Sashe 72
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bashir yasan hali don haka ya k'araso cikin d'akin.
Lokacin Jamila ta k'arasa mata d'aurin ta zauna.
"Am sorry my yaya, ba abin zafi bane, kiranki ake a waje."
"Shine Bazaka fadamin ba kake kirana kamar nice mufeeda koh."?
Shidai Bashir shuru yayi, Jamila kuma ta zuba musu ido bata son tasa musu baki.
Please Yaya ki zo dai jiranki ake."
Yana gama fad'ar haka ya fice.
Yana fita Jamila tayi magana.
"Ki tashi Hafsah, kinga may be ya dad'e yana jiranki, kinga _no wonder_ ma tun d'azun nan ma shi ya kiraki so kada yace kina mishi wulak'anci don ya biyo ki har gida."
Jamila ta mik'e ta d`auki Jakarta ta bud'e, ta zaro wani pink jambaki da powder nan ta d'azu.
Ta mik'awa Hafsah, Ki shafa wannan lipstick, zai miki kyau, wannan powder shima kuma ki rik'e yana da kyau.
Hafsah ta tsaya saroro tana mamakin Jamila.
Jamila tayi murmushi, ki amsa mana."
Ta ajyewa Hafsah a gefenta.
Nagode Jamila.
Hafsah ta fada, sannan ta d`auki jan bakin ta mik'e ta, Kalli mudubi.
Ta dinga murmushi ganin yacce tayi kyau matuk'a.
Ta dan goga Jan bakin tana murmushi azuciyarta tana godewa Jamila, don yau tana da burin ta yanki ukhasha da yawa.
Wow Jamila thank you fah, dama kefa kin iya kwalliya, amma wanna daurin like irin makeup artist ce
ke.!!
Ta bude drawer zata dakko mayafi.
Jamila tayi murmushi.
Hmm, H hameeed, da gaske d`in ita ce.
Hafsah ta juyo da mamaki.
Jamila ta jinjina kai, Hmm, H. Hammed sana,ar da ake zaton inayi ba ita nake ba yanzu, Allah ne shaida ta, shiyasa nace miki zanzo zuwa na musamman ina so ki bani shawara, inaso na inganta rayuwata nima."
Jikin Hafsah yayi sanyi ta matso a hankali ta kamo, hannun Jamila.
Sam Jamila batayi irin raunin da Hafsah tayi ba, Hafsah har kwalla ce ta cika mata ido.
Jamila ta lura, sai tayi murmushi kawai, ta yarda cewa a duniya bata da kamar Hafsah H hameeed.
"Ki saka kwalli mana."
Jamila ta share zancen da fad'ar haka.
Hafsah ta juya ta d'auka.
Jamila ta sa hannu ta d'akko turaren data gani cikin drawer, sannan ta rufe drawer da murfinta.
Aka kuma turo d'akin, wannan karon mama ce.
Fuska babu annuri sosai ta leko d'akin ta k'are musu kallo, Hafsah nasa kwalli Jamila tsaye.
Jamila tayi saurin cewa, "Sannu mama."
Lokacin ta bude baki zata fara magana.
Maimakon ta amsa ta sai kawai ta fara maganar ta.
"Ke Yaya ba cewa akayi kinyi bako ba."?
Kafin Hafsah ta amsa mata. Ta kalli Jamila "Yawwa."
Hafsah ta juyo.
Mama gani nan fah.
"Zo ki wuce toh."
Sannan ta kalli Jamila. Ki jirata kinji."
Aa mama nima ina sauri ne bari mu fita tare."
Mama bataji dadin hakan ba, kawai sai ta juya tabar musu d'akin.
Jamila ta fesawa Hafsah turare itama ta fesa.
Hafsah ta dakko takalmi a hannu suka fito.
Jamila ta durkusa da suka iso palour, "Mama, sai anjima.!
"To ki gaida gida."
Zasuyi gaba, mama ta kira Hafsah.
Suka fara tafiya sun fita kofar palourn har sun nufi hanyar waje, mama ta kira Hafsah.
Hafsah ta dawo tana mamakin kiran.
"Zauna kiji."
Hafsah ta zauna.
Mama tayi shuru, ta shiga wata sabgar ma.
Kusan minti biyu, suna shurun.
Awaje kuma Jamila na tsaye.
Hafsah ta rasa dalilin kiranta da mama tayi, gashi bata mata magana ba kuma.
"Tashi kije ma kawai .!!
Mama ta fad'a mata.
Da sauri Hafsah ta mik'e ta fita.
Jamila ta tsargu da kiran da akayiwa Hafsah. Amma da Hafsan ta fito bata nuna mata komai ba. suka had'u a harabar gidan.
Ukhasha tun sanda Jamila tazo ta tsaya ya lura da ita, dake suna daga gefe shida Basheer.
Don ya hana Basheer tafiya sai janshi yake da hira.
Acikin hirar ne ya gane cewa Basheer k'anin Hafsah ne, kuma ya ji cewa Basheer ba anan yake karatu ba, kuma shima engineering yake karantawa.
Sannan daga baya yaga Hafsah ta fito, Basheer na ganin fitowarta ya mik'e yayi waje Ukhashatu sallama,
"Agaida gida yaya nah.!"
Ukhashatu ya tsaya yana kallon shi, "Haba aboki ya zaka tafi kuma."?
"Dama zani wani waje ne."
Ukhashatu ya mik'a mishi hannu sukayi musabiha.
"Okey thanks alot, zan kiraka in sha Allah tunda kayi swapping layin."
"Okey nagode ka gaida gida." Inji Bashir.
Hafsah niyya tayi da ta wuce shi, ta raka Jamila in yaso idan ta dawo taje wajenshi. Amma sai ta kasa samun nutsuwa da hakan.
Tana ji ajinkinta kallontan da yake. Kawai sai ta nufi wajen shi. Ganin haka Jamila ma ta bita amma sai ta tsaya daga can gefe.
Wani shudadden murmushi suka dinga yiwa juna, ukhashatu yaji zuciyar shi fes, kamar an wanke mishi, ganinta yake kamar wata sabuwa, yau tayi mishi wani kyau ne na musamman daya tafi da tunaninshi..
Assalamu alaykum.
Cikin sakin murmushinya amsa mata yana k'ara kallon cikin idanunta.
Hafsah ta kawar da kai tana murmushi.
Tana tsaye har yanzu. Ahankali taji yace "Queen!!
Ta amsa mishi da idanu.
Yayi mata nuni da kujera. Sai ta girgiza kai.
Ya kalleta cikin kwayar ido, cikin marairaice fuska yana neman dalili.
Tayi mishi nuni da Jamila.
"Kawata ne mun dad'e bamu haduba for years yau tazo min so zan dan taka mata ne."
Hafsah ta manta da ukhasha take magana, sannan kafe ta da ido da yayi yaja tayi saurin furta wad'annan kalaman babu shiri.
Ukhashatu ya lumshe ido a hankali, sannan ya zuba su can Wajen da jamila take. Hakika farkon tahowarsu tafi mishi kama da k'anwar babar Hafsah, amma da suka doso shi, xubinta da Yanayin shiga yasa yaji ya kori wancan tunanin kuma yaji yana bukatar jin wacece ita."?
Murmushin ya saki, sannan yace "Okey, kuma ba zaki kawota mu gaisa ba."?
Ya fad'a da zolaya.
Hafsah tayi murmushi sannan ta matsa ta kira Jamila.
Cikin yauk'i tazo amma yin tozali da idon ukhasha sai da yasa ta gyara tsayuwarta. Shikuma ya sami dama yayi mata cikakken kallon na seconni a lokacin.
"Sannu Barka da yamma."
Cikin sakin fuska yace "Barka dai."
Hafsah koh sai murmushi ta ke.
Daga nan Jamila ta nemi zata tafi, ta hanyar kallon Hafsah sannan batayi magana ba ta fara tafiya.
Hafsah ta d'agawa ukhasha hannu alamun yayi hakuri tana zuwa. Ta bi bayan Jamila tana murmushi.
A hankali ya sauke ajiyar zuciya. sannan a zuciyarshi ya furta k'awarta."?
Hakika dole yayi nazarin akan al,amran. Kada dai ace Hafsah nayi mishi rufa-rufa ne. Banda haka kawayenta biyu kenan wad`anda kana kallon su zaka d'ora zuciyarka _a layin shakku game da su._ Amma me yasa take ce mishi ta dad'e rabon da ta had'u dasu."?
Me take nufi."?
Anya bata zo da rainin hankali ba.?
Ita kanta tasan basuyi kama da qawayen kirki ba sam shiyasa bata son a ganta dasu, shine dalilin kenan daya sa take yunk'urin kare kanta, ko nisanta kanta dasu idan ya ganta dasu.!!
Ahankali ya furta, _dole na nemi sanin dalili._
Baya mata mummunan zato, amma baya jin zai iya zuba ido tana mu,amala da k'awaye irin wad'annan.
Amma koma menene to dole yasan dalilin daya sa take mishi k'arya.
_Na dad`e ban ganta ba for long ko for years!!_
Shafshaf Hafsah tayi sallama da Jamila hankalin ta duk yayi wajen ukhasha, suka tsayar da Matsaya cewa Jamila zata dawo idan ta dawo daga Dubai.
Yanayinshi ya d'an nuna sanyi. D fara,a ta nufo shi sai yaji sanyi cikin zuciyarshi, tabbas Allah ne yayi mishi gam da katar d`in samunta.. Hakika komai nata yayi mishi. Komai cikin nutsuwa da hankali..
Ahankali cike da kulawa yace mata "Sannu fah."
Muryar tayi tasiri wajen sata saurin amsawa tare da sakin murmushi.
"Yawwa ya kake ya hanya."?
Alhamdulillah hope ban katse muku hira ba.
Hafsah ta girgiza kai.
Noo, dama gaisawa ta biyo mukayi."
Okey, ya fada sannan ya kauda zancen da cewa kamar rad'a. Kinyi min kyau matuk'a, kina da kyau masha Allah."
Hafsah ta saki murmushin jin dadi.
Sannan taji ya kuma cewa, "Ai da gaske you're beautiful shi yasa kika burkita min lissafi.!!
Hafsah ta saki murmushi, tana dan sunkuiyar da kai.
Bayan dan shuru sannan yace, ya mum ya family."?
Suna lafiya lau.
OK so ya kike kema."?
Ya fad'a cike da kulawa wacce zaka karanta kai tsaye cikin idanunshi.
Ahankali tace "lafiya lau.!!
Alhamdulillah, Kinsan dole nayi taking care, na mai sunan Hajiyata.
Hafsah tayi murmushi, sannan ta gyara daidaitonta a kujerar.
"Sunan hajiyarka kenan.?
Yes my queen Hajiyata sunan ta kenan kuma tana so na."!!
Ya k'arashe zancen yana mata murmushi.
"Allah ya kara lafiya.
Ta fad'a a hankali shikuwa yaji ta tarr.
Cikin nuna jin dad`in adduar yace, "Amiin Queen."
Suka d'anyi shuru kafin Hafsah ta dan daga mishi hannu, please "Ina zuwa.!!
Ya girgiza kai yana kallon ta. Ta mishi alamun tambaya da ido.
"Please kada ki tashi.!
"Tayi murmushi, i'm sorry yanzu zan dawo.!!
Yaji dad`in kalmar _i'm sorry_ d`in data ce. Ya saki tattausan murmushi.
"To kije.!
Sannan ya cukune fuska kamar yaron da aka kwacewa alawa.😀
Ta mik'e tana kunshe dariyarta.
Tana juya baya ya zuba mata ido yana k'arewa tafiyar ta kallo, _cikin nutsuwa take._ yana jin dad`in hakan har ta shige kofar cikin gidan.
Ita da mufida suka dawo, ta rakota da try d`in lemo, ita kuma ta taho da snacks da dambun nama..
Suka mishi sallama dukkan su, ya amsa, suka ajye a kan table d`in, sai faman bin hafsah da ido yake.
Mufida ta gaida shi.
Ya amsa cikin sakin fuska sosai.
Hafsah taja kujera ta zauna, ta d'anyi kafin ta dago da niyyar mishi magana.
Karaf idanunsu suka had'u dama shi kallonta yake.
Ta dan kalleshi na seconni itama, shi ko ko kiftawa baiyi ba, hakan ya bata tsoro tayi saurin k'asa da ido ta fasa maganar.
"Itama k'anwarki ce."?
Ta d'aga gira kawai.
Yayi murmushi.
Sannan yace, Hafsah.!!
Ta tsayar da duk tunaninta kanshi amma bata ko motsa ba bare ta amsa.
Ya dace kisan ko ni waye koh."?
Ta saki murmushin jin dad`in zancen.
Ya d'ora "Tun kafin ki gaji dani."
Ta sake yin murmushin dai.
Ya jinjina kai yes, amma kafin in fad'a miki sai kin amsa min wata tambaya.
Ta kalle shi cikin ido tana sauraren shi.
Lokacin Jamila ta k'arasa mata d'aurin ta zauna.
"Am sorry my yaya, ba abin zafi bane, kiranki ake a waje."
"Shine Bazaka fadamin ba kake kirana kamar nice mufeeda koh."?
Shidai Bashir shuru yayi, Jamila kuma ta zuba musu ido bata son tasa musu baki.
Please Yaya ki zo dai jiranki ake."
Yana gama fad'ar haka ya fice.
Yana fita Jamila tayi magana.
"Ki tashi Hafsah, kinga may be ya dad'e yana jiranki, kinga _no wonder_ ma tun d'azun nan ma shi ya kiraki so kada yace kina mishi wulak'anci don ya biyo ki har gida."
Jamila ta mik'e ta d`auki Jakarta ta bud'e, ta zaro wani pink jambaki da powder nan ta d'azu.
Ta mik'awa Hafsah, Ki shafa wannan lipstick, zai miki kyau, wannan powder shima kuma ki rik'e yana da kyau.
Hafsah ta tsaya saroro tana mamakin Jamila.
Jamila tayi murmushi, ki amsa mana."
Ta ajyewa Hafsah a gefenta.
Nagode Jamila.
Hafsah ta fada, sannan ta d`auki jan bakin ta mik'e ta, Kalli mudubi.
Ta dinga murmushi ganin yacce tayi kyau matuk'a.
Ta dan goga Jan bakin tana murmushi azuciyarta tana godewa Jamila, don yau tana da burin ta yanki ukhasha da yawa.
Wow Jamila thank you fah, dama kefa kin iya kwalliya, amma wanna daurin like irin makeup artist ce
ke.!!
Ta bude drawer zata dakko mayafi.
Jamila tayi murmushi.
Hmm, H hameeed, da gaske d`in ita ce.
Hafsah ta juyo da mamaki.
Jamila ta jinjina kai, Hmm, H. Hammed sana,ar da ake zaton inayi ba ita nake ba yanzu, Allah ne shaida ta, shiyasa nace miki zanzo zuwa na musamman ina so ki bani shawara, inaso na inganta rayuwata nima."
Jikin Hafsah yayi sanyi ta matso a hankali ta kamo, hannun Jamila.
Sam Jamila batayi irin raunin da Hafsah tayi ba, Hafsah har kwalla ce ta cika mata ido.
Jamila ta lura, sai tayi murmushi kawai, ta yarda cewa a duniya bata da kamar Hafsah H hameeed.
"Ki saka kwalli mana."
Jamila ta share zancen da fad'ar haka.
Hafsah ta juya ta d'auka.
Jamila ta sa hannu ta d'akko turaren data gani cikin drawer, sannan ta rufe drawer da murfinta.
Aka kuma turo d'akin, wannan karon mama ce.
Fuska babu annuri sosai ta leko d'akin ta k'are musu kallo, Hafsah nasa kwalli Jamila tsaye.
Jamila tayi saurin cewa, "Sannu mama."
Lokacin ta bude baki zata fara magana.
Maimakon ta amsa ta sai kawai ta fara maganar ta.
"Ke Yaya ba cewa akayi kinyi bako ba."?
Kafin Hafsah ta amsa mata. Ta kalli Jamila "Yawwa."
Hafsah ta juyo.
Mama gani nan fah.
"Zo ki wuce toh."
Sannan ta kalli Jamila. Ki jirata kinji."
Aa mama nima ina sauri ne bari mu fita tare."
Mama bataji dadin hakan ba, kawai sai ta juya tabar musu d'akin.
Jamila ta fesawa Hafsah turare itama ta fesa.
Hafsah ta dakko takalmi a hannu suka fito.
Jamila ta durkusa da suka iso palour, "Mama, sai anjima.!
"To ki gaida gida."
Zasuyi gaba, mama ta kira Hafsah.
Suka fara tafiya sun fita kofar palourn har sun nufi hanyar waje, mama ta kira Hafsah.
Hafsah ta dawo tana mamakin kiran.
"Zauna kiji."
Hafsah ta zauna.
Mama tayi shuru, ta shiga wata sabgar ma.
Kusan minti biyu, suna shurun.
Awaje kuma Jamila na tsaye.
Hafsah ta rasa dalilin kiranta da mama tayi, gashi bata mata magana ba kuma.
"Tashi kije ma kawai .!!
Mama ta fad'a mata.
Da sauri Hafsah ta mik'e ta fita.
Jamila ta tsargu da kiran da akayiwa Hafsah. Amma da Hafsan ta fito bata nuna mata komai ba. suka had'u a harabar gidan.
Ukhasha tun sanda Jamila tazo ta tsaya ya lura da ita, dake suna daga gefe shida Basheer.
Don ya hana Basheer tafiya sai janshi yake da hira.
Acikin hirar ne ya gane cewa Basheer k'anin Hafsah ne, kuma ya ji cewa Basheer ba anan yake karatu ba, kuma shima engineering yake karantawa.
Sannan daga baya yaga Hafsah ta fito, Basheer na ganin fitowarta ya mik'e yayi waje Ukhashatu sallama,
"Agaida gida yaya nah.!"
Ukhashatu ya tsaya yana kallon shi, "Haba aboki ya zaka tafi kuma."?
"Dama zani wani waje ne."
Ukhashatu ya mik'a mishi hannu sukayi musabiha.
"Okey thanks alot, zan kiraka in sha Allah tunda kayi swapping layin."
"Okey nagode ka gaida gida." Inji Bashir.
Hafsah niyya tayi da ta wuce shi, ta raka Jamila in yaso idan ta dawo taje wajenshi. Amma sai ta kasa samun nutsuwa da hakan.
Tana ji ajinkinta kallontan da yake. Kawai sai ta nufi wajen shi. Ganin haka Jamila ma ta bita amma sai ta tsaya daga can gefe.
Wani shudadden murmushi suka dinga yiwa juna, ukhashatu yaji zuciyar shi fes, kamar an wanke mishi, ganinta yake kamar wata sabuwa, yau tayi mishi wani kyau ne na musamman daya tafi da tunaninshi..
Assalamu alaykum.
Cikin sakin murmushinya amsa mata yana k'ara kallon cikin idanunta.
Hafsah ta kawar da kai tana murmushi.
Tana tsaye har yanzu. Ahankali taji yace "Queen!!
Ta amsa mishi da idanu.
Yayi mata nuni da kujera. Sai ta girgiza kai.
Ya kalleta cikin kwayar ido, cikin marairaice fuska yana neman dalili.
Tayi mishi nuni da Jamila.
"Kawata ne mun dad'e bamu haduba for years yau tazo min so zan dan taka mata ne."
Hafsah ta manta da ukhasha take magana, sannan kafe ta da ido da yayi yaja tayi saurin furta wad'annan kalaman babu shiri.
Ukhashatu ya lumshe ido a hankali, sannan ya zuba su can Wajen da jamila take. Hakika farkon tahowarsu tafi mishi kama da k'anwar babar Hafsah, amma da suka doso shi, xubinta da Yanayin shiga yasa yaji ya kori wancan tunanin kuma yaji yana bukatar jin wacece ita."?
Murmushin ya saki, sannan yace "Okey, kuma ba zaki kawota mu gaisa ba."?
Ya fad'a da zolaya.
Hafsah tayi murmushi sannan ta matsa ta kira Jamila.
Cikin yauk'i tazo amma yin tozali da idon ukhasha sai da yasa ta gyara tsayuwarta. Shikuma ya sami dama yayi mata cikakken kallon na seconni a lokacin.
"Sannu Barka da yamma."
Cikin sakin fuska yace "Barka dai."
Hafsah koh sai murmushi ta ke.
Daga nan Jamila ta nemi zata tafi, ta hanyar kallon Hafsah sannan batayi magana ba ta fara tafiya.
Hafsah ta d'agawa ukhasha hannu alamun yayi hakuri tana zuwa. Ta bi bayan Jamila tana murmushi.
A hankali ya sauke ajiyar zuciya. sannan a zuciyarshi ya furta k'awarta."?
Hakika dole yayi nazarin akan al,amran. Kada dai ace Hafsah nayi mishi rufa-rufa ne. Banda haka kawayenta biyu kenan wad`anda kana kallon su zaka d'ora zuciyarka _a layin shakku game da su._ Amma me yasa take ce mishi ta dad'e rabon da ta had'u dasu."?
Me take nufi."?
Anya bata zo da rainin hankali ba.?
Ita kanta tasan basuyi kama da qawayen kirki ba sam shiyasa bata son a ganta dasu, shine dalilin kenan daya sa take yunk'urin kare kanta, ko nisanta kanta dasu idan ya ganta dasu.!!
Ahankali ya furta, _dole na nemi sanin dalili._
Baya mata mummunan zato, amma baya jin zai iya zuba ido tana mu,amala da k'awaye irin wad'annan.
Amma koma menene to dole yasan dalilin daya sa take mishi k'arya.
_Na dad`e ban ganta ba for long ko for years!!_
Shafshaf Hafsah tayi sallama da Jamila hankalin ta duk yayi wajen ukhasha, suka tsayar da Matsaya cewa Jamila zata dawo idan ta dawo daga Dubai.
Yanayinshi ya d'an nuna sanyi. D fara,a ta nufo shi sai yaji sanyi cikin zuciyarshi, tabbas Allah ne yayi mishi gam da katar d`in samunta.. Hakika komai nata yayi mishi. Komai cikin nutsuwa da hankali..
Ahankali cike da kulawa yace mata "Sannu fah."
Muryar tayi tasiri wajen sata saurin amsawa tare da sakin murmushi.
"Yawwa ya kake ya hanya."?
Alhamdulillah hope ban katse muku hira ba.
Hafsah ta girgiza kai.
Noo, dama gaisawa ta biyo mukayi."
Okey, ya fada sannan ya kauda zancen da cewa kamar rad'a. Kinyi min kyau matuk'a, kina da kyau masha Allah."
Hafsah ta saki murmushin jin dadi.
Sannan taji ya kuma cewa, "Ai da gaske you're beautiful shi yasa kika burkita min lissafi.!!
Hafsah ta saki murmushi, tana dan sunkuiyar da kai.
Bayan dan shuru sannan yace, ya mum ya family."?
Suna lafiya lau.
OK so ya kike kema."?
Ya fad'a cike da kulawa wacce zaka karanta kai tsaye cikin idanunshi.
Ahankali tace "lafiya lau.!!
Alhamdulillah, Kinsan dole nayi taking care, na mai sunan Hajiyata.
Hafsah tayi murmushi, sannan ta gyara daidaitonta a kujerar.
"Sunan hajiyarka kenan.?
Yes my queen Hajiyata sunan ta kenan kuma tana so na."!!
Ya k'arashe zancen yana mata murmushi.
"Allah ya kara lafiya.
Ta fad'a a hankali shikuwa yaji ta tarr.
Cikin nuna jin dad`in adduar yace, "Amiin Queen."
Suka d'anyi shuru kafin Hafsah ta dan daga mishi hannu, please "Ina zuwa.!!
Ya girgiza kai yana kallon ta. Ta mishi alamun tambaya da ido.
"Please kada ki tashi.!
"Tayi murmushi, i'm sorry yanzu zan dawo.!!
Yaji dad`in kalmar _i'm sorry_ d`in data ce. Ya saki tattausan murmushi.
"To kije.!
Sannan ya cukune fuska kamar yaron da aka kwacewa alawa.😀
Ta mik'e tana kunshe dariyarta.
Tana juya baya ya zuba mata ido yana k'arewa tafiyar ta kallo, _cikin nutsuwa take._ yana jin dad`in hakan har ta shige kofar cikin gidan.
Ita da mufida suka dawo, ta rakota da try d`in lemo, ita kuma ta taho da snacks da dambun nama..
Suka mishi sallama dukkan su, ya amsa, suka ajye a kan table d`in, sai faman bin hafsah da ido yake.
Mufida ta gaida shi.
Ya amsa cikin sakin fuska sosai.
Hafsah taja kujera ta zauna, ta d'anyi kafin ta dago da niyyar mishi magana.
Karaf idanunsu suka had'u dama shi kallonta yake.
Ta dan kalleshi na seconni itama, shi ko ko kiftawa baiyi ba, hakan ya bata tsoro tayi saurin k'asa da ido ta fasa maganar.
"Itama k'anwarki ce."?
Ta d'aga gira kawai.
Yayi murmushi.
Sannan yace, Hafsah.!!
Ta tsayar da duk tunaninta kanshi amma bata ko motsa ba bare ta amsa.
Ya dace kisan ko ni waye koh."?
Ta saki murmushin jin dad`in zancen.
Ya d'ora "Tun kafin ki gaji dani."
Ta sake yin murmushin dai.
Ya jinjina kai yes, amma kafin in fad'a miki sai kin amsa min wata tambaya.
Ta kalle shi cikin ido tana sauraren shi.