← Book details Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 32 OF 84

Sashe 32

Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tunowa tayi da plan dinsu tafara kokarin turesa tana fadin AK katafi kar wani yaganmu bata gama rufe baki ba sukaji anturo kofar
Atsorace yasaketa sukajiyo atare dan ganin Wanda yashigo

Fa'iz suka gani atsaye yana kallonsu idonsa cike da hawaye

Me kake anan....
AK yafada yana daka mai tsawa

Shuru yayi yakasa magana yana binsu da kallon tuhuma

Janshi AK yayi dakarfi yafito dashi Waje
Damamaki kowa ke kallonsu

Ahasale grany tace kai abidi sakeshi mana meyamaka

Aysha tayi saurin fadin grany lekani yake ina canza kaya
Juyowa fa'iz yayi yana kallonta da jajayen idanuwansa

Zaiyi magana kenan AK ya wankesa da mari yana fadin me ya kaika dakinta

Zai karamishi kenan asma'u tarike hannunsa tana kallon fa'iz tace dagaske kaje dakinta

Zai yi magana AK yarigashi dafadin tambayarsa ma kike kenan karya zan masa kome

Inna ameena tace yo kai AK ya akayi kasan yaje dakin kana daga ciki kodaga waje

fa'iz zaiyi magana AK yakara katseshi dafadin wallahi idan nakara ganinka kanufi dakinta sena tattaka ka

Kwaceshi asma'u tayi daga hannun AK tanuna mai hanyar fita tana fadin wuce gida

Cikin rawar murya yace ammah listen

I said out ....

Saurin barin wurin yayi khadeeja tabi bayansa

Hakuri AK yaba su inna akan abunda yafaru

Murmushi tayi tace ba komai abidi ai fa'iz kaninka ne zaka iya hukuntashi idan yayi badaidai ba

Fita asma'u tayi tabi bayan khadeeja akarkashin bishiyar kofar gida ta iskosu yasa kai aguywa yana kuka khadeeja na zugunne kusa dashi tana lallashi

Asma'u nakarasowa yamike zai bar wurin tayi saurin rikosa tana bashi hakuri

Cikin sheshshekar kuka yace yanzu amma kema kinyarda na aikata abunda tace wallahi karya takemun

Rikoshi tayi tana murmushi tace nasan ba halinka bane fa'iz amma bayanda zanyi inkareka

Kauda kai yayi yana share kwalla yace amma meyasa kika auri AK Sam bai dace dake ba ba mutumin kwarai bane kuma wacece wannan yarinyar danagansu tare

Murmushin dole tayi tace haba fa'iz meyasa zaka ce haka kaifa kake yabon AK hausawee kuma yau kana kushisa wannan yarinyar kanwarsa ce shiyasa kaga yamaka haka akanta amma ba halinsa bane yanada kirki kuma yanada hakuri bayada saurin fushi kuma ko yayi nantake yake mantawa

Da kyar tasamu ta lallasheshi suka wuce gida da khadeeja ita kuma tadawo ciki

Karo sukaci dasu inna zasu fita hakuri tabasu kuma taroki kar su gayama Ummi da abba abunda yafaru sannan sukayi sallama suka tafi

AK natsaye yana kallon sarah da aysha dake dariya karasawa yayi wurinsu fuska ahade yace inafata dai Baku kuka shirya wannan wasan kwaikwayon ba

Kame kame suka fara suna kallon kallon zai yi magana kenan ahmad yakirasa awaya yana tambayar ya yake yaji wai police sunzo Neman sa

Murmushi yayi yace I am fine friend yanzuma nakeso nazo company

Dariya ahmad yayi yace har kagama cin amarcin ne

Katse kiran yayi batare dayace komai ba
yana dubawa yaga harsun bar wurin girgiza kai yayi
Yajuya zai fita sukaci karo da asma'u tazo wucewa dafe goshi sukayi atare cike ahasale yace wai meyake damunki ne

Murmushin yake tayi tana mai alama da grany tana kallonsu

Shima kalan murmushin yayi yana taba goshinta yace meyasa ba kya kula dakanki ne kinfiso kiyita jima kanki ciwo kina bani aiki

Inna ameena dake kallonsu tayi dariya tace ai kakanninmu sunce in mata da miji sukayi karo sau uku to ba mai rabasu sai Allah saboda haka kunyi daya saura biyu

Kan asma'u Yakama yahada danasa da karfi saida taji zafi seda yayi har sau biyu sannan yawuce yana shafa goshinsa ....

Da daddare yana kuance kan gado yayi rub daciki yana kallon TV ga bowl din gyada ahannunsa yana ciki

Asma'u tashigo dakin rike da mug din coffee dinsa kusa dashi ta ijiye batace komai ba da alamun damuwa afuskanta

Binta yayi da kallo yana fadin fushi kike ne dan nadaki kaninki

Juyowa tayi tana kallonsa tace meyasa zanyi fushi dan yayi laifi ka hukuntashi
Sedai inaso nasan meyasa kamareshi
dan yashiga dakin
Kodan yaganka tare da aysha

Shuru yayi baice komai ba yaci gaba da cin gyadarsa

Bathroom tanufa tana fadin kunasaka familyna amatsala saboda makauniyar soyayyarku

Dakallo yabita har tashiga sannan yadauki coffee dinsa yanasha

Can anjima tafito sanye da doguwar rigan baccinta ga towel akanta tana tsane gashinta

Remote din kusa dashi tadauka takashe AC tanufi dressing mirror tana gyara gashinta

Da mamaki yake kallon dogon gashinta dan Sam bai San tanada gashi haka ba

Remote din yadauka yakunna AC
Juyowa tayi takallesa yayi saurin kauda kai yana kallon TV

Zuwa tayi tashiga gaban TV tahanashi kallo

Kashe AC din yayi takoma wurin dressing mirror

Kara kunna AC din yayi yana murmushi
Juyowa tayi tana yarfa hannu tace wai miye haka kakeyi

Gyana nakeci....
Yafada batare da yakalleta ba

Kusa dashi tamatso dan ita se alokacin ma ta lura da gyadan hadiye yawu tayi tana murmushi tace tsammun gyadan

Make kafada yayi yace naki kije wurin grany tabaki

Grany tayi bacci

To kijira dasafe tabaki

Dawke bowl din tayi daga gabansa tana fadin Allah senaci

Dirowa yayi daga kan gadon yana fadin to kikawo na tsammiki da kaina

Guduwa tafarayi tana cin gyadar shikuma yana kokarin kamata seda suka zagaye dakin kap sannan takara cika hannu da gyadan ta mika mai tana fadin to tsaya gashi Allah kadan naci

Kin karba yayi yana kokarin kuace na hannunta suka fada kan gado shi Asama ita akasa
Kallon juna sukafarayi alokaci guda suna tuna lokacinda suka fara haduwa da zamansu awuri guda

Asma'u ce ta tuna lokacinda AK kecemata gobe ana daura auren sarah zata bar gidan

Tureshi tayi tatashi tana gyara balanket dinta dake kasa ta kuanta tana hawaye
AK ma shiru yayi yaci gaba da kallon TV har bacci yadaukesu

Washegari dasafe ....
Khadeeja nazaune adaki tun jiya take kuka har yau tana tuna shikenan yau ahmad zaizam nawata shikenan zata rabu dashi

Umma ce tashigo dakin cike da tausayi take kallonta tace khadeeja kiyi hakuri shi aure nufi ne na Allah tunda kikaga bai aureki ba Allah yayi ke ba matarsa bace

Shuru khadeeja tayi tan sharan kwalla

Cikin sassanyar murya Umma tace zaki samu zuwa bikin kuwa

Girgiza kai tayi batace komai ba se hawayen ta dasuka karu

Abangaren ahmad ma haka Zaune yake atakure ga idonshi yayi ja da alama kuka yasha bakadan ba Momy batayi wani taron biki ba dan tasan ahmad ba son aurennan yakeba dafashi tayi da damuwa afuskanta tace ahmad kaifa namiji ne za a iyama mace auren dole tazauna amma ba namiji ba idan har kasan baka son sarah to karkayi kuskuren aurenta
Namiji shine ginshikin aure idan har bazaka iya jan ragamarsa ba to baida wani anfani

Girgiza kai yayi yace Momy banason sarah amma zan aureta saboda wani dalaili

Tashi yayi yafita yana fadin Bari nashirya natafi AK yana jirana

Asma'u na bangaren grany bayan tagama hada breakfast ta fito tana kallon grany tace
Grany har kinshirya lalle kin kosa sarah tayi aure

Dariya grany tayi tace eh mana asma'u ai rana tafarayi gashi har mutane sunfara taruwa jeki kema kishirya

Zama asma'u tayi tana fadin bari har nacika tumbina grany

Ina wani tumbi anan Abu kaman faranti

Wai ina abidi banganshiba yau

Yana bacci ....

Oh to nidai yau Allah sa yasa manyan kaya wallahi natsani kananun kayannan daurin aure guda amma kagansu da kananun kaya kamar wasu turawa

Dariya tayi tace karki damu grany tunda ba kyaso bazai saka ba

Wa ya isa ya hanasa asma'u mutumin da kika ga ko juma'a kananin kaya yake sakawa

Tashi tayi tafita tana fadin
Grany idan kasan halin mutum zaka ita sashi yayi abunda kakeso

Tana isa bangarensu ta iskoshi kwance yana bacci murmushi tayi tanufi bayi tayi wanka kayanta taduba taciro wata doguwar riga mai kyew da dogon wandonta kamar na India se gyalen kayan

Datasakasu ita kanta sunbirgeta mai kawai tashafa sedan kunne datasaka kalan kayan

Drowan AK taduba taciro mashi kananun kaya masu kyew sannan tafito

Azaune ta iskoshi bakin gado tunda tafito yake kallonta seyaga tayi kyew yau

Murmushi tayi tadawra kayan kan gado tana fadin ABI....bata karasa ba yawatsamata harara tayi shuru tana kunshe dariyarta

Can kuma tace to ai ban fada duka ba tunda ka kirani da chitti ai nima zan iya kiranka da ABIDI amma sunan yamun yawa shiyasa na rageshi

Daure fuska yayi yace to kikirani da AK ko ABID mana
Miye nawani ABIDI

Dariya tayi tace ashe ba dadi idan bakaso nakiraka ABI to nima kadaina kirana chitti

Shuru yayi yana kallon kayan da ta ijiye kan gadon murmushi tayi tadauko kayan tana nuna mai tace ga kaya nazaba maka kasa zasuma kyew

Kauda kai yayi yace karki manta matsayinki awurina so stop acting like my wife

Dariya tayi tace banmanta ba amma ai duk dahaka ni matarka ce kuma kananun kaya suna maka kyew inason ganinka acikinsu shiyasa nakeso yau kasa

Kwace kayan yayi ahannunta yanufi dressing room yana fadin tunda kinaso kwa bazan saka ba kuma kidaina tabamun kayana daga yau

Murmushi tayi tana kallonsa har yashiga sannan tafara gyara gadon

Can anjima yafito sanye da manyan kaya sunmasa kyew bakadan ba

Dariya takusa kwacemata ganin yanda yake tattare rigar ga hular akarkace

Daure fuska yayi yanufi dressing mirror yana fesa turare

Kallonsa tayi tana dariya tace yallabai hularka akarkace
Banza yayi da ita yana gyara zaman wandonsa

Dagowa yayi yana kallonta tana dariya yace ai gwara ni koba komai ansan nayi kyew ke kuma fa dako janbaki baki iya sakawa ba kin wani yafa gyale kamar dillaliya ...
Fita tayi tana dariya tace wani gwara kai dawata hularka har tarufe girarka Allah sama kana gani da kyew

Bin bayanta yayi suka fito tare yana rike da rigar da yakeji tamai dabaibayi

Tasashi agaba se dariya takemai tun yana daure fuska har yabiyemata suna dariyar

tunda aysha ta tsinkayesu taji kamar andaba mata wuka suna sakkowa aka hau yima AK dariya bashir ne yagyara masa hularsa kowa nafadin yau ya canza kamar bashiba grany tace manyan kaya sunfi yimasa kyew

Matsowa aysha tayi taja asma'u gefe ahasale tace ke wai meyake faruwa ne

Bige hannunta asma'u tayi tana murmushi tace abunda idonki yaganemaki

Firan me kuke da AK dazu dakuka sakko
Chapter 32 · 0% Book details