← Book details Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 40 OF 84

Sashe 40

Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Gefen fuskanta yashafo yana murmushi yace aysha kifahimci halin da grany take ciki kinsan tana son asma'u dayawa to kafin in rabu da ita ina bukatar hujja ko dalilin dazan kare kaina dashi awurin grany idan bahaka ba gaskiya bazan iya sakinta haka kawai ba
to mezan gayama iyayenta idan ita tasan dalilin dayasa na aureta su basu saniba

Murmushi tayi tace OK I understand amma dan allah kadaina shishshige mata dazu fa ina ganin lokacinda kuke dariya a asibiti
Nidai gaskiya kadaina sake mata fuska kaga tafara raina mutane tun ba'aje ko inaba

kauda kai yayi yana fadin nasan menakeyi base kin gayamun yadda zan zauna da ita ba

Yana kainan yamike yanufi masallaci

Dakallo tabisa har yafita sannan ta tashi ahasale tawuce dakinta

dakarfi ta tura kofar dakin tashiga tana fadin ina bazai yuwu ba wallahi wannan ai shirmene

dolema nasan abinyi ina ganin abun kamar wasa gashi yafara zama babbar barazana wa farin cikina """"
[19/07, 17:03] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚
👨‍👧 _DOMUN KANWATA_ 👩‍👧

Na( *Maryam Mhd*)

1⃣2⃣0⃣

Da yamma aysha taraka sarah gidansu asma'u taje Neman khadeeja

Bayan sungaisa dasu Umma khadeeja tarakosu har waje

Juyowa sarah tayi tana kallonta da murmushi afuskanta tace to deeja nizan tafi se kinzo gobe

kauda kai tayi tana daure fuska tace allah ya kaimu

ahasale aysha taja hannun sarah tana fadin wai sarah meyake damunki ne kintsaya karamar yarinya tana daddaure maki fuska kar allah sa tazo

Kwace hannunta tayi tana daka mata tsawa tace aysha ya isa haka karkimanta matsayinta awurina so behave ur self

Dariya khadeeja tayi tadawo gaban aysha tatsaya tana fadin

malama dafarko dai inaso kisan bani nagayyace Ku gidanmu ba so dole zaku Bini aduk yadda nakarbeku ku idan kinga bazaki iya ba hanya abude take

Sannan tajuyo wurin sarah tace ke kuma sarah ina so kisan cewa koda gaba daya mutanen duniya zasu yarda da canzawarki to ni khadeeja bazan fada tarkonki ba

Saboda nasan people like u won't change easily

nasan kina da wata buyayyar manufa akan wannan fuskar mutuncin dakika ara

nunata tayi dayatsa tace

let me worn u sarah if u dare do something terrible to me or my sister I will make ur life a living hell that's my promise

tana kainan tajuya tabarsu atsaye suna binta da kallo har tashige ciki sannan sarah tajuya jiki asanyaye tashiga mota aysha tabita tana jan dogon tsaki

AK na zaune apalo asma'u tashigo tana kwasan gyalenta tawuce takusan shi zata shiga daki hannunta yakamo yajuyo da ita gabansa yana fadin zo nan hajajju ina so in tambayeki wani abu

zaunawa tayi daga kasa suna fuskantar juna takure shi da ido batace komai ba kallon kallon suka farayi nadan lokaci kana yaja nunfashi yana Sosa kai yace mema zan tambayeki ?

tashi tayi tana fadin bari natafi inada abun yi idan katuna seka kirani

Janyota yayi yazaunar da ita yana fadin a'a dawo natuna nace wai me kika gayama sarah ne har tayi saurin gane abunda najima ina kuatanta mata

murmushi tayi tace ni nama manta abunda nagayamata kawai dai magana namata kuma banmasan zata dauki abunda nafada ba

kankance ido yayi yana kallonta yace um um chitti a iya sanina sarah ta tsaneki bata sonki amma ya akayi lokaci guda tafadi magana mai dadi akanki anya kwa ba magic dinnan naki kika mata ba kuwa ni kikoyamun yanda ake nama grany tafarayin duk abunda nakeso

Dariya tayi tace wane magic kuma nidai bawannan ba gaskiya ABI bai kamata ayi bikin khadeeja anan gidan ba duk da sarah tahakura amma bazataji dadi ba

zaiyi magana kenan sukaji sarah nafadin
Ba abunda zanji sister anan zamuyi bikin kanwarmu kamar yadda Yaya yafada
Juyawa sukayi suna kallonta da murmushi afuskansu

Karasowa tayi kusa da AK tazauna tana kallon asma'u tace bama wannan ba sis kushirya gobe da daddare nahada dan kwarya kwayan party wa ahmad da khadeeja saboda inaso musanar da abokanansa da kawayanta zancan bikinsu kuma natayasu murnan cimma burinsu

kallonta AK yayi cike da tausayi yace kintabbata ba wata matsala sarah can u bear it ?

Dafashi tayi tana dariya tace Yaya come on I am not a kid ko kuma Baku yarda nahakura bane

murmushi sukayi suna kallonta basuce komai ba

da daddare har Sarah ta kuanta aysha ta iskota rai bace tace sarah ni nakasa ganeki wai ina sarahn da nasani wacce bata hakura da abunda takeso bare abunda nasan kinfi sonshi fiye da komai aduniya yaushe kika dawo hakane ko kema sallon yaudarar asma'u yayi tasiri akanki ne

Daure fuska tayi tana kallonta tace aysha waini wacece dabazan gyara rayuwata ba ko kafiri yakan musulunta yazama nagari bare ni me kika daukeni ne to nagaji da abunda kike mun kar ki kara mun wannan banzar tambayar kinji nafadamiki

ahasale tafita tana banko kofar dakarfi

washegari dasafe AK d nabangaren grany yana breakfast kan dining asma'u nagefensa azaune tana kokarin zuba kunu akofi amma takasa saboda hannunta da yayanke wurin girki

inna ameena nazaune daga gefe tana kallonsu

karasowa tayi wurinsa tana murmushi tace AK kaga asma'u tayanke dazu ahannunta kazubamata kunun mana kabata

kwarewa yayi yayi saurin daukan ruwa yakora yana kallonta da mamaki yace inna me ...mekikace ....nabata kunu fa

daure fuska tayi tace yo miye ba matarka bace kai gaka ahaka kamar zakayi soyayya amma ashe ko wayewar ma bakayi ba

Harara yajefa ma asma'u yana fadin to dabana nan waye zaibata kunun ko dolene ma setasha kunu

tafa hannu inna ameena tayi tana salati tace oh ni ameenatu menakeji haka kamar gwaranci abakin AK

amma wallahi kabani kunya se anyi magana kuce mana yan zamanin da to mudai bahaka mazan mu ke mana ba

Kallon asma'u tayi tana fadin baiwar allah shiyasa da daddare sena koreki kike tafiya allah kadai yasan me yake miki

labace baki asma'u tayi kamar zatayi kuka tace inna infadamiki wani Abu
Zaunawa inna ameena tayi kan kujera tana fadin inajinki asma'u menene

"Jiya ma haka ya.....

bata karasa ba yayi saurin fadin

OK fine....zan bata abar zancan

gyada kai inna ameena tayi tana fadin dadai yafi maka inba haka ba yanzu nakira grany asma'u tafadi komai agabanta

Kofin kunun ya fizge ahnnun asma'u yana ji kamar yarusa mata shi abaki seda yafaki idonsu ya ciko cokali da barkono ya zuba cikin kunun ya juya yana murmushin mugunta yakai kofin bakin asma'u yana fadin enjoy ur self baby !!!

Kurban farko taji kunnanta ya amsa saboda yaji

saurin janye bakinta tayi tana kallonsa

Murmushi yayi yakara kai kofin bakinta yana fadin drink it badai kunu kike soba

kallon inna ameena yayi yace kinga ai halin matan kenan tace kunu yanzu kuma nafara bata tana nuna bataso

hannunsa asma'u takama takai kofin bakinta tana shan kunun kamar ba komai aciki

Da mamaki yake kallonta seda tayi rabi sannan takai kofin bakinsa tana lashe baki tace to kaima kasha darling!!

zaro ido yayi yana kokarin kauce bakinsa inna ameena tace kai kasha mana yau naga sakaran yaro

asma'u zatayi magana kenan yayi saurin kama hannunta ya kai kunun bakinsa ya kurba

saurin hadiyewa yayi ya kauda kai gefe yana huddo harshe

Kallonsa inna ameena tayi da mamaki tace wai yanaga kana Abu kamar dayaji akunun ne

dariya asma'u tayi tace inna yaji ya....

bata karasa ba yayi saurin katseta dafadin kaji inna kuma mezai kawo yaji cikin kunu waima banaji grany nakiranki ba kitashi kije mana zamu kula da kanmu ai

Gyara zamanta tayi tana fadin ba inda zani se kungama kaidai sha kunun

Juyowa dakansa asma'u tayi takara kai kofin bakinsa tana murmushin mugunta

Ganin yakasa jure yajin kuma bayaso inna ameena tagani yasa yayi saurin tashi yabar wurin yana shakan iska yana fiddo harshe
[19/07, 17:03] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚
👨‍👧 _DOMUN KANWATA_ 👩‍👧

Cigaban 1⃣2⃣0⃣

tashi asma'u tayi tabishi tana dariya daki ta iskoshi zaune yana guma ruwan sanyi abakinsa

Dariya tayi tace ai shi dama ramin mugunta kamata yayi ka ginashi gajere gashi yanzu kai kafada ciki

Harara ya watsamata da ruwa abakinsa yace Gagagagagga

Dariya tayi har da rike ciki tace ni banajin mekake fadi amma bari nataimaka maka

Fita tayi ba adau lokaci ba tadawo da manja acikin dan karamin bowl yatsanta ta tsoma aciki tana fadin bude bakinka

Kauda kai yayi yana girgiza Kai

"Bude mana shafa maka zanyi zai rage maka zafin yajin

Ruwan bakinsa ya hadiye zaiyi magana ta tura yatsanta cikin bakinsa ta shafo man jan aciki

Saurin tashi yayi yanufi bayi yana yamutsa fuska

Fita tayi daga dakin tana dariya

Da daddare aka fara party kowa yazo cikin abokansu ahmad da kawayen khadeeja sarah senan nan take dabaki aysha ko haushi yagama cikata se masifa take tana hantarar kawayen khadeeja

apalon gidan ake komai wurin yayi haske kamar darana kowa naharkan gabansa ga daddadan sawti natashi khadeeja da ahmad sunyi matukar kyew kamar prince and princess se alokacin kowa ke ganin dacewarsu abokanansu se kodata suke suna fadin tafi ahmad kyew saura suga amaryar AK ita kuma yatake sunsan se tafi kanwarta kyew

AK nazaune adaki yana jiran asma'u

Can anjima tafito tana sanye da doguwar riga tasha katon gyalenta se kokowa take dashi

Tagumi yayi yana kallonta har zata fita tawaigo ganin bai tashi ba
tace muje mana ai nashirya

kallonta yayi sama da kasa yace muje ina ai da injera dake ahaka gara nazauna banje ko ina ba

dawowa tayi gaban dressing mirror ta tsaya tana kallon kanta da mamaki tace me kuma nayi nifa nan karshen fitowata kenan

tasowa yayi yazo kusa da ita yana fadin wai ke chitti anya kwa a abuja nan aka haifeki yanzu saboda allah kodan yafa gyalen nan na yan mata baki iya ba allah inaga ko grany tafiki iya dawri mai kyew

Labace baki tayi kamar zatayi kuka tace to ni ban iyaba ya zanyi ka kira mun khadeeja to tamun

" ni kuma kawai se aganni nakira khadeeja wai zatama matata kwalliya haba chitti abokanaina zasu mun dariya

komawa tayi bakin gado tazauna tana fadin to shikenan tunda hakane ba inda zanje kawai katafi

Shuru yayi nadan lokaci kana yajanyo drowan dressing mirror din yana fadin badai akwai kayan kwalliyar ba zo kidanyi ko yayane mugani
Chapter 40 · 0% Book details