← Book details Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 88

Sashe 9

Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*Nunkuwar* shak'uwarsu da yusuf, nunkuwar soyayyarshi azuciyarta..don a kullum soyayyar yusuf k'aruwa take a zuciyar Hafsah.
Ahakan kuma waya, kawai suke shima ab'oye, amma kullum cikin lallab'ashi take akan lokaci ya kusa da zai zo wajanta..
Wata hira da sukayi, wata rana da daddare suna waya. Ya saisaita murya, dai dai yadda yafi jawo hankalinta gareshi.
"Baby"
Tace "Na,am dear"
"Ina son yi miki wani question ne"
"Ina jinka"
"Wai kina sona kuwa?
Ta d'anyi shiru sannan tace
"Haba dear me yasa kamin wannan tambayar?
Yai k'asa da murya "Am sorry bana nufin b'ata miki rai, ina tunanin, ni kad'ai ke wahalar son ki ne"
Ta marairaice.
"To Ba haka bane wallahi, u know my friend Basma koh, har cewa take wai
'Me yasa nake sonka da yawa ne?
Ya gyara kwanciyar shi, "To wane answer kika bata? "
Haka nace mata, "kanada abubuwan da nake so ne,..an then ka iya soyayya"!!
sai taji yayi dariya ahankali.
"Hahh da gaske ina da abubuwan da kike so kuma na iya soyayya??
Ta gyad'a kai kamar a gabanshi.
"Exactly yadda nake son mijina ya kasance, to haka kake."
Yai ajiyar xuciya "Thank you my hafsat!
Ya fad'a da wata kasalalliyar murya.
"Meya faru?" Ta tambayeshi.
Ya kuma ajiyar xuciya sannan yace "Am bacci nakeji, and abinda kika fad'a yasa naji wani 'Laziness' ya saukar min.
'Kasala kuma'??
Ta tambaya da mamaki.
"Oh, no kada ki damu, ki gaidamin da k'awar taki.. Gud night"Ya kashe wayar.
Sai kawai ta yi kissing d'in wayar, abinda bata tab'a yi ba a tarihin soyayyar su..
Wata ranar juma,a hafsah ta shirya cikin wata doguwar rigar atamfa fiffted. Tayi kyau sosai ta yafa d'an k'aramin mayafi. Batayi kwalliya ba sosai.
Ta fito falo, tace wa mama "Mama zan tafi, "
Maman har da bata kud'in mota.
"don Allah Hafsah kada ki dad'e har abbanku ya dawo"
"In sha Allah"
"Ki duba ta.
"Tom"
Ta rayata jakarta ta fito."
Cewa maman nata tayi wai ' Mamansu basma ce bata da Lpia zataje dubota, wai har asibiti ta kwanta.. 'Wannan shawarar basma ce, da Hafsah ta dame ta ya zatayi da yusuf?'
Tana zuwa unguwar ta kira basman a waya. Don bata san gidan nasu ba, layin ta kwatanta mata, da number gidan. Tana zuwa ta tarar Basman ce kad'ai a gidan sai 'yan aikinsu, maman tata bata nan.
Gidan nasu ya tsaru babu laifi..
Basma ta ruk'unk'ume ta,
" H, Hamid a gidanmu lallai ina da Manyan bak'i.
A falo suka zauna wanda ya had'u da gujeru da adon fulawoyi..
Basma ta sa aka kawo mata kayan ciye ciye..
Kad'an taci. Ta Kalli agogon dake falon.
"Kinga bai Kira ni ba har yanzu, gashi mama tace kada na dad'e."
"Hum, kema ai baki shirya ba"?
Hafsah ta kalleta cikin rashin fahimta.
"Kinga ni tashi muje ki shirya dallah, ahaka zai ganki"?
Taja hannunta, babu musu ta bita.
Wani dak'i suka shiga daya tsaru sosai basma ta nuna mata toilet.
"Ki shiga ki wanke fuskanki"
Ta shiga tayi yadda tace d'in.
Tana fitowa taga rashin ajye mata wasu riga da wando (pencil) iyakacinshi guiwa rigar kuma T. Shirt ce amma bata da hannu.
Ta nuna mata kayan "kisa wannan"
No, basma sunyi k'anana gaskiya"
Ta d'an b'ata fuska
"Kinjiki ai"
Ta mik'a mata wata powder shafa wannan"
Ta karb'a, Hodar ta amsheta sosai.
Ta mik'o mata sauran kayan kwalliyar
"Gasunan bari nayi wanka."
Ta shige toilet.
Hafsah ta yi kyau sosai.
Tana gamawa Basma ta fito d'aure da towel ajikinta da kuma wani d'an k'arami hannunta tana goge jikinta dashi.
"Wow kinyi kyau"
Yanzu dai ga wani humra ki shafa saiki sa kayan."
Ta dakko mata wani towel a drawer ki d'aura wannan sai ki cire gown d'in.
"Hafsah ta kalleta Nifa gaskiya Basma bazan iya fita gurinshi da wannan kayanba"
"So wai meyasa?
Kawai,ki barni da wannan gown d'in yayi ai"
"Nooo, bazaki fara zuwa wurinshi da dressing na wani atamfa ba gaskiya, dole ne ki chanja malama."
"To gaskiya sai dai a chanja wani."
"OK ai ga drawer d'innan duba wanda ya miki.'
Ta fad'a tana nuna mata wardrobe d'inta.
Suna cikin haka wayar Hafsah tayi k'ara, da d'auka da sauri.
"Hello"
Am baby nazo unguwar wane link ne?
"Om..
Ta mik'awa basma ta kwatanta mishi.
"Sai kiyi sauri ki nema wanda zaki sa."
Ta fad'a tana mik'a mata wayar.
* * * * *
* * * * *
Wani kyakywan had'ad'd'en saurayi (First Class) Basma ta yi tozali da shi..
A zatonta da yadda Hafsah ke kwarzanta mata yusuf bata ta'ba zaton yakai Kwatar hakan ba.
(Colour of my dream)
Ta fad'a a zuciyarta.
murmushi kawai yake sakarwa Hafsah, tare da wani irin kallo wanda ya so rikitata.
suka isa wajenshi..
Hafsah ta nemi gefenshi shi ta tsaya.
Ahankali tace mishi
"You're welcome my dear"
Ya zuba mata idanu "Thank you my baby"
"Am mu k'arasa ciki Koh?
Basma ta fad'a.
Sai lokacin ya kalleta. yace
"Sannunki fa"
Tayi wani murmushi cike da gogewa
"Am yawwa..
Basma na gaba suna bayanta..
Wani d'aki ta bud'e musu dake farfajiyar gidan, sanyin AC ga kuma wani daddad'an k'amshi dake tashi..
A wata kujera ya zauna three seater,
Hafsah ta zauna a 'me kallonshi' suna fuskantar juna.
"Am ina zuwa.."
Basma ta fad'a, sannan ta fita, sai wani rangwad'a take.
Falon ya d'anyi shiru, kusan mintuna biyu, sai kawai kallonta da yusuf yake..
"Can taji yace " you look so cute my baby".. Kinyi min kyau."
"Thank you"
Kazo lpia?
"Lpia lau, but full of kewanki amma."
Ya fad'a yana wani d'age gira.
Tayi 'yar dariya.
"Gani nan kam yanzu Koh??
"Ya mamanku"
"She's fine"
Ya d'an gyara zama sannan yace
"Baby baki son ganina koh,? duk na rame, kin hana in ganki..
"Am sorry ba haka bane, na fad'a maka abbanmu ba zai barni fitowa ba, sai nayi candy."
"Hum long distance, u mean bazan dinga ganinki ba koh?
"A,a mana, yanzu ai mun had'u koh?"
"Yes, but this won't satisfy me.
ya zuba mata ido
"Ko dai zaki zo gidanmu ne kawai sai muna hira acan".
Ta d'an zaro ido.
Yayi wata siririyar dariya wacce taji ta har cikin ranta.
"Ba zaki zo ba koh.."?
Ta rufe idonta d'aya da hannunta tana kallonshi da d'aya idon..
'Kallon yayi tasiri a zuciyarshi.'
"Bazaki zo bane Koh?
Tayi shiru
"Uhum..?
Ta kuma yin shiru
"Talk to me mana kinji..?
Basma ce ta shigo da Tray a hannunta taja wani center table ta d'ora akai..
Ta Kalli Yusuf
"Ga drink koh?
"Ok thank you"
Leb'enshi kawai ta kalla ta gane me yake fad'a, saboda a hankali yayi maganar.
'Hafsah ta kalleshi.
"Dear ga Basma fa"
Ya jingina kanshi jikin kujerar, sannan ya kallo Basma, yana jijjiga k'afa.
"Am sannunki koh?
"How are you?
Kut..😒 (Basma ta fad'a azuciyarta) "Rainin sense" wato gayen nan wani nauyin kai ne dashi..😅
Ok bari na zo mishi ta yadda yazo min..

~'To Basma ya kike so ya miki? Koh kece Hafsan ne'*~🤔

Tayi wani murmushi a d'an share tace "Am fine"..
yace "Gud"
"Am yau dai kaga hafsan naka koh??
Yai murmushi sosai wani b'oyayyen kyawunshi ya bayyana
"Of course, alot of thanks to you."
"No ai ana tare ne Koh,?..
Ta Kalli Hafsah..
"Ai kamar sister na take."
"Gud!"
Ya Kalli Hafsah wanda dama Basma ta lura rabin hankalinshi na kanta dama.
"Baby friend enki nada kirki fa."
"Sosai ma, kuwa inji Hafsah"
Sannan ta mik'e ta zuba mishi lemon a cup.. Basma idonta kir tana kallonsu..
K'okari take ta gano a ina ne Hafsah ke da rauni.?
Amma duk kwakwarta bata gano ba.
Sai ma wani sirri data gano a wajen Hafsan.
Wato yadda yanayin 'Movement' motsinta yake da banbanci da na sauran 'yan mata. Bata abu da gaggawa sannan bata da sanya.. komai takeyi cikin nutsuwa take yinsa, sannan tana da shiga rai sosai.
Ta mik'a mishi lemon ya karba yana murmushi.
Ta zuba itama sannan ta dawo ta zauna tana sha..
Am bari na barku haka koh?
Ta Kalli
"Yusuf ka gaida gida"
Ok bye bye"
Hafsah sai kin shigo.
Bayan fitar basma, Yusuf hira ya fara yi mata ta rayuwarshi a k'asashen waje, k'arara yake nuna mata 'banbancin' dake tsakanin can da nan.
Misali acikin labarin shi tsaf yake fad'a mata irin rayuwar shi da 'yan matan shi acewarshi (School mate enshi ne) ko da cikin labarin yakan ce mata "She hugged me and then.." ita dai Hafsah sai dai tajishi da kunne ko tayi murmushi, itama bata son ta nuna mishi 'Gidadanci' kamar yadda yake d'aukar hakan, sai dai a hirar tasu ta fahimci wani abu..
'wato, Yusuf sam bai san wani abu wai shi 'Babu ba' duk da itama ba wai wahalar tasani ba, amma shi batajin yasan da wata abu wai ita wahalar rayuwa..
Tsoron da take ji shine kada 'Banbancin' dake tsakaninsu ya kawo musu matsala acikin alak'ar su.
"Baby meyafaru ne?
Babu komai.
"Sure?
"Yes"
"OK please close your eyes for me!
I have a surprise for you!
Ya fad'a yana kashe miki ido.
"Am ok"
Ta rufe idon..
Tsayawa yayi ya k'arewa fuskartata kallo tun daga saman goshinta har zuwa k'asan hab'arta.. Ahankali yace
"My Baby is beautiful!
Hafsah ta gaji don haka ta bud'e idonta
suka had'a ido.. tare sukayi murmushi "plz baby ki rufe fa"?
"Ok"
Ta kuma rufe idon..
Ya taso ahankali ya iso gabanta.. sunkuyo dai dai saitin fuskarta.
Numfashinsa daya sauka kan fuskantarta yasata saurin bud'e idonta bata shirya ba.
Ta zaro ido.
Yai wata dariya me sauti..
Uhum.. "Calm down"
Ya fad'a cikin rad'a"
Ita dai shiru ta kasa magana.
Hannunta taga ya Kama wanda hakan yasa jikinta b'ari..
Zobe ya ciro daga aljihinshi Gold ne mai kyau, ya fara sa mata ahankali.. tana son ta k'wace hannunta, amma kuma ta kasa, bata
son ta bada kanta da yawa.. Amma azuciyarta Allah Allah take yanayin ya shud'e, gabad'aya nutuwarta bata tare da ita..
Shiko fuskarta kawai yake kallo yana mata murmushi..
Ya gama sa mata amma kuma yak'i sakin hannun na ta.
K'okarin kai hannun nata bakinshi yake.. Ta zaro ido
*"Kiss wai yake shirin min?*😳
(ta fad'a a zuciyarta)
Chapter 9 · 0% Book details