Sashe 45
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
"Hafsy..Hafsy,!!
Nazeer ya kwalo-mata kira.
Har aranta bataji dad`in kiran ba, bata son abinda yake mata bare yanzu cikin yanayin da take, da ita kad'ai ce babu abinda zai hanata yin _burus_ dashi, amma kuma ga k'anwarshi gefenta dole ta amsa, ko dan gudun kada ta ji haushin hakan, tunda ance _d`an-uwa rabin-jiki."_
"Hafsah Ya Nazeer fa yana kiranki."
Fateema ta qara qarfafa mata guiwa da haka. Ala dole ta miqe, ta fita, bata da qarfin muryar da zata amsa.
Yana tsaye a parlour ta motsa baki, zatace _"Gani."_ ya tare ta.
"Haba Sisi na, kiran ma baza,a amsa min ba."?
"Banji ba ne." ta fad'a murya a dashe.
"Nidai ayi hakuri idan ni na b'ata miki rai, dama abinci za,a taimaka min dashi."
Ya fad'a yana qare mata kallo.
Abin ya bata kunya, taji kunyar kanta, ta dan saki rai sannan tace, "Ciwon kai nakeyi."
"Ayya sannu kinsha magani."?
Ta girgiza kai.
'To kije kisha bari na zuba abincin da kaina."
Ta girgiza mishi kai, bata son ya dinga karantar k'osawar da tayi da shi don haka ta wuce kitchen.
Shi kuma ganin ya sami abinda yake so sai ya wuce d`akin shi.
Ranta ya qara b'aci bata son shiga d`akinshi sam, da yaran suna nan babu abinda zai hana ta basu su kai mishi. Amma babu yadda ta iya.
A bakin kofa ta tsaya. "Ga abincin."
Ta fad'a a qasan mak`oshi.
"Kiyi hakuri ki miqo min ciki."
"Shima yayo magana da ga cikin dakin.
Ta ajye abincin ko kallonshi bata yi ba, zata juya taji yace.
"Don Allah Hafsah, ki zo kiji."
Ta juyo ta tsaya tana kallon shi.
"Ki zauna mana please."
Ta dan d`osanu a Kujera.
Ya juyo gaba-d`aya Ya fuskanto ta.
Cikin marairaice murya ya fara magana.
"Jibi zamu shiga _camp_ Hafsah, gobe zan tafi in barku."
Shuru tayi tana, nazarin zancen, mene alfanun fad'ar kalmar nan."?
Tana tsakiya da mamaki taji yace.
"Zanyi kewar ku Hafsah.!!
Binshi da kallo tayi kawai.
"Baki da waya koh."?
Ta gaji da irin salon nashi me yake nufi, a irin wannan lokacin da take cikin halin k'ila wa k'ala, akan Yusuf, zai dinga zuwa mata da wani zance ?? don haka, ta had'e rai.
Ya lura da hakan, nan ya shiga tunani,
_"Ya dace, ya bar yarinya da wannan batun don da alama hankalinta ba akanshi yake ba kuma, akwai sauran yarinta a tattare da ita."_
_Zai barta zuwa wasu lokuta yaga idan akwai rabon shi._
Ya saki ajiyar zuciya, "Okey thank you, kije ciki na gode."
Ta miqe kamar akan qaya take.
_Ya bi bayanta da kallo yana kissima abubuwa da dama, ko dai ya hakura ne kawai.?_
To, babu yadda Fateema bata yi ba, don "Hafsah ta fada mata dawa tayi waya amma fir taki fad'a.
Don haka ta rabu da ita, sai kawai tayi saving number, da Hafsan ta kira.
Daren Hafsah, cike da mafarke-mafarken Yusuf da Basma mara sa dad`in bada labari, haka ta wayi gari da alwashin sai taje inda Basma ta fad'a mata don a banbance tsaba da tsakuwa tsanin ita da ita.
Da sassafe, Nazeer ya gama shiri tsab, ya fito da jakarshi sab'e zai musu sallama, dakin Mamanshi ya fara shiga ta dad'e tana yi mishi addu,ar samun nasara da tsarin ubangiji..
"Amin mama Nagode." haka yake ta fad'a.
Suka fito shida mama zuwa palour, yaran duk suna nan dake Lahdi ce, mama ta qare musu kallo babu Hafsah aciki, "Fateema jeki kira Hafsah suyi sallama.
Yaji dad`in hakan sosai.
Tare suka dawo da Fateeman.
Ta saki fara,a kuma. "Har da cewa yaya tafiyar ce."?
Shiko abin nema ya samu, murmushi yayi mata. "Eh mun fito sai Allah ya dawo damu, kwana biyu kema ki huta da zubamini-zuba-mini."
Dariya, sukayi musu, mama nacewa, "Ah toh, ashe dai ka sani."
Har habar gidan aka fita raka shi, Hafsah taga bata da zab'i sai illa itama ta bisun. Don haka tabi bayansu.
Kallonta yake sosai, kallon da kowa yaso lura dashi. Kallon da Hafsah ta kasa fassara shi. Daga bi sa-ni ya d`auke idonshi yana da murmushi had`i da daga musu hannu bye-bye."
Yace musu. Driver yaja, suka dawo ciki anata hirar kewa.!
Kusan Yinin ranar Hafsah a d`aki tayi shi, tanata kissima abubuwa da dama a ranta.
_Tabbas sai taje ga Basma. Dole taje ta nuna mata, shuru shuru ba wasa bane, kuma dole ta nuna mata cewa tabbas tayi kafuwar da ita bazata tab'a yi ba har abada a zuciyar Yusuf._
Mama bata takura mata da tambayoyi ba yau, tun bayan da ta tambayi Fateema _"Ko akwai bayani.?_ fateema tace mata babu, amma kuma a bisa dole, ta labarta mata batun wayar da, Hafsah tayi a jiya.
"Ki dinga kaffa-kaffa da wayarki kema, sannan sai kin qara qaimi, kinsa dabara ko in koya miki dabarun."?
Fateema tayi dariya "Aa, ki bari mama, zan iya."
"Yawwa, ko kefa."?
Tun da rana mama ta zubawa duk wani motsin Hafsah ido, tana gani tayi wanka da la,asar ta shirya cikin kaya masu kyau, shirin dai yafi kama da na wanda zai fita.
Bata tanka, mata ba, amma a zuciyar ta ta kissima, _"Kada dai ace yarinyar nan wani ta jawo min gidan nan._
K'arfe 5:30pm, Hafsah nata kallon agogo, ji take kamar akan qaya take, gashi mama ta kasa ta tsare a parlour.
''Oh my God.!! Take ta fad'a a zuciyarta hira kawai ake, amma sam ba fahimta Hafsah take ba, hankalinta na can wani guri, zuciyar ta na raya mata abubuwa da dama bata so, Basma ta ce _tsoro taji_ shiyasa ta qi zuwa.
Ana hada wayar mama tayi qara, ta d'auka ta fara waya, sai kuma tayi d'akinta.
Damar da Hafsah ta samu kenan ta, wuce daki cikin hanzari Fateema na kwance ta ganta, da azama kafin tayi magana ta d`auki jakarta da mayafinta ta fice.
A parlour, sai su Al,ameen da Nour, ta kakkkalle su kawai ta fice.
Yaya Hafsah ina zaki."?
Inji Al,amin.
Abinda mama taji kamar kunnen ta ya jiyo mata take ta yanke wayar. Itako Hafsah, ai jin yaran sunyi magana tuni ta qara da gudu-gudu har ta isa gate ta bude kofa ta fice."
Fitowar mama kenan taci karo da Fateema ita ma.
Maman ta fara magana kenan tana tambayar yaran "Ku Hafsah ce ta...
Kafin ta Ida tambayar su taji fateema na cewa "Mama aiken Hafsah kikayi."?
Cikin rud'ewa mama, ta qarasa tambayar, "Nace muku Hafsah ce ta fita."?
"Har sun dan fara rud'ewa, suna in'ina, "A,eh" fita tayi, muma bamu san ina ta tafi ba."
Mama ta tafa hannaye tana salati, yarinya zata ja mata masifa, ubanta ya amince ya bata ita amma kuma tayi mata haka, du-du-du, ko sati bata cikasa a gidan ba.
Da azama mama ta figi mayafinta, fateema ta bita cike da rud'u.
Me yake faruwa da Hafsah ne, gaskiya bata san halin mamansu ba da bazata dinga, irin haka ba. Da ace ita ce, ai kashinta ya bushe..."
_Har rige-rigen fita suke ita da mama, kuma babu wanda yacewa wani uffan, to ina ma suka ga lokacin magana."??....._
📝
*HAJEEYAH KHAREEMERH*
♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(masoyin k'warai )
*Cigaban littafin Zazzafan so*
*(Guba ne)*
💔💔
*By:*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah khareemerh)*
*Dedicated to Unique in your love heart group member*
📄 *42*
Nazeer ya kwalo-mata kira.
Har aranta bataji dad`in kiran ba, bata son abinda yake mata bare yanzu cikin yanayin da take, da ita kad'ai ce babu abinda zai hanata yin _burus_ dashi, amma kuma ga k'anwarshi gefenta dole ta amsa, ko dan gudun kada ta ji haushin hakan, tunda ance _d`an-uwa rabin-jiki."_
"Hafsah Ya Nazeer fa yana kiranki."
Fateema ta qara qarfafa mata guiwa da haka. Ala dole ta miqe, ta fita, bata da qarfin muryar da zata amsa.
Yana tsaye a parlour ta motsa baki, zatace _"Gani."_ ya tare ta.
"Haba Sisi na, kiran ma baza,a amsa min ba."?
"Banji ba ne." ta fad'a murya a dashe.
"Nidai ayi hakuri idan ni na b'ata miki rai, dama abinci za,a taimaka min dashi."
Ya fad'a yana qare mata kallo.
Abin ya bata kunya, taji kunyar kanta, ta dan saki rai sannan tace, "Ciwon kai nakeyi."
"Ayya sannu kinsha magani."?
Ta girgiza kai.
'To kije kisha bari na zuba abincin da kaina."
Ta girgiza mishi kai, bata son ya dinga karantar k'osawar da tayi da shi don haka ta wuce kitchen.
Shi kuma ganin ya sami abinda yake so sai ya wuce d`akin shi.
Ranta ya qara b'aci bata son shiga d`akinshi sam, da yaran suna nan babu abinda zai hana ta basu su kai mishi. Amma babu yadda ta iya.
A bakin kofa ta tsaya. "Ga abincin."
Ta fad'a a qasan mak`oshi.
"Kiyi hakuri ki miqo min ciki."
"Shima yayo magana da ga cikin dakin.
Ta ajye abincin ko kallonshi bata yi ba, zata juya taji yace.
"Don Allah Hafsah, ki zo kiji."
Ta juyo ta tsaya tana kallon shi.
"Ki zauna mana please."
Ta dan d`osanu a Kujera.
Ya juyo gaba-d`aya Ya fuskanto ta.
Cikin marairaice murya ya fara magana.
"Jibi zamu shiga _camp_ Hafsah, gobe zan tafi in barku."
Shuru tayi tana, nazarin zancen, mene alfanun fad'ar kalmar nan."?
Tana tsakiya da mamaki taji yace.
"Zanyi kewar ku Hafsah.!!
Binshi da kallo tayi kawai.
"Baki da waya koh."?
Ta gaji da irin salon nashi me yake nufi, a irin wannan lokacin da take cikin halin k'ila wa k'ala, akan Yusuf, zai dinga zuwa mata da wani zance ?? don haka, ta had'e rai.
Ya lura da hakan, nan ya shiga tunani,
_"Ya dace, ya bar yarinya da wannan batun don da alama hankalinta ba akanshi yake ba kuma, akwai sauran yarinta a tattare da ita."_
_Zai barta zuwa wasu lokuta yaga idan akwai rabon shi._
Ya saki ajiyar zuciya, "Okey thank you, kije ciki na gode."
Ta miqe kamar akan qaya take.
_Ya bi bayanta da kallo yana kissima abubuwa da dama, ko dai ya hakura ne kawai.?_
To, babu yadda Fateema bata yi ba, don "Hafsah ta fada mata dawa tayi waya amma fir taki fad'a.
Don haka ta rabu da ita, sai kawai tayi saving number, da Hafsan ta kira.
Daren Hafsah, cike da mafarke-mafarken Yusuf da Basma mara sa dad`in bada labari, haka ta wayi gari da alwashin sai taje inda Basma ta fad'a mata don a banbance tsaba da tsakuwa tsanin ita da ita.
Da sassafe, Nazeer ya gama shiri tsab, ya fito da jakarshi sab'e zai musu sallama, dakin Mamanshi ya fara shiga ta dad'e tana yi mishi addu,ar samun nasara da tsarin ubangiji..
"Amin mama Nagode." haka yake ta fad'a.
Suka fito shida mama zuwa palour, yaran duk suna nan dake Lahdi ce, mama ta qare musu kallo babu Hafsah aciki, "Fateema jeki kira Hafsah suyi sallama.
Yaji dad`in hakan sosai.
Tare suka dawo da Fateeman.
Ta saki fara,a kuma. "Har da cewa yaya tafiyar ce."?
Shiko abin nema ya samu, murmushi yayi mata. "Eh mun fito sai Allah ya dawo damu, kwana biyu kema ki huta da zubamini-zuba-mini."
Dariya, sukayi musu, mama nacewa, "Ah toh, ashe dai ka sani."
Har habar gidan aka fita raka shi, Hafsah taga bata da zab'i sai illa itama ta bisun. Don haka tabi bayansu.
Kallonta yake sosai, kallon da kowa yaso lura dashi. Kallon da Hafsah ta kasa fassara shi. Daga bi sa-ni ya d`auke idonshi yana da murmushi had`i da daga musu hannu bye-bye."
Yace musu. Driver yaja, suka dawo ciki anata hirar kewa.!
Kusan Yinin ranar Hafsah a d`aki tayi shi, tanata kissima abubuwa da dama a ranta.
_Tabbas sai taje ga Basma. Dole taje ta nuna mata, shuru shuru ba wasa bane, kuma dole ta nuna mata cewa tabbas tayi kafuwar da ita bazata tab'a yi ba har abada a zuciyar Yusuf._
Mama bata takura mata da tambayoyi ba yau, tun bayan da ta tambayi Fateema _"Ko akwai bayani.?_ fateema tace mata babu, amma kuma a bisa dole, ta labarta mata batun wayar da, Hafsah tayi a jiya.
"Ki dinga kaffa-kaffa da wayarki kema, sannan sai kin qara qaimi, kinsa dabara ko in koya miki dabarun."?
Fateema tayi dariya "Aa, ki bari mama, zan iya."
"Yawwa, ko kefa."?
Tun da rana mama ta zubawa duk wani motsin Hafsah ido, tana gani tayi wanka da la,asar ta shirya cikin kaya masu kyau, shirin dai yafi kama da na wanda zai fita.
Bata tanka, mata ba, amma a zuciyar ta ta kissima, _"Kada dai ace yarinyar nan wani ta jawo min gidan nan._
K'arfe 5:30pm, Hafsah nata kallon agogo, ji take kamar akan qaya take, gashi mama ta kasa ta tsare a parlour.
''Oh my God.!! Take ta fad'a a zuciyarta hira kawai ake, amma sam ba fahimta Hafsah take ba, hankalinta na can wani guri, zuciyar ta na raya mata abubuwa da dama bata so, Basma ta ce _tsoro taji_ shiyasa ta qi zuwa.
Ana hada wayar mama tayi qara, ta d'auka ta fara waya, sai kuma tayi d'akinta.
Damar da Hafsah ta samu kenan ta, wuce daki cikin hanzari Fateema na kwance ta ganta, da azama kafin tayi magana ta d`auki jakarta da mayafinta ta fice.
A parlour, sai su Al,ameen da Nour, ta kakkkalle su kawai ta fice.
Yaya Hafsah ina zaki."?
Inji Al,amin.
Abinda mama taji kamar kunnen ta ya jiyo mata take ta yanke wayar. Itako Hafsah, ai jin yaran sunyi magana tuni ta qara da gudu-gudu har ta isa gate ta bude kofa ta fice."
Fitowar mama kenan taci karo da Fateema ita ma.
Maman ta fara magana kenan tana tambayar yaran "Ku Hafsah ce ta...
Kafin ta Ida tambayar su taji fateema na cewa "Mama aiken Hafsah kikayi."?
Cikin rud'ewa mama, ta qarasa tambayar, "Nace muku Hafsah ce ta fita."?
"Har sun dan fara rud'ewa, suna in'ina, "A,eh" fita tayi, muma bamu san ina ta tafi ba."
Mama ta tafa hannaye tana salati, yarinya zata ja mata masifa, ubanta ya amince ya bata ita amma kuma tayi mata haka, du-du-du, ko sati bata cikasa a gidan ba.
Da azama mama ta figi mayafinta, fateema ta bita cike da rud'u.
Me yake faruwa da Hafsah ne, gaskiya bata san halin mamansu ba da bazata dinga, irin haka ba. Da ace ita ce, ai kashinta ya bushe..."
_Har rige-rigen fita suke ita da mama, kuma babu wanda yacewa wani uffan, to ina ma suka ga lokacin magana."??....._
📝
*HAJEEYAH KHAREEMERH*
♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(masoyin k'warai )
*Cigaban littafin Zazzafan so*
*(Guba ne)*
💔💔
*By:*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah khareemerh)*
*Dedicated to Unique in your love heart group member*
📄 *42*