← Book details Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 64 OF 84

Sashe 64

Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bincika office din tafarayi sedai bataga zanen ba

dariya jamilu yahau yi yana fadin kicigaba da dubawa mana ko kingaji ne ga Wanda ya satar miki Zane nan agabanki kina kallo amma kinzo kina tuhumata ......yakarashe maganar yana nuna ahmad

Zaro ido ahmad yayi yana kallonsu yace wa.....ni akan wane dalili zan saci zanen dani nayishi da hannuna kuma tunda nake bantaba satar Zane se yau ne zan fara

"Ah toni shekara nawa nayi ina aiki anan shine yau zata thumeni dasata

nufo wurinsa asma'u tasakeyi tana fadin eh natuhumeka saboda nasan zaka iya yin abunda yafi haka dan nace seka biyani kudina kuma bakada inda zaka samesu shiyasa kazabi kasacemun Zane dan kasayar kasami kudin

Saurin rikota AK yayi yana fadin ya isa haka asma'u karfa kimanta uncle dina ne fa kuma ni natabbata bashibane kawai dai shedanne yake nema yashiga tsakaninku

Cike da takaici ahmad yace akwai wani shedan din dayawuce shi har ni zai kalawa sata

Kallonsu AK yayi yana shafa kai yace kunga mubar wannan magnar dan allah muje muci gaba da bincikawa natabbata zamu sameshi

Kin tafiya asma'u tayi taciro wayarta a alijihu tana fadin dama yau ne ranar karshe da nabaka kuma yanzu zan turaka inda yafi dacewa dakai

Dariya yayi yana nuna ahmad yace kinga semu tafi tare dan dole shima kiyi kararshi akan batar da zanen dayayi dan yana cikin dokar wannan company

Juyowa tayi tana kallon ahmad taji yabata tausayi yanda taga damuwa karara afuskarsa

Maida wayar tayi aljihu tajuya afusace tafita daga office din su ahmad suka bi bayanta danci gaba da binciken kowa na company din

Dawowa takarayi office din har kusan jamilu ta tsaya tana kallonsa da jajayen idanuwanta cikin murya mai kaman rada tace nasan cewa kai kasaci wannan zanen gara ka mayarmun dakayana tun kafin lokaci ya kuremaka..... jamilu idan kasake nakamaka wallahi sekayi nadamar ranan haihuwarka that's my last warning.....tana kainan tajuya tafita tabarshi atsaye yana binta da kallo mai cike da tsana seda yatabbatar ta tafi sannan yazo yarufe kofar yacigaba da wayarsa

tana fita office dinta tanufa dan ita tasan cewa ba Wanda yadauki wannan zanen se jamilu

wayarta tadauka tarasa wama zata kira can tayi dialing numban Umma tajima tana ringing sannan tadaga shiru asma'u tayi takasa magana tana ji Umma nasallama amma batace komai ba se kukan datake dannewa har kiran ya katse sannan tadora kanta saman table tafashe da kuka mai cin rai

Khadeeja dake kusan Umma zaune takarbi wayan tana fadin waye

tabe baki Umma tayi tace bansaniba inata magana shiru nikuma nakashe

Shiru khadeeja tayi nadan lokaci sannan tamike tanufi dakinta dawayar tana shiga tadanna kira jin ringing yasa asma'u tadago tana share hawayenta takai wayar kunnenta batare datayi magana ba

Shiru sukayi nadan lokaci sannan khadeeja takatse shirun cikin sassanyar murya tace

Ya kike......

gashewa asma'u tayi da kuka tana rike wayar dahannu biyu takasa magana itama khadeeja hawayen ne suka zubo mata cikin rawar murya tace I am always waiting for ur call ....meyasa kika dau lokaci kafin ki kirani

Cikin muryan kuka asma'u tace khady kifito waje gani nan zuwa yanzu......

ba'adau lokaciba segata tayi parking akofar gida dagudu khadeeja ta isa wurinta suka rungume juna gaba dayansu kowacce nasharan kwalla sun jima ahaka kafin khadeeja ta janye jikinta tana rike da hannun asma'u tace ammah miyake damunki ne naga kamar kina cikin damuwa

nunfashi taja tafurzar tana jinginuwa da motarta tace khady damuwa ba kadan ba daga ranar da nagane cewa rayuwar ABI da dukiyarsa suna cikin hatsari daga ranar nayi ban kuana da kuanciyar hankali

Kusa da ita khadeeja tamatso cike da mamaki tace kamar ya ....

"Wato khady....ranan naje company inaso inga ABI se naji Uncle jamilu da aysha namaganar shirinsu akan mallake dukiyar ABI dadai sauran abubuwa marasa dadin ji ....banjira naga ABI ba kawai nabaro company din alokacin narasa mezanyi ta ina zanfara kawai se naje nasami grany nagayamata komai nan take mukayanke shawaran kafin muceto dukiyarsa to dole se an kwaceta daga hannunsa kinji dalilin dayasa muka shirya wannan plan din to daga baya nagane duk yanda muka dauki abun ya wuce haka uncle jamilu gaba daya yabi takan kudi masu yawa sauran nasan konawane sauran kuma allah kadai yasani ....bansan ko ahmad ya gayamiki zancan aysha nada ciki ba ....to daga baya nagane cikin bana ABI bane kawai laka masa tayi dan tacimma burinta naya aureta .....bangama magance wa'innan matsalolin ba gashi yanzu ansace Sabin zanen da ahmad yayi ....matsalar har mun sayarda zanen bansan mezai biyo baya ba idan Wanda yasata yasayar dashi ......

Ajiyar zuciya khadeeja tasauke tana jinjina lamarin tace to yanzu miye abunyi

zatayi magana kenan sukaga Umma tsaye daga bakin get tana kallonsu sunkuy dakai asma'u tayi tana runtse idanuwanta wasu hawayen nagangarowa akan kuncinta

Karasowa Umma tayi taja hannun khadeeja afusace tana mata fadan tsayuwar metake da asma'u

Kuka khadeeja tafarayi tana fadin Umma dan allah kitsaya ki saurareni dagowa asma'u tayi tana mata alamar tayi shiru amma bata kulataba tahau ba Umma labarin abunda yafaru

Cike da tausayi Umma ke kallon asma'u cikin sassanyar murya tace asma'u meyasa baki gayamun ba kya bukatar albarka tane ina fushi dake shiyasa abubuwan suka jagule maki amma yanzu danasani kinga zan tayaki da addu'a

dagudu asma'u tazo tarungume Umma tana sakin kukan dazan iya cewa na fadin ciki ne

Shafa kanta Umma tayi tana samata albarka tace kike asma'u je kifuskanci makiyanku insha allahu kezakiyi galaba akansu albarkata tana tare dake allah zaimiki jagora

Janyo jikinta tayi daga na Umma tana murmushi tace nagode Umma kuma insha allahu namiki alkawarin sena tuna musu asiri gaba dayansu senasa sunji kunyar Kansu da Kansu

tana kainan tajuya tanama khadeeja alama da hannu tazagaya suka shiga mota atare tafigeta aguje suka bar layin dakallo Umma tabisu cike dafarin ciki tana musu addu'a har suka bacemata sannan takoma gida

Suna cikin tafiya asma'u tajiyo tana kallon khadeeja tace khady kira ahmad awaya ...

Wayarta taciro tana fadin incemashi me ...

kedai kawai kikirashi

Kiransa tayi bugu biyu yadaga hade da sallama

amsa sallamr tayi tana kallon asma'u tasaka wayar a loudspeaker sannan tace Tarzan ya kake
"ba lafiya deeja wallahi inacikin matsala
Zaro ido tayi kamar dagaske tace meyafaru

"Sabon zanen danayi aka sace ....kuma ni kinsan meyake dauremun kai bafa inda naje yau ko office din AK ban lekaba kawai dai nasan naje wurin securities

Saurin juyowa asma'u tayi takalli khadeeja sannan tacigaba da driving dinta

gyara zama khadeeja tayi tace to kaima meyakaika fita batare dakarufe office dinkaba

"taya zan rufe bayan sarah tana ciki

Saurin taka birki asma'u tayi tana kallon wayar cike damamaki khadeeja kuma sarakan kishi har tahada fuska tana fadin me sarah take acikin office dinka

dariya yayi yafara bata labarin abunda yafaru bata gama jiba tamai sallama hade dakatse kiran tana kallon asma'u tace ya kuma kika tsaya

murmushin gefe tayi tana girgiza kai tace sarah ......sarah....idanuwana sun rufe akan jamilu shiyasa namanta da ita amma tadibo ruwan dafa kanta

khadeeja tace ohh kenan sarah ce tasaci zanen ....to amma meyasa kika ce nakira ahmad

Murmushi asma'u tayi tana tada motar tace saboda nasan zai gayamiki gaskiyar abunda yafaru ....yanzu dani natambayeshi bazai natsu yagayamun duk abunda yafaru ba

yanzu bari muje naga sarah idan har bata sayar da zanen ba zanbuga wasan tare da ita ...ita dakanta zata jefa kanta arami

👨‍👧 _DOMUN KANWATA_ 👩‍👧

1⃣8⃣5⃣

Bayan sun isa gida tana gama parking tafito tabar khadeeja amotar ita kuma tashiga ciki
Zaune suke gaba dayansu apalo harda sarah dake jiran wa'inda zasu sayi zanen sukirata dan tuni uncle jamilu yahadata dasu sedai kudin ne basukai yanda take so tabukaci sukara wani Abu akai shine sukace tajira zasuyi shawara sukirata

Batako kallesuba tahaura sama yitayi kamar zataje bangarensu sekuma tayi saurin karya kuana tawuce dakin sarah agaggauce tafara bincika ko ina amma bataga zanenba har zata fito sekuma takoma tanadaga katifa segashi murmushi tayi tana sauke ajiyar zuciya tamaida katifar tagyara bedsheets din sannan tafito direct waje tanufa batare data shiga bangarensu ba

tana shiga ta tada motar sukabar gidan shiru tayi tana tunanin miye abunyi
Cike da tausayi khadeeja ke kallonta tace ammah tasayar dashine

girgiza kai tayi tace naga zanen yana nan bata sayar ba.... ammah idan muka bata lokaci zata sayar

"To meyasa baki dauko zanen ba tunda kinganshi

"Khady yanzu ba zanen bane agabana nafi bukatar tona mata asiri agaban kowa ABI yasan cewa ita tasaci zanen .....ya amince dasu sosai hartakai baya yarda daduk wani abunda za'a fada akansu .....shiyasa nakeso yagani da idonsa ....yanzu sarah itace first target dina tunani nake ina zansamu Wanda zanhada kai dashi amatsayin Wanda zai sayi zanen ahannunta ....sedai ahalin danake ciki yanzu I can't trust anyone

jinjina kai khadeeja tayi tana fadin ok......nagane to baga Ali namu ba tunda yayi karatu ai zai iya acting din

"wane irin Ali kuma khady kinmanta tasanshine

Dariya khadeeja tayi tana kauda kai tace Ahab ina rabaki da idan allah yatashi tona maka asiri gaba daya basirarka kwancewa take .....kuma ai bahaka zai jemata ba za'a iya canzamishi kamanni kamar irinsu gemu ko gashin baki dadai sauransu

juyowa asma'u tayi tana kallonta nadan lokaci sannan tayi murmushi tace kinkawo shawara mai kyew khady....amma ba Ali bane zai yi wasan kece ....

saurin juyowa khadeeja tayi tana kallonta damamaki tace kamar ya ni kuma.....Ali ma kince tasanshi bare ni....kuma kwata kwata ma bai kamata ace mace ce zata sayi zanen ba .....idan taga haka bazata ba abun mahimmanci ba....kinfasan sarah tanada wayau

Karya kuana asma'u tayi tana fadin ba amace zakije ba amatsayin namiji zakije mata badai kin iya canza murya zuwa tamaza ba to kibarmun sauran ...kedai kawai kisa ido kiyi kallo

ahanya asma'u tasayi sim tasaka awayan khadeeja sannan tasa takira sarah cikin murya irin tamaza akan zatasayi zanen a iya kudin dasarah takeso nan take sarah ta amince suka tsaida wurin dazasu hadu awani katafaren hotel mai hade dawurin cin abinci bayan la'asar

Suna gama wayar asma'u tarungume khadeeja cike da fadin ciki tace bravo!!! Khady gaskiya koni naji wannan muryan zanyarda namiji ne yanzu Abu daya garage mana kamanninki zamu canza izuwa namiji

Itadai khadeeja tayi shiru tazubama asma'u ido dan ganin yanda za'ajuyata takoma namiji
Chapter 64 · 0% Book details