← Book details Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 55 OF 84

Sashe 55

Domin Kanwata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Itama tadamu sosai dayana yinsa amma seta dangantashi da cewar datayi tana sonsa ne ya janyo hakan saboda haka tayanke shawarar janye jikinta daga garesa amma taga hakan ba wani saukin dayakawo

yanzu aysha hankalinta ya kwanta saboda AK yana kulata ko baya gida yana kiranta awaya yaji ya take

Asma'u tadamu matuka da halin da AK ke ciki zaune take tana kuka kawai tayanke shawarar zataje office tasamesa suyi magana

Yamanta da duk abunda tafada dawasa take ba dagaske bane dan haka sudawo yanda suke da matsayin abokai

Sedai wannan ranar takasance bakar rana awurinta seda tayi nadamar zuwa company

Saboda anan taji aysha da uncle jamilu na maganar plan din dasuka shirya dan mallake dukiyar AK daga karshe intakama ma su kasheshi kuma su kori kowa nagidan har taji aysha nafadin

Dady itama sarah daka gani dukiyar nan takeso saboda naji da kunnena tace daga ranar da tashiga hannunta gabadaya zata kori kowa daga gidan haka ma inna ladidi itama dukiyar takeso shiyasa ta aiko bashir yana aiki anan .....

Bata tsaya tagama jin karshen maganar ba ta baro company din ko AK din ma bata ganiba
[19/07, 17:05] Hubbey Frd Ameena Kn: baki da hanci suka saki suna kallonta wasu kuma gulma nacinsu se fadin suke wannan kamar madam Asma'u
badan wannan shigar tata ba daba abunda zai hana muce itace dan gaskiya kamar tabace

Bakin takalmi ne akafanta (cover shoe👢) tana sanye da wando tight light blue se T-shirt dinta fara tadoro dark blue din jacket maidan tsayi daidai guywa tayi rolling dabakin gyale fuskanta yasha make up tana sanye da bakin glasses afuskanta wanda shi yakara fito da ainahin kyawun fuskarta

lafiyayyen agogon fata ne daure ahanunta se wani dan karamin zoben azurfa makale ayatsanta

tsayawa fadar haduwar wannan yarinyar bata lokaci ne kana ganinta zaka rantse ba yar Nigeria bace ko daga yanayin shigarta kawai ka kalla kasan kudi sun zauna

Glasses dinta ta cire ta sakala shi awuyan rigarta ko kadan ba alamun far'a afuskarta

Kallon ma'aikatan gidan tayi daya bayan daya sannan ta nuna wani dayatsa cikin siriruwar murya tace

Kai zo nan

Jiki narawa ya nufi wajanta yana washe baki ya durkusa har kasa yana gaidata

batare da ta amsa gaisuwarsa ba ta Tamika mai makullin motar tana fadin kashigo mun dakayana ciki

cike da kasaita take takunta kamar bata son taka kasa har ta isa dab da kofar palon sannan taja birki ta tsaya

Hawayen fuskarta ta goge sannan tamaida glasses dinta seda taja dogon nunfashi ta furzar sannan tasa kai cikin gidan

zaune suke gaba daya apalon gidan suna fira aunty sadiya da fitowarta kenan daga kitchen rike da plate din dambun nama bata San lokacinda ya subuce mata ba yafadi kasa ba

gaba daya suka juyo dan ganin meke faruwa sedai lokaci guda sukayin saurin mikewa tsaye suna kallon abin al'ajabi

Nunata sadiya tayi da yatsa baki na rawa tace wa...... Wa nake gani haka kamar asma'u

Kallon kallon akafara tsakaninsu sannan suka jiyo suna kallonta anrasa Wanda zaice wani Abu

ahankali take takunta kanta asama tana bin palon da kallo har ta iso wurinsu sannan ta tsaya tana binsu da kallo daya bayan daya fuskarta ahade ba alamar annuri

karasowa wurinta grany tayi tana kallonta sama da kasa cikin rawar murya tace a....asma'u kece?.... ina kika shiga har tsawon wata guda muna nemanki ?

Jin shiru yasa takara matsowa tana kureta da ido tace wai kodai ba asma'u bace

Ganin batada niyyar bata amsa yasa tajuya tana kallon bashir tace kai je kakira mana Abidi yazo yatayamu ganin ikon allah ....

bata gama karasa maganarta ba AK yashigo palon aguje dan tuni ma'aikatan gidan suka sanardashi zuwanta
Nufo inda take yayi da sauri sauri har yana tuntube yana dariya mai yar sauti yace chitti kece kika dawo haka wow gaskiya kinyi kyew amma wannan shigar ai se ta tsorata mu

yana isowa dap da ita ya tsaya cak yana kallonta tundaga kasa har sama cike da mamki azuciyarsa yana fadin kodai ba chitti bace wannan

Amma jikinsa yana bashi tabbas itace saurin rungumeta yayi dakarfi kamar zai maidata ciki cike da farin ciki yake fadin

Chitti dama kina raye Ashe zan kara ganinki me yasa kika barni alokacinda nafi bukatarki

Koma ina kikaje meyasa baki gayamun muntafi tare ba

Muryansa ne takarye yana kara matseta ajikinsa kamar zai yi kuka
yace chitti u have no idea how difficult it was for me to live without u

nasan namiki laifi but I am sorry bazan karaba zan dawo yanda muke da I promise kuma dama ina so ingayamaki chitti l lo.........

baikarasa ba ta tattaro illahirin karfinta gaba daya tasa hannayenta biyu ta turasa baya dakarfi har saida yakusa faduwa bashir yayi saurin tarosa tabaya

😱Shocking!!!

Zaro ido sukayi gaba daya suna kallon Abu kamar film dan haryanzu basu yarda ba wai dagaske asma'u ce tadawo ba

kara nufota yayi yana fadin chitti yau ni kike turewa haka nasan fushi kike dani har yanzu amma nace kiyi hakuri idan bazaki hakura ba u can punish me bu please don't ever leave me again

Glasses dinta tacire tana nunasa dayatsa cikin kakkausar murya tace kar kasake katabani *AK* ko kamanta cewa banada wani matsayi awurinka ne I am jus a stranger to u saboda haka u have no right to touch me

baki ya saki yana kallonta cike da mamaki yama kasa magana

Wannan wane kalan iskanci ne haka kananin mutane zaki daukemu idan kinmanta mutuncinki ai bazaki manta cewa shi mijinki neba ....uncle jamilu yafada cike da bakin cikin sake ganinta arayuwarsa

Juyowa tayi tana kallonsa fuska adaure sanann ahankali takarasa inda yake tsaye tana nuna AK da yatsa cikin murya mai kaman rada tace

Wannan tsakanina dashi ne ba girmanka bane shiga abunda bai shafeka ba so stay out of it idan zaka iya kallo kayi idan bazaka iyaba kuma se kabar nan

Fizgota aysha tayi ahasale tace malama ki iya bakinki duk fitsarar dakika koyo ta tsaya kansu amma kar kisaka babana aciki

Kuace hannunta tayi tana murmushi tace baban naki yakamata ki gayama ya iya bakinsa baniba

baki suka saki gaba daya suna kallonta cike da al'ajabi

cike da takaici inna ameena tace ke wai ma tukkuna wacece ke dan ni har yanzu banyarda asma'u bace dan ba abunda kuka hada banda kama

Saurin juyowa asma'u tayi tana tafa hannu tace good question inna kab cikinsu bawanda yamun wannan tambayar seke ?

yanzu kuwa zakuji koni wacece

Asma'u Mahammad Magaji ko kuce Asmy Magaji

sannan ina farin cikin sanar daku cewa I am the new owner of the hausawee properties ma'ana namallake duk wata kadara da ajiyayun kudi na AK hausawee

Wani irin wawan jiri ne yadibe jamilu se akan kujera tim nan take zufa ta hau karyomai kamar yashiga kasan shower

saurin dafashi aysha tayi tana mai alamar ya natsu sannan ta tsiyayi jus a copi ta mika mashi

What nonsense... AK yafada yana daka mata tsawa

toshe kunnenta tayi tana runtse ido nadan lokaci sannan tabude idanuwanta tana nufo wurinsa cikin sassanyar murya tace

Easy man ai abun bai kai haka ba idan kabini ahankali zaka fahimci komai

juyo da ita grany tayi afusace ta wanketa da lafiyayyen mari saurin dafe kuncinta tayi tana kalkon grany da mamaki tace grany ni kika mara

"An mareki idan akwai abunda yafi mari ma ya cancanci amaki ke bakiji kunyar furta wannan kazamin furucin agabanmu ba to idan ma wasa kike kidaina dan mu ba abokanan wasanki bane mara kunyar banza kawai

karasowa AK yayi yadafa kafadarta yana fadin yi hakuri grany mudan bita asannu kamar yadda tace inaga daga karshe zamu gane tasamu matsalar kwakwalwa ne shiyasa take wannan abun

Dariya bashir yayi yana fadin kai amma wannan haukar da dadin kallo take Yaya

akwatinta tanufa taciro wasu kardu tana murmushi Tamika ma AK tana fadin ga wannan shizai tabbatar maka da abunda nafada ba hauka bane

Karban takardun yayi yafara dubawa nan take jiri yafara dibansa seda yazauna kan kujera dagowa yayi yana kallonta da jajayen idanunwansa bakinsa narawa amma yakasa furta koda kalma daya

Saurin kauda kanta tayi ta koma gefe ta zauna kafa daya kan daya yafara magana kamar haka

nasan zakayi mamakin ganin abunda nafada gaskiya ne kuma kana so kasan ya akayi sa hannunka yazo kan takardun batare da saninka ba

AK kayi wawta matuka da kayarda cewa haka kawai nake zaune dakai bayan nasan cewa baka sona bana sonka

gaskiya ada nayi niyyar rabuwa dakai amma daga baya nayi wani tunani meyasa zan tafi nabar wannan tarin dukiyar batare Dana dibi kasona ba shiyasa nahakura naci gaba dazama dakai ahaka har zuwa lokacinda nacimma burina

Daga lokacinda nagane illahirin takardun kadarorinka suna wurin grany daga lokacin
nayi iya kokarina wajan cusa yardata azuciyarta har takai ta amincemun nashiga ko ina abangarenta ta wannan hanyar nayi nasarar sace takardun kai kuma nayi anfani da wata hanyar nasa kayi signing dinsu batare dasaninka ba

sanin cewa idan har zan rike dukiya irin wannan ina bukatar experience hakan yasa nashirya tafiya coast zuwa America batare dakowa yasaniba har natsawon wata daya gashi yanzu nagama cikin Sa'a nadawo zan kula da dukiyata yanda yakamata .....takarashe maganar tana kwantar dakanta kan kujera hade da lumshe ido

Tsit palon yayi tamkar anyi ruwa andauke bakajin komai sai saukar ajiyar zuciyoyi daga kowane gefe

AK kam tamkar gunki haka yadawo dan ko yatsarsa yakasa motsawa har yanzu yakasa yarda da abunda kefaruwa yakosa yafarka daga wannan rikitaccen mafarkin mai ban takaici wai chitti ta yaudaresa

Dafasan da bashir yayi ne yadawo dashi hayyacinsa dagowa yayi yana kallonsu daya bayan daya kamar baitaba ganinsu ba har yazo kan asma'u sannan da kyar ya bude bakinsa cikin wata iriyar murya yace but u said u love me

Dagowa tayi tana kallonsa sannan ta kwashe da dariya tace it's all part of my plan so karma kasa abun aranka

Shiru yayi baice komai ba yana kallon takardun hannunsa

Zunbur uncle jamilu ya mike cike da masifa yace kai ina walkahi bazai yiwu ba haba Abu sekace wasan yara tayama za'ayi ace wai keda kikazo jiya jiya har kin mallake gaba daya dukiyar ai baki isa ba wallahi

toshe baki aysha tayi jin katobarar da ya abka
Chapter 55 · 0% Book details