← Book details Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 20 OF 84

Sashe 20

Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dirowa daga kan gado sarah tayi tana fadin haba nifa nasani seda nagayama ahmad yarinyar nan basonsa takeba kawai kudinsa takeso shine yanzu taji AK hausawee yana Neman aurenta mezai hana ta amince bayan tasan ya ninka ahmad kudi

To yanzu miye abun yi inji aysha datakejin kamar ta kurma ihu saboda tashin hankali

mikewa AK yayi yana fadin kawai zanje nasamu grany nagayamata abunda yake faruwa inada tabbacin ita dakanta zata nemi afasa auren

saurin riko hannunsa tayi tana fadin Yaya dan Allah kataimake ni kar kafasa aurennan
Shiga gabanta aysha tayi cike da Bacin rai tace sarah hankalinki daya kike fadan wannan maganar kuwa

Tureta sarah tayi seda takusa faduwa AK yayi saurin rikota tafado kansa

Cikin daga murya sarah tanunata dayatsa tace

da yayana nake magana bake ba so stay out of it

Gefen fuskarta AK yashafa da hannunsa yana fadin come down baby take it easy

meyasa kike so na aureta

Hannunsa takamo cikin dasashshiyar muryanta take fadin
Yaya kaga kai kasan yarinyar kasan cewa kudi ne kawai agabanta mayaudariya ce shikuma ahmad bai saniba ko zamu shekara muna fadamasa ba yarda zaiyi ba Idan har kafasa aurenta shi zai aureta kaga zata cutar dashi nasan kana son ahmad bazaka so wani Abu yasameshi ba so please help us !!!

No sarah I can't do this bazan iya auren yarinyar da ahmad yake mutuwar so ba

Yaya please kafahimci abunda nake nufi natabbata ba ahayyacinshi yake ba wayasani ma ko asiri tamasa kawai dan tacimma nufinta akansa kaga idan ka aureta zamu koyamata darasi shikuma ahmad zai gane ba dagaske take sonshi ba natabbata zai dawo gareni kai kuma ka ceto abokinka daga hannunta

Shiru yayi nadan lokaci yana tunani

Aysha ce tadafa kafadansa tana fadin AK dan Allah kar kayarda da shirmen sarah tayama zaka sauri wannan yarinyar bayan kasan ahmad yana sonta dawane ido zaka kalleshi

Katseta yayi dafadin

ZAN AURETA KODAN FARIN CIKIN KANWATA

Sannan naceto abokina daga tarkonta I will punish her senasa ta tsani rayuwarta se nasa ta durkusa gaban ahmad da sarah tanemi yafiyarsu

Rungumeshi sarah tayi cike dafarin ciki tana fadin Yaya thank u
You are my hero

Girgiza kai aysha tayi tafita daga dakin aguje tana sharan kwalla

Dakallo AK yabita yana yunkurin binta sarah tarikoshi tana fadin a'a barta Yaya zan mata magana nasan zata fahimceni

Ok bari nasa akawomaki wani Abu kici se kisha magani

Bakin gado yakaita yana fadin come and have some rest

Bayan kuana biyu......

Shirye shirye yakan kama atsakanin gidajen biyu dan tuni magabatan ahmad suka suka je sukasami abba da duk wani abu na al'ada kuma sukace basa bukatar komai daga wajan iyayen amarya abba yayi farin ciki matuka nan take aka tsaida dawrin aure ranar juma'a a central mosque

Umma ma shiri take bana wasa ba gyaran jiki asma'u kesha nafitan hankali Umma dakanta kemata dama guana ce awannan Wurin cikin kuana biyu asma'u ta canza tayi wani fresh da ita ko ina bata zuwa daga daki se bayi sedai daga ka ganta kasan tana cikin damuwa nakadan ba

Su khadeeja da nusaiba ba'akama hannun yaro kullun suna zirga zirgan zuwa kasuwa da shagon dinki damma abba yace bawani party ko dinner nan daza'ayi ana dawra aure akayi walima za'akai amarya dakinta
Bayanda basuyi dashiba amma yaki
haka suka hakura

Abangaren grany ma tagama shirinta tsap yau za'akai lepe akwatina goma shabiyu kuma tsadaddun kayane acike makil bawanda zaice a Nigeria ta hada lepenta ko yan uwansu sundawka akasan waje aka hado

Sarah ma tsake da ita ake komai tun grany tana mamaki har tasake sukaci gaba dashiri

AK kam idan bawanda yasani ba bawanda zaice shine angwan bayanda grany batayi ba dashi akan yaje Yaga asma'u kafin dawrin aure amma yaki ba inda yake zuwa daga daki sai masallaci rashin ahmad akusa dashi duk seyaji bayajin dadi kuma har yanzu yana jimamin tayadda ahmad zai fuskanci abun anya kwa baiso kansa dayawa ba wata zuciyar tace ai kayine saboda shi kuma sadaukarwa ce wata rana shidakanshi zai godemaka akan abunda kayimasa

Da wannan tunanin yake dan samun natsuwa amma ya yanke shawaran tura ahmad Turkey saboda bayaso yasan dazancen auren harsai komai ya kammala

Abangaren aysha kuwa
duk dacewa sarah tashayo kanta ta amince da maganar auren amma sam takasa sakewa tana tunanin matakin da iyayenta zasu dawka akanta idan suka dawo dan duk abunda yafaru itace sila
Ga inna ladidi da bashir sun sakata agaba da tsokana wai tayi kuantai wani lokaci tahade fuska ko tayi tsaki wani lokacin har kuka yitake

ganin abun yayi yawa tashirya zatayi tafiya amma AK yahanata wai tatsaya ta tayashi cin uban amaryarshi ....lol😅
[18/07, 15:04] Hubbey Frd Ameena Kn: 📚📚📚📚📚📚
👨‍👧 _DOMUN KANWATA_ 👩‍👧

Na( Maryam Muhammad jibril)

6⃣5⃣

Gida yasha gyara banawasa ba hatta paitin gidan ansake shi

sedai AK bai yarda kowa yasan da zancen aurensa ba saboda bakowa yasan asalin sunansaba kowa yafi saninsa da AK hausawee

tun ajiya yayi nasaran tura ahmad turkey kan harkokin kasuwancin su batare da ahmad yasan zancan auren aminin nasa ba haka yatafi yana kokonton akwai abunda AK keboye masa ko khadeeja ma se awaya yafada mata zancan tafiyarsa

seda grany tamatsama AK sannan ya amince akan zaije ya gaida abba da Umma sannan yaga asma'u daga can

Seda yafara zuwa wurin abba yagaidashi cike da ladabi da girmamawa yasamu tarba ta musamman daga wajan inna dan rasa inda zata sashi tayi
yadan jima awurinsu seda sukayi sallar isha'i sannan yawuce gidan su asma'u bayan ya ijiye mata bandir din kudi itada sauran mutanen gidan

Yana isa gidan su asma'u aka mishi iso har cikin palon gidan
Nan ma cike da ladabi yagaida Umma da sauran mutanen dasuka zo taron biki Umma tayi farin ciki matuka saboda tayaba da nagartar AK nan take taji ya kuantamata duk wani zargi yafita aranta tasamu nutsuwa

Bayan sungaisa da Umma tanufi ciki akan zata turo asma'u sugaisa

Dakin asma'u tanufa cike da farin ciki

Bakin gado ta iskota azaune khadeeja kuma tana gefe tana sallah

Kusa da ita Umma tazauna tana fadin asma'u tashi kije Ku gaisa ya iso

Tashi asma'u tayi jiki asanyaye tana fadin Umma kidan jira khady tagama tarakani mana

Daure fuska Umma tayi tace dan Allah wuce yana jiranki me khadeeja zata maku banda shirme da surutu

Tafa hannu khadeeja tafarayi alaman adan jirata

Dariya Umma tayi tace ai kuma sedai kiyi
Sannan tajuyo tana ma asma'u alamar ta tafi

Fita tayi daga daki tana gyara zaman gyalen data rufe fuskarta dashi

Tunda tanufo palon wani fitinannen kanshin turare yadaki hancin AK shakan iska yayi ya furzar yana lumshe ido yana hangota ya kauda kai yana daure fuska

Ahankali takaraso palon tazauna daga gefe ta takure wuri guda tana gaidasa

Wani kallon tsana yawatsa mata aransa yana fadin afuska kamar mutuniyar arziki dama kindaina ba kanki wahala dan nasan ainahin wacece ke

Mamaki ne Yakama asma'u jin bai amsa gaisuwarta ba kamar tadago takallesa se kuma tadake data tuna bawannan ne karo nafarko dayafara mata haka ba

Shuru sukayi apalon bawanda yace komai har natsawon lokaci

Wata karamar yarinya ce tazo wucewa ta palon AK yakirata

Tana zuwa kusa dashi tagaidashi yace ya sunanki tace nafisa
Yace yawwa nafisa je kicema Umma uncle zai tafi
Dagudu yarinyar ta tafi tana fadin toh
Haushi ne Yakama asma'u ahasale tamike tanufi dayan dakin tana jan tsaki

Da kallo yabita yana murmushin mugunta aransa yana fadin kin kusa shigowa hannu yarinya wannan tsiwar taki zata zama tarihi arayuwarki

Shigowan Umma ne yakatse mashi tuna ninsa mikewa yayi yana fadin Umma nizan wuce dare yayi se wani lokacin
Murmushi Umma tayi tace to Allah yakaimu ina ita kuma wannan yarinyar take

Murmushin yake yayi yafita yana fadin Umma kibarta kawai tahuta gajiya ce tamata yawa zamuyi waya anjima

Murmushi Umma tayi tace to shikenan ka gaida gida Allah yakiyaye

Khadeeja ce tafito aguje tana gyara zunbulelen hijabinta tanufi waje tana salati
Dakallo Umma tabita tana dariya
Dawowa tayi jiki asanyaye tazauna tana fadin haba Umma meyasa zakimun haka kinsan kwa yanda nakosa naga mutuminnan shine zaki mun cikas

Dariya Umma tayi tace to kuana nawa yarage khadeeja har sai kin gaji da ganinsa

Langwabe kai tayi tace Umma bazaki gane ba....

bata karasa ba tahango damen kudi akan kujerar da AK yatashi

Saurin tashi tayi tanufi wajan tana fadin umma ango yayi kwai

Kauda kai Umma tayi tana fadin kefa kin cika shirme wane irin kwai kuma

Kudin tadakko tanufi umma tana washe baki tace wannan shine fidduniya hasanatan
Karban kudin Umma tayi tace kawo khadeeja nabama asma'u wayasani ma ko yamanta ne mukuma mayun kudi kawai muhau kai ni wallahi da nagansu kafin yatafi da bazan karba ba
Kinga ko yanzu yamuka kare da tsegumi wai auren kudi mukama asma'u

Tsaki khadeeja taja tace Umma idan kika biye ta mutane to ko abinci bazakiciba Allah dai yabasu zaman lafiya kawai

Hannunta takai kan kudin tana fadin amma dai wannan kwan kikawoshi nasoyeshi

Bige hannunta Umma tayi tace dallah can matsa kudin nan ijiyesu zanyi khadeeja gaskiya bazan Ciba

Tashi khadeeja tayi tana kuasar hijab dinta tawuce daki tana fadin kawai dai ki ijiye inda bazan ganiba

Rana bata karya
Yau takasance juma'a kuma itace ranar daurin auren AK da asma'u

Dasafe misalin karfe 11narana sarah da aysha ne zaune abangaren AK suna fira

AK yadago yakalli sarah yana murmushi yace ya ake ciki ne wai zancan bikin nan wane shirye shirye kukeyi

Dariya tayi tace bawani shirin da ake ni abun ma dariya yake bani kaman wasan yara

Dariya aysha tayi tace amma ina mamakin meyasa dangin amarya ko kawayenta basu nemi wani Abu da yashafi kudi ko gudunmawa daga wajan angoba

Tashi AK yayi yanufi daki yana fadin abbanta yace bawani shagalin da zasuyi walima kawai ta isa

Sarah tace eh haka naji abakin grany

Mu kuma idan ankawota zamu hada dan kwarya kwaryan party anan gidan daganan kuma kowa ya watse

Aysha tace AK ya kukayi da momyn ahmad dataji zaka auri wata daban daki yashiga yana fadin bansan yasukayi da grany ba nasan abakinta taji

Misalin karfe 14:00 dubbanin jama'a suka shaida *auren* ABID da ASM'AU akan sadaki 500.000
a central mosque dake Abuja
Chapter 20 · 0% Book details