← Book details Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 49 OF 84

Sashe 49

Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

sautin kukanta ne yakaru tace ABI ni nafiso namutu karayu akwai mutane dayawa akarkashinka ga grany da sarah wane hali zasu shiga idan wani Abu yasameka

"Kema ai kinada responsibility ga Umma ga inna da khadeeja kece mai kula dasu yazasuyi idan bake

Cikin sheshshekar kuka tace idan har kana nan bandamu ba nasan zaka kulamun dasu amma idan baka ni bazan iya komai ba ABI

runtse idanuwansa yayi dan tuni kafadunsa sun fara zafi cikin muryan wahala yace yanzu dai abar zancan meyasa kincika surutu ne kina gabar mutuwa ma bazakiyi shiru ba to nidai ki kyaleni inyi istigfari dan nafara hango barzahu

Shiru tayi hawayenta nakaruwa tana ji dama itace akasa dan tasan shikadai yasan meyakeji ahalin yanzu

Har dare yayi su AK na ahaka tuni yafara gajiya dan har wani jiri jiri kedibansa kawai taimakon allah ne da jarumta irin tashi yasa har yanzu yake durkushe awurin amma guywowinsa da kafadunsa jiyake kamar ana Sara mai gatari gashi yanada asma tuni yaji tafara kokarin tashi

asma'u ma haka tagaji da tsayuwa jikinta har rawa yake tun tana kuka har tagaji tayi shiru tana addu'a sedai jefi jefi AK yakan tsokaneta wani lokaci takulashi wani lokaci kuma sedai tafashe da kuka har takai lokacinda suduka sukayi shiru bamai magana """""
[19/07, 17:04] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚
👨‍👧 _DOMUN KANWATA_ 👩‍👧

Na( *Maryam Mhd*)

1⃣4⃣5⃣

Kokarin janye kafarta tafarayi daga kan kafadunsa tana fadin ABI
katashi katafi kabarni anan kawai koban mutu yanzuba anjima mutuwa zamuyi gaba daya dan natabbata bazamu iya kai safe ahaka ba kuma koda munkai ma kashemu zasuyi

Kaga damu mutu gaba daya gara kai katsira koba komai abun zaima su Umma sauki

Kokarin kuance hannayensa yafarayi yana fadin chitti miye haka kike kokarin yi stop moving ur legs dan allah u are hurting me kina so kikashe kanki ne idan natafi nabarki anan miye anfanin zuwana mezan gayama su Umma idan nakoma
Cikin Sa'a kuwa ya kwance hannayansa har takusa sauke kafanta yayi saurin rikosu cikin rawar murya yace

Chitti kinga na kuance hannayena kiyi kokarin kwance naki abun baida kwari sosai

Shiru tayi hawaye nacigaba dazuba afuskanta yana rike da kafafuwanta akan kafadunsa yana cigaba da lallashinta har tafara kwance hannayenta da taimakon allah tayi nasaran kwancewa sannan tafidda yagiyan wuyanta atare suka fadi awurin suna maida nunfashi

Cike da tausayi ta sunkuyo saitin fuskar AK cikin rada take jera mai sannu

Yajima ahaka kafin dakyar ta taimaka mai yatashi yana runtse idanuwa saboda azaban da kafadunsa da guywowinsa kemasa

Hannunta Yakama yana leken su JJ dake sharan bacci kaman matattu sunsha sunyi tatil

Cikin sanda suka fara tafiya seda suka dan yi nisa sannan suka fara gudu suna kara shiga cikin dajin batare da sunsan inda suka dosa ba

Sunyi nisa sosai asma'u taci birki tana fadin ABI gaskiya nagaji bazan iya cigaba da gudunnan ba mudan zauna mu huta mana

bai musa mata ba dan shi kanshi juriya kawai yake amma bayajin zai iya tafiya mai nisa bai fadi ba

Zaunawa sukayi suka jinginu da katuwar bishiyar dake wurin suna maida nunfashi sun jima ahaka kafin suka fara bin wurin dakallo se alokacin suka fahimci ba karamin daji suka shigo ba dan gaba daya wurin manya manyan bishiyoyi ne azagaye dasu kasan kuma ciyayi ne da ramummuka iri iri

Adan tsorace asma'u tamatso kusan AK cikin rada tace ABI nan ina ne

jinginar dakansa yayi jikin bishiya yana lumshe ido cikin dasashshiyar muryansa yace da a maiduguri muke dase ince wannan shine dajin sambisa
amma yanzu bansan mezan cemaki ba

shiru tayi nadan lokaci tana kallonsa sannan ahankali tadafa kafadansa cikin sigar tausayawa tace kanajin zafi ko

Dagowa yayi yakalleta suka hada ido sannan yaballe bottom din rigarsa yafito dakafadansa yana murmushi yace ba sosaiba nagode allah bakida nauyi sosai da yau namutu

Murmushi tayi da hawaye afuskanta tadora hannunta kan kafadarsa tana shafawa ahankali

Jinginar dakansa yayi jikin bishiya idonsa alumshe yana jin dadin shafawar dakate kaman tana Sosa mai wurin ne

juyo dakansa yayi yana kallonta ahankali yace kinajin tsoro ?

Gyada kai cikin rawar murya tace eh amma basosai ba

Kaifa?

Murmushi yayi yana kallon wurin dasuke baice komai ba

maidamasa wuyan rigarsa tayi tana maida masa maballan alokaci guda suna kallon junansu suna jin wani yanayin dasuka kasa fassara shi

Mutsa bakinta tafarayi ahankali tana ji kamar tagayamasa tana sonsa amma kuma tana tsoron mezai biyo baya

Suna cikin haka sukaji wani gurnani gurrrrrr

atsoarace suka kalli juna cikin rawar murya asma'u tace ABI did u hear that ??

Kai ya gyada mata yana waige waige sekara shigema juna suke

gurnanin suka kara ji anyi atsorace asma'u tarungumeshi da karfi tana jero addu'a

Dariya yayi yana rike ciki yace chitti ba komai bane ciki nane fah

Kallonsa tayi da mamaki tace cikin ka fah ABI wannan fa kamar zaki ne ko damisa

janyeta yayi daga jikinsa yana shafa cikinsa yace cikina ne yunwa nakeji yau ba abunda naci tun jiya rabona da abinci

itadai bata yarda ba se bin wurin take da kallo tana karanto duk addu'ar datazo mata tun yana mata dariya har shima yafara tsorata dayanayin wurin yafara tasa addu'ar

Washegari dasafe dai daga cikin yaran JJ yafara tashi yaga ba su AK hankali tashe yatashi sauran yasanar dasu

afusace JJ ya hausu dafada kamar su suka kwancesu bashiri ya rarrabasu acikin dajin suje su nemosu hankali tashe suka bazu nemansu hardashi JJ kuma yayi alkawarin yana ganinsu zai kashesu kowa yahuta

tun safe ahmad yaje police station suka fara shirin fita Neman su

agidama haka sun dage da addu'a tun suna kuka har sun hakura sun barma allah gidajan biyu sunzama tamkar gidan mutuwa Sam ba walwala ba farin ciki acikinsu

lokaci guda khadeeja tarame tafita hayyacinta kowa yaganta seya tausayamata kowane lokaci suna waya da ahmad yana kara kuantar mata da hankali

bangaren sarah ma abun yafara damunta saboda bata San halinda AK yake cikiba dan tasan idan dai JJ yagansa bazai kyaleshi ba

aysha ma haka tana mamkin rashin dawowar AK tunda JJ yacemusu yakashe asma'u gashi kuma sunji shiru suna kiransa basa samunsa

Kuance suke suna bacci hankali kuance AK yadora kafansa kan cikin asma'u ita kuma tayi reran dayan hannunta kan kirjinsa

ahankali tafara bude idanuwanta tana bin wurin da kallo saurin tashi tayi tana ture kafan AK daga jikinta tafara tashinsa

gyara kuanciyarsa yayi cikin muryan bacci yace chitti bring my coffee kafinnan zantashi

Dariya tayi tana daddabashi tace wane kalan coffee kuma ABI kamanta inda muke ne

janye hannunta yayi daga kan kafadarsa idonsa arufe yace jiya nayi wani mafarki mai ban al'ajabi idan kin kawomun coffee dina se inbaki labari

Ganye ta tsinko tadora akan bakinsa tana dariya tace ba coffee sedai dambun nama inzakaci

saurin tashi yayi zaune yana kakkabe bakinsa lokaci guda yana bin wurin da kallo

Runtse idanuwansa yayi yakara budesu yanaso yatabbatar ko dagaske ba marfaki yayi ba

tashi zaune yayi dakyar yayi mika yana salati kamar daga sama sukajiyo
Tafiyar yaran JJ suna nemansu

atsorace suka kalli juna suna mikewa tsaye asma'u ta cakumo rigarsa cikin rawar murya tace
ABI... mun ..shiga uku za.....

Bata karasaba yaja hannunta aguje suka cigaba da gudu suna kara kutsawa cikin dajin seda sukayi nisa sannan suka fara tafiya suna Jan kafa kamar bugaggu ga kishi da yunwa dasuka addabesu karfin hali kawai AK yake amma tuni yafarajin asman shi na kokarin tashi

Tafe suke shi agaba ita abaya sekara kutsawa cikin dajin suke

Karasowa asma'u tayi kusa dashi cikin dasashshiyar muryanta tace ABI I am hungry

baijiyo yakalleta ba yace gani kici

Dariya tayi tace ai koda inacin naman mutane ba'abunda zanyi danaka dan dagani ba dadi zai yiba

Shiga gabanshi tayi tana rike cikinta kamar zatayi kuka tace

ABI dagaske yunwa nakeji kuana biyu fa ba abunda naci ko ruwa bansha ba

Kafadunta Yakama ya juyar da ita sukaci gaba datafiya yana fadin chitti ki kalli nan wurin da kyew kigani banda ciyayi da bishiyoyi ba abunda keda kwai

Idan bamuyi gaggawan barin wurinnan ba mune zamu zama kalacin namun daji

Saurin juyowa tayi tana fadin 😧namun daji fa kace kana nufin akwaisu anan

Dariya yayi yawuce gaba yana fadin awannan dajin miye baza'a rasa ba kima kula da inda kike sa kafanki kar ki taka maciji

saurin bin bayansa tayi tana riko hannunsa tace to wai aganinka suwaye wa'yannan kuma meyasa suka kamani

"Ke baki sani ba taya za'ayi ni insani

Shiru tayi batace komai sukaci gaba datafiya batare da sunsan inda suka nufa ba amma kowane da tunanin dayake aransa

Tuni ahmad da yan sandan suka shigo dajin sedai abun takaicin basusan ta ina zasu bi sufara nemansu ba hakanan dai suka rarrabu gida uku sukashiga dajin dafatan ganin su ko ko sukama yan daban

agida kuma tun safe grany da inna ameena suka je gidansu asma'u aka taru acan ana taya juna jaje da addu'ar allah yabayyana su

har yanzu JJ nacigaba da nemansu AK acikin dajin nan saboda yanada tabbacin bai isa sunfita daga dajin ba dan yanada girma sosai za'ajima kafin akai kyawyukan dake kusa dawurin

suna cikin tafiya asma'u tarangada ihu atsorace AK yajiyo yana duddubata yaga ko wani Abu yasameta

Tsalle tafara cike dafarin ciki tana nuna mai bishiyar mangoron datahango

tace ABI kalla kaga mangoro acan wallahi mangoro ne
tsaki yayi yana kallon bishiyar mangoron shi kanshi tabirgeshi bai San lokacinda yasaki wani lallausan murmushi ba suka nufi wurin

dutse yadauka yafara jifan mangoron amma yakasa samun koda guda dayane

labace baki tayi kamar zatayi kuka tana kallonsa tace ABI haka bazai yiba kahau mana katsinko

Baki yasaki yana kallonta yace nahaufa kika ce wannan katuwar bishiyar nasan miye akai haka kawai ke ki hau mana

tureshi tayi daga wurin tana fadin yo se in hau mana ai ba yau nafara ba bishiyar ma dako tsawo batada

Matsawa yayi yabata wuri tafara kokarin nawa se dariya yake yana tafa hannu yana fadin chitti!!!chitti!!!chitti!!!

Tafara hawa kenan tayo kasa zata fadi yayi saurin tareta tafado kansa suka fani kasa tare

Dafe bayansa yayi yana runtse ido hade dasakin yar kara atsorace ta riko gefen fuskarsa tana fadin ABI are u ok kaji ciwo ne ?
Chapter 49 · 0% Book details