwa yau baka sha wani Abu ba

bansha ba amma zansha anjima coz I will celebrate abokina yadawo kuma kanwata zata auri Wanda takeso
Nakusa rabuwa da kaya

Barin wurin tayi batace komai ba tanufi sama tana share hawayenta tasan ahmad yana auren sarah AK zai saketa yazatayi da ummanta

Ba adau lokaciba se gata ta sakko da gudu gudu tasha handbag dinta tun tada datana gida

Har takusa kofa grany tace a'a asma'u ina kuma zakije haka kamar ankoroki

Fita tayi tana fadin grany gida zanje ana nemana yanzu zan dawo

Kusan AK da aysha sarah tamatso tana fadin ina kuke ganin asma'u zataje

Dariya yayi yace kan cinyar ummanta zataje tarera kukan bakin ciki

dariya suka sa aysha tace zataje takona photunan ahmad dake wurinta ne

Asma'u tana fita ta tari addedeta se gida

Khadeeja ta isko tana wanke wanke Umma kuma na daki

Khadeeja na ganinta tazo dagudu ta rungumeta tana murnan ganinta

Shafa gefen fuskanta asma'u tayi cikin rawar murya tace deeja kinsan ahmad zai auri sarah

Kauda kai khadeeja tayi tana maida hawayen idonta tace eh nasani

To meyasa zakisashi ya auri sarah bayan kina sonsa

Ni bana sonsa ammah kawai kimanta dazancan karma Umma taji

Jin muryan Umma sukayi abayansu tana fadin meye ba'aso naji

Bayanta khadeeja takoma tatsaya tana kallon asma'u tace
Umma wai kewarki take shine tazo tadubaki amma bataso kisan tazo

Kusan asma'u Umma tamatso takama hannunta tana fadin asma'u lafiya naganki haka meyake damunki
Anya kwa kina samun kuanciyar hankali agidan mijinki kuwa

Murmushi asma'u tayi takai Umma Palo tazauna sannan tazauna kusa da ita tace

Haba Umma meyasa kike damun kanki ne akan abunda ba gaskiya ba ina zaune lafiya agidan mijina yan uwansa suna sona suna kula dani to me kikeso
Gaskiya zanje nasamu abba yazama dole ki koma wurin inna kuzauna tare ko kya rage kewa in yaso nan se asa yan haya

Murmushi Umma tayi tace
To shikenan ni dama damuwata bansan wane kalan zama kike agidanki bane

Kuantar da hankalinki Umma komai lafiya kalau

To shikenan dazu munyi waya da haleema tace tunda basu samu zuwa bikinki ba zasuzo itada Ali suga gidanki

Shiru asma'u tayi da alamun damuwa afuskanta

Kama hannunta Umma tayi tace nasan abunda kika tuna asma'u kimanta da komai yanzu bagashi kinyi aurenba kinma auri Wanda yafishi komai ai nafiso suzo sugani da idonsu wannan dai asma'un dasuka hana dansu ya aura saboda suna so ya auri yar attajiri gashi ta auri mijin dakowace mace ke fatan samu

Tashi asma'u tayi tana fadin Umma bari natafi kar yamma tayi

Rakota sukayi har waje da mamaki Umma tace asma'u duk ina motocin mijinki zaki zo a napep

Dariya dole asma'u tayi tace ohhh sauri nakene Umma shiyasa banjira ankawoni ba

Tana dawowa dakinsu tanufa tayi alwala tayi sallar la'asar tana ninke hijabinta AK yashigo

Kan gado yazauna yana fadin chitti kin fara parking ne
Da kin kyewtama kanji dan jibi warahaka tuni nayi waje dake daga gidan nan

Ijiye hijab din tayi tanufi dressing mirror tana fadin ni ba chitti sunana ba kuma basai ka koreni daga gidanka ba ni zantafi dakaina

Kusa da ita yamatso yana fadin ina kika je dazu

Jadabaya tafarayi tanakallonsa tace badai sokake na nemi izini awurinka kafin nafita ba

Girgiza kai yayi yamatseta da bango suna kallon cikin idon junansu yace inaso namiki kashedi ne idan har kika yi wani abunda dazaisa ahmad yafasa auren sarah se na kwakulo wannan idon dakike yaudaran maza dashi

Turesa tayi tawuce batace komai ba amma jikinta yayi sanyi

Komawa yayi yazauna yana fadin cigaba da parking nidai zansa ido kar amun sama dafadi da wasu abubuwana

Hijabin tasa a drowan kayanta tana fadin base nayi parking ba saboda ba abunda zan fita dashi daga nan gidan

Dole kitafi da tsummanki wazaki barmawa

Idan ka auro aysha setasa

Ba abunda aysha zatayi da kayanki tafi karfin kwance

To ai ni duk kayan dakaga inasakawa daga gidanmu nazo dasu nawane bana bukatar Wanda yafito daga hannunka

Karya kike kice ba kyason abun hannuna bayan saboda shi kika aureni

Kusa dashi tazo tatsaya tana kallonsa tace wai meyasa kakeso ahmad ya auri sarah bayan kasan bayasonta kana tunanin tunda ta auri Wanda takeso zatayi farin ciki kenan

Dagowa yayi yana kallonta da mamaki yace wai shawara kike bani ko fada kike mun

Kauda kai tayi batace komai ba

Wa yagayamaki ahmad baya son sarah ?
Suna son junansu ke kika shiga tsakaninsu Yanzu kinga asirinki yatonu shine zaki fara kame kame aurene dai ba fashi kuma daga andaura aurensu ni kuma zan warware nawa dake

Fita tayi daga dakin tana fadin nakasa gane wane kala ne kai u keep making the wrong decision
[18/07, 15:04] Hubbey Frd Ameena Kn: Tana sakkowa kasa ta isko mutanen gidan zaune apalo kusan grany taje tazauna suna fira

Cike da takaici aunty sadiya ke kallonta kusan inna ladidi tamatsa cikin rada tace
ladidi natsani yarinyar nan duka duka yaushe tashigo gidan nan amma ji yanda grany tawani jata ajiki ni tsoro na ma kar abata jan ragamar gidan

Dariya ladidi tayi tace haba wa ai wallahi bata isaba barima kigani

Tana fadan haka tamike tanufi wurin asma'u tana murmushi tace gaskiya yau yakamata musan dandanon girkin surikarmu tunda tazo bamuci abincinta ba koya kuka gani

Aysha tayi carab tace wallahi kwa gaskiya yau yakamata tamana girki

Daure fuska grany tayi tace dacan wayake maku girki yanda kuke dinnan tukunya nawa zata daura muku

Sadiya tace grany tukunya daya ta isa base tayi daban daban ba mudai yayi dadi kawai

Shuru grany tayi batace komai ba
Tashi asma'u tayi tace ba komai grany zan musu girkin ai dama aiki nane amatsayin surikarsu
To shikenan asma'u jeki amma aysha kitashi kitayata

Carab sadiya tace a'a grany aysha aikenta zanyi wani wuri

Haka tashiga kitchen tafara aiki sauran ma'aikatan natayata se bayan mangariba tagama suka taimaka mata ta jera a dining sannan taje tayi wanka tayi sallah

Koda ta sakko suna zaune gaba daya akan dining sunsa kuloli agaba suna hadiyar yawu grany tahana kowa ci wai se wacce tagirka tazo

Tana zuwa tazauna kowa yafara ci ana santi AK dashigowarsa kenan shima yaje yazauna kusa da grany yafara ci

Lomar farko yace um um um grany amma yau ke kikayi girkinnan ko

Bashir yace Yaya narigaka azuci ka rigani afili nifa tunda nabude kular nan nasan abincin nan ba kalar nakullun bane Shiyasa naga uncle jamilu an karkace hula

Harara uncle jamilu ya watsamai bashiri yayi shuru yana kunshe dariyarsa

Cike da farin ciki grany tace yo ai asma'u ce tayi girkin

Shuru AK yayi baice komai ba se bashir ne keta koda abincin

Daure fuska grany tayi tana kallon AK tace nace matarka ce tayi girkin kuma kayi shiru

Dagowa yayi yana kallonta yace to mezan ce

Harara tawatsamai tana kara daure fuska

Kallon asma'u yayi yace ohhh Ashe haka kika iya girki darling shine ba kya mana gaskiya daga yau girkin ki zamu rika ci agidan nan

Zaro ido tayi tana kallonsa takasa cewa komai

Ladidi tace gaskiyarka AK daga yau mun samu kuku

Dariya sukayi gaba daya sarah tace tunda takasa wurin daukan wanka da kwalliya se tamana girki mai dadi muci
Chapter 29 · 0% Book details