← Book details Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 84

Sashe 21

Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Anci ansha anmore duk da dai bahaka akaso ba amma anji dadi grany da inna baki yaki rufuwa

asma'u kuma tundaga lokacin tafara kuka khadeeja natayata har izuwa lokacinda za akaita dakin mijinta kuka take kaman ranta zaifita tsam tarike Umma da inna taki sakinsu haka da aka kaita wurin abba yamata nasiha da kyar aka banbarota ajikinsa

Motoci na alfarma suka zo daukan amarya tasamu rakiyar mutane da dama su Ummi ne akan gaba se Momy da zainab din yahya da sauran dangi da yan uwa sedai ba kawayen amrya dan asma'u batada wata kawar data wuce khadeeja yan matan wurin duk kawayen khadeeja ne

Tun amota asma'u ke kuka khadeeja na gefenta tana lallashinta har suka iso dankareren gidan AK wato (hausawee Mansion)

Inda suka samu tarba ta musamman daga wurin dangin ango bangren grany akafara kaita bayan anmata nasiha da sauran abubuwan al'adarsu sannan aka nufi bangaren AK da ita baki bude kowa keyawo agidan tundaga get wasu sukafara santin gidan bare daga ciki aljannar duniya sekafita waje zaka San dare yayi yan mata sun zage se selfi ake ana turo baki

Da kyar so Momy suka tattara su suka fita dasu

Asma'u nazaune akan gado khadeeja tashigo kusa da ita tazauna tana fadin ammah kinga gidanki kuwa adduniya wama fiha Yasin aka sakeni tsab zan bata agidan nan gaskiya yahadu

Momy ce taleko tana fadin to khadeeja kuzo mutafi dare yayi konan zaki kuana

asma'u tayi saurin fadin eh Momy kubarta anan

Tashi khadeeja tayi tasukuyo saitin kunnen asma'u cikin rada take fadin ammah gara ma kibarni natafi I'm just 17 karku rudani gashi ahmad baya gari bare ayi namu gobe
Tureta asma'u tayi tana fadin Allah ya shiryeki kekam

Dariya Momy tayi tace tafara halinta ko saurin barin wurin khadeeja tayi tana fadin a'a Momy kawai cewa nayi zaman aure ibada ne yi nayi bari nabari
Dariya Momy tayi tabi bayanta tana ma asma'u seda safe akan se sunzo walimar gobe

Sunkuy dakanta tayi cikin guywowinta tana zubar da kwalla yaune karo nafarko dazata kuana batare da ummanta ko khady ba tunani dai iriiri take yi har dare yayi tsawo amma ba ango ba alamarsa

Gidan yayi shuru ba kajin motsin kowa

har karfe dayan dare amma AK baishigo ba tun tana tsoron shigowarsa har tafara damuwa
Ganin dare yaraba tafara tunanin ko lafiya

Shi kuwa AK yana can wurin aysha yana lallashinta dan tunda taji andaura aure tafara rusa kuka tana shagwaba iri iri

atakaicedai bashi yashigo ba se karfe biyun dare
Ahankali ya tura kofar yashiga tana zaune agefen gado tana gyangyadi

Tsaye yayi daga bakin kofa yana kallonta tana bacci batamasan yashigo ba

Cikin sanda yanufi dan karamin frig din dake gefe ya dauko goran ruwa mai sanyi yadawo tagefenta ya tsaya yana bude gorar ruwan yana murmushin mugunta

Daga goran yayi sama yafara kwarara mata ruwan tundaga kanta

afirgice tafarka tana Jan dogon nunfashi tana goge ruwan fuskarta tana fadin miye haka dan Allah
Wannan wane irin rashin iman....

Nunfashinta ne yakusa dawkewa ganin AK tsaye agabanta rike da goran ruwa fuskarnan tashi kamar baitaba dariya ba

Nunashi tayi dayatsa muryanta narawa take fadin kai....kuma...mekake anan

Kara daure fuska yayi yafara matsowa kusa da ita tana ja dabaya seda yakaita jikin bango

atsorace tarufe idanunta kam tana sauke nunfashi ahankali
Hannunsa daya yakai jikin bangon cikin murya mai kaman rada yake fadin

Kina mamaki ne ...
Son abun duniya ya rufe maki ido har takai baki damu dakisan waye mijinki ba Yaya kamaninsa suke Yaya halayensa suke wannan duk bai dameki ba tunda kinsamu abunda kike kwadayi

Da mamaki tabude idonta tana kallonsa cikin rawar murya tace ni bansan abunda kake magana akai ba

Ban nemi nasan kamanninka ba saboda badan haka na aureka ba

Juyawa yayi yana fadin yes!!! Dama nasan badan haka kika aureni ba sedan kinsan ina da kudi

Matsowa tayi daga jikin bango tana fadin Kaine kudi yadama ni basa gabana na amince da aurenka ne sedan kawai inada tabbacin abbana bazai zaba mun abunda zai cuceniba

Kuma nasan wacece grany shiyasa kawai na amince da na'aureka amma danasan Kaine wallahi daba abunda zaisa na aureka mezanyi da....

Juyowa yayi ahasale ya cabki wuyanta idonshi yayi ja nan take yarikide yazama tamkar wani zaki a tsorace asma'u ke kallonsa tana kokarin kwace wuyanta daga hannunsa amma takasa koda motsa hannunsa ne

Cikin kakkausar murya yake fadin ke bakyama jin kunyar fadan wannan maganr agabana ko kina tunanin bansan ko ke wacece ba idan kinyi nasara akan abokina to ni Nafi karfinki

sena hukuntaki senasa kin tsani rayuwarki I will make ur life a living hell
I will destroy ur happiness daga yanzu kinyi bankuana da farin ciki arayuwarki

ba abunda zai biyo baya se da kinsani danadama kuma bazata miki anfani ba

Turata yayi dakarfi akan gado tafadi tana tari tana shafa wuyanta daysha damka

Hanyar fita yanufa zai fita tayi saurin tashi tashiga gabansa cikin rawar murya take fadin

wai miye laifina da na cancanci wannan hukuncin daga gareka kawai dan na amince da aurenka

Idan kasan bakasona meyasa ka aureni

Kallonta yayi sama da kasa ganin yanda tayi wujiga wujiga ga doguwar rigarta tajike sharkab da ruwa

Kwashewa yayi da dariya wadda daga gani kasan taketa ce kyalkyalata yake bawasa har da dafe ciki baki bude asma'u ke kallonsa takasa magana

cikin dariyar yake fadin come on laugh kiyi dariya kila tazama itace takarshe dazakiyi arayuwarki

Sannan yatsagaita da dariyarsa yamatso kusan yana fadin
Tambayata ma kike wai miye laifinki ko to bari nafadamaki

kinsan ahmad

wane ahmad tafada tana ja dabaya

Wani malalacin murmushi yayi yace karma kice mun harkin manta da saurayinki da kika yaudara bayan kinsa yayi nisa asonki kika watsar dashi kika aureni dan kinji zancan kudi

Kikasa kanwata ta zubar da hawaye daga ranar da taganki a office dinsa daga ranan tadaina farin ciki
kika rabani da aminina tunda muke dashi bamu taba fada ba se akanki
Lokaci guda kika shigo rayuwarmu kika ruguza mana ita dayanzu mosoyiyata ce anan dakin amma adalilinki tana can tana zubar da kwalla

Wannan auren punishment ne agareki sekinyi dakinsanin rayuwarki senasa kin tsani rayuwarki sekowa yasan true color dinki sannan zan sakeki

Yana kainan yatureta daga gabansa yawuce yana banko kofar dakarfi

Nan take jikin asma'u yafara rawa durkushewa tayi awurin tafashe da wani irin kuka mai cin rai cikin kukan take fadin

😭meyake shirin faruwa dani ne menayima waya'nnan mutanen zasu dawki alhakina ni bansan meyake magana akai ba wayyo Allah nah!!!

Saurin safe kanta tayi data tuna maganganunsa

Cike datashin hankali take fadin ohh my god kenan ya aureni ne amatsayin budurwan ahmad ganin dasuka mun a office dinsa ranan tunaninsa nice khadeeja

Wayyo Allah nagodemaka daka kubutar da kanwata daga sharrinsu dayanzu itace ahalin danake ciki yanzu wayyo khadyta Allah yashiga tsakaninki dasu

Haka dai tayi rusa kuka tana sambatu iri iri jin kanta yana Sara mata yasa ta sulale awurin taci gaba da kukanta har bacci yadauketa

AK kuma yana fita daganan farm house dinsa yanufa cikin Daren dayake banisa acan ya kuana se dasafe yanufo gida

Cikin sanda yashigo gidan dan kar kowa yagansa da gudu gudu ya hawra sama yana waigen bangaran grany yana isa yatura kofar yashiga

akuance ya iskota inda yabarta jiya da alama tun baccin jiya da yadauketa bata farka ba da har yanzu kayan jiya ne ajikinta

Toilet yanufa batare da yasake kallon inda takeba

Karan knocking din dataji ne yatasheta daga baccin datake ahankali tafara bude idonta tana fatan duk abunda yafaru jiya yakasance mafarki ne ba gaske ba

Wasu sababbin hawayene suka gangaro afuskanta lokacinda take karema dakin kallo tana tuno abunda yafaru jiya

Jin anata knocking yasa tatashi jiki asanyaye tanufi kofa Sam bata lura da yanayin datake ciki ba

Grany tagani tsaye abakin kofa rike dawata kwalla tana washe baki

Dip murmushin fuskarta yadauke lokaci guda tana kallon asma'u sama da kasa cike damamaki ta ijiye kwallar Tana fadin lafiyanki kuwa asma'u yanaganki haka meyasameki ina abidi din yake

Zatayi magana kenan taji anrungumota tabaya atsorace ta juya dan ganin waye
AK tagani atsaye yana mata murmushi cikin shirinsa tsab yayi kyew matuka sekanshi yake zubawa janyota yayi jikinsa yana fadin good morning darling ...

Baki bude take kallonsa ko kifatawa batayi
Takasa cewa komai

Juyowa yayi yakalli grany dake tsaye tana kallonsu tana murmushin jin dadi
Yace

Ohh grany ashe kina nan kintashi lafiya sannan yamaida kallonsa kan asma'u yana murmushi yace kinganta ko gajiya ce tamata yawa tun jiya dasuka zo take bacci se yanzu da kyar natasheta

Juyawa grany tayi tana murmushi tace kuyi sawri kushirya ana jiranku akasa kashiga da wannan kwallan ciki

Yana ganin grany ta tafi yajanye jikinsa daga asma'u ya wuce batare da yace komai ba
Dakallo tabisa har yafita sannan ta dauki kwallan tashiga da ita ciki

Zaunawa tayi abakin gado tana share hawaye

Sarah ce tashigo dakin rike dawasu kaya ahannunta ta ijiye abakin gadon tana fadin amarsu ta ango ina kwananki

Lafiya asma'u tafada tana kauda kai

Murmushi tayi tace ko dayake ban damu dasanin ya kika kuana ba dan nasan Yayana yakula dake yanda yadace

Kayan tanuna mata tana fadin ga wannan kiyi sawri kishirya ana jiranki

AK ne yashigo yana fadin kidan Zane mata fuska da kawalliya karta tsorata mana yara da jajayen idonta

Dariya suka samata ahasale tadauki kayan tanufi bayi tana fadin
Kune abunda tsoro bani ba

tana shiga ta turo kofar dakarfi
Sedai mamaki ne yakamata ganin bawani alamun wurin wanka awurin

Wani makeken wurine dafadinsa har yafi nadakin girma
Drowa ce gaba daya azagaye dawurin Cike makil da kaya kamar anbude shago dayan gefen kayantane awurin amma yawancinsu dogayen riguna ne se English wear masu bala'in kyew dayan gefen kuma kayan AK ne Jere awurin daga kasa kuma takalmansa ne kala kala gefe guda kuma turaruka ne da kayan shafa kala daban daban sewani daddaden kamshi ketashi awurin

seda ta kwashi tsawon lokaci tana zagaye wurin amma bataga alamun kofa ba tsaki taja tafita tana fadin yanda mai dakin yake arikece haka komai nasa yake ahargitse
ahankali tabude kofar ta leko kanta dan ganin ko suna nan AK kawai ta hango azaune yana waya
tsaye tayi tana kallonsa tana wasa dayatsunta
Chapter 21 · 0% Book details