Sashe 75
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Am Eh Abba dama naga wani yazo wajen aunty Hafsah ne yau kuma naga kamar tana sauraren shi itama."
Abba yayi murmushi.
"Nasan zancen, na gamu dashi kuma har nace ya turo iyayenshi ma."
Bashir ya d'ago da sauri yana mamaki, Abba yayi murmushi.
Ba yace min yasan ka ba."?
Bashir ya labartawa Abba had'uwar su da Ukhashatu sannan ya dora da cewa, amma sun dad'e da aunty sunfi wata d'aya zasuyi biyu ma, kuma yace min zuwan shi na biyu kenan."
"To masha Allah Allah yayi jagora."
Bashir yace Amiiin, shima yaji dad`in abinda mahaifin nashi ya yanke.
____________________
Hafsah cikin tunani, barkatai da takaicin Ukhashatu ta kwanta, shiyasa tana ganin kiranshi amma ta share, takaicin ta d'aya matar daya boye mata yana dashi.
Har kwalla ta zubar, meyasa sai da ta fara sonshi sannan zaiyi mata wannan tozarcin, gaskiya maza basu da amana.
Share shin da take ya fara azabtar dashi, don haka ya shirya kalaman ban hakuri masu sanyaya zuciya da taushi ya turo mata.
_Kiyi hak'uri Queen idan nayi laifi, ni mai matuk'ar son ganin farincikinki ne, joking with you inpresses me ina son wasa dake amma wallah bani da mata bare 'ya na nuna miki k'anwata ne da 'yar yayana, am sorry dear na zabtu bzn kuma ba, kiyi picking call kiji wani abu kinji gimbiya.!!_
Sanda text d`in ya iso wayarta, da daddare ne, amma tana dubawa bazan san sanda ta saki wani dan ihu ba, da saida Zainab ta ankarar da ita _dare ne,_ sannan ta nade tabarmar kunya da hararar Zainab.
Zainab itama ta harare ta a wasa ta juya tana kus kus.
Ta jira kiranshi amma bai shigo ba, ita kuma tanajin kunyar kiranshi da kanta.
♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so*
*(Guba ne)*
💔💔
*By:*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah khareemerh)*
*Dedicated to Unique in your love heart group members.*
📄 *60*
#Not edited
*Kuyi hakuri da typing error.*
______________________________
*Farar* Safiya ce misalin k'arfe takwas na dare, gidan yayi shuru kasancewar _*Mazauna Gidan* (Haermebaererh novels_)
basa nan, Abba anyi mishi wata rasuwa ta Babban abokin sa, a daren jiya daya saka shi fitar sassafe don ya sami Jana'iza.
Ita kanta matar gidan ta fita, wani uzuri nata, yayin da sauran 'ya'yan gidan suka fita nasu harkokin. Sai su biyu da suka rage a gidan kamar idanu.
Ita kadaice a d'akin ta, jin shurun gidan ya k'aru ya tabbatar mata da cewa mutanen gidan basa nan.
Gani tayi wannan wata dama ce ta samu na gabatar da abinda take ganin maslaha ne gareta. Wanda kuma take ganin zai dakatar da abinda ake shirin yanke mata.
_Bata shirya amsar aure yanzu ba don haka bata jin zata yarda da katsalondon irin wannan._
Doguwar riga ce ajikin ta, ba tare da bata lokaci ba ta d'ora wani mayafi da taga yafi kusa da ita, kawai ta kwashi takalma a hannu cikin sand'a ta fara takowa tana waige waige kamar _barauniyar data shigo sata._
Cikin sa,a babu wanda taci karo da shi. Har zuwa kofar fita, shima a sa,a babu mai gadi a wajen, da Alama ya zagaya wani wajen.
Da gudu ta k'arasa ficewa sai lokacin taji ta sami sukunin watsar da takalman hannunta a k'asa sannan ta saka, jikin ta na rawa ta fara tafiya.
Cikin layin ta hango napep ta tsare amma ya girgiza kai alamun Aa, cikin k'osawa ta kara sauri tana mita, a zuci..
Ta d'anyi yar tafiya kafin ta hango wani, kamar ta kifa take tsayar dashi.. Aikuwa ya tsaya.
Ta kara sauri sannan ta afka ciki cike da jindadi, har da ajiyar zuciya.
Sannan ta sami sukunin sanar da shi inda zai kaita.
Tarauni zaka kaini.!!
Me Napep ya juyo ya kalleta, sanye yake cikin wata riga wacce ta dan dame shi, mara hannu, (sleeveless) blue color, sai farin wandon jeans iya gwiwa, (three-quater). Kanshi ya tara gashi. Yafi kama da matasa wadanda ake kira _'yan swagger._
Ta yatsina fuska ganin ya k'ura mata ido har da daga gira.
"Okey, yanmata."
Yace da ita, sannan ya juya ga tuk'insa.
Ta kuma yatsina ffuska, da takaicin kiranta da yanmata da yayi, sai kuma taji fargaba tuno cewa bata sami damar dakko kudi ba bare _purse._
Me Napep gudu dinga yi da ita, yanayi yana bin wakar daya kunna musu.
Da sauri suna isa, unguwar sannan tayi mishi nuni daya kaita cikin wani layi, babu musu ya kaita har k'ofar gida.
Sannan ta bude baki, cikin yauki' saboda taga ta dawo cikin nutsuwarta tace, "Am na manta kudi na a gida, so zan dan shiga ciki na amso maka kud'in."
Ya bita da kallo kafin ya jinjina kai babu magana.
Ta juya ta shiga gidan, shiko ya bita da kallo.
Kai tsaye dakin maman ta nufa, tana kala mata kira, Mama!! Mama!! Maman ta yi saurin fitowa suna had'u a palour, da sauri cikin faraa, ta rungumeta "Yawwa my daughter.!!
Cikin jin dadi itama ta k'ara rungume matar kafin tayi saurin sakinta tace, "Oh mum nabar Napep a waje so bani 500 na bashi."
Okey, inji matar, ta duba gefenta kan kujera, ta dauki Jakarta ta dakko ta bata. Da sauri ta fita, ta tarar da shi ta mik'a mishi, ya amsa yana lalubo chanji, yaga tana kokarin juyawa, "Wallahi kin burgeni fah."
Ta zaro ido lokaci guda tare da jan tsaki. Sannan ta juya da sauri, tana fad'in Nonsense.!!
Ta dawo cikin gida, abinda ya kawo ta ya fi karfin ta tsaya tuna abinda mai Napep din yayi mata.
Tana zama maman ta tare ta da tambaya.
Ya akayi kika fito."?
Sun fita ne duka, anyiwa Abba rasuwa.
Okey good.
Sannan ta saita murya itama ta yar ta bata hankali.
"Shawara daya na yanke wacce nake ganin itace matakin k'arshe.!!
Indai mukayi haka to dole a fasa auren nan, kuma zamu aiwatar da komai ne a yau, don bamu da wani lokacin daya dace idan ba yau ba."
'Yar ta jinjina kai, maman ta d'ora, "Ai kinsan gidansu koh."?
Ta jinjina kai.
Eh, ya taba kwatantamin.
"Can zamuje.!!
Ta fada kai tsaye.
Yar ta zaro ido, uwar ma ta kafe ta da nata idanuna, tare da nuna ta da yatsa.
_matukar baki yadda mun dauki wannan matakin ba, to sai dai ki zauna ki aure shi kuma kada ki sake, mini complain akan bakya sonshi._
Ta dire zancen cikin daga murya tace, ko kin fara sonshi ne, kin yadda zaki aure shi."?
Tayi saurin girgiza kai.
Uwar ta mike tare da sab'ar jakarta, sannan ta mik'o mata hannu.
"Taso muje."
Babu musu ta mike ta bita, suka shiga motar uwar suka dauki hanya.
Jikin yar duk a sanyaye ko menene dalili oho.
Lura da hakan da uwar tayi yasa ta shiga yi mata wasu jawabai.
_ina raye bazan zuba ido ayi miki auren dole ba, tunda shi ya rantse bazai janye kudurinsa ba, ni ina da yadda zanyi.
Idan su gidan su yaron suka ce basayi ko shi yaron su ai ba zai musu dole ba koh."?
Ki kwantar da hankalin ki, ayau zuwa gobe zakiji batun auren ki babu shi kinga sai ki auri duk wanda kike so koh."?
Sukayi murmushi a tare, sannan sukayi shuru kowa da nashi tunanin.
Sub iso unguwar, sai da suka had'a da tambaya sannan aka nuna musu gidan.
_"Babban gida kalar gidan manyan mutane.",_
Matar wacce zatayi kimanin shekaru Hamsin
ko da d'oriya, na zaune a palournta, tayi shuru a zuciyarta tana lissafin wani abu.
Wato batun auren babban d'anta dake k'aratowa.
Ita ba tunanin hidindumu ne ya dame ta ba, Aa sai dai wani rad'e-rad'i daya ke ta isowa ga kunnenta a kullum, Wato _wai kalar yarinyar da d'anta ya dakko._
Bataji wanda ya yabi yarinyar ba sam, Sai dai kushe, amma ta daure abun, tunda ta tambayi mijinta kuma ya bata yak'inin tabbas mahaifin yarinyar mutuminki kirki ne kuma ya bawa 'ya'yanshi tarbiyya. Don haka ta yanke wani hukunci cikin tunanin da take na, _zata tuntubi dan nata sannan zata sa itama ayi mata binciken sirri._
Tunda indai kaji anfiya batu kan abu guda toh akwai magana.
Tana tunanin ne ta sami sakon cewa, wai tayi bak'i, abinda, ta fara yi shine duba agogo.
K'arfe 11:00am, don haka sai tayi tambaya "Su wane"?
Dan aiken yace, Hajiya dana tambaye su cewa sukayi, su ba baki bane, surukaine don haka in barsu su shigo.
Kamar zata sake magana sai kuma k'aguwa ( _eager_ ) taga su waye, yasa tayi saurin cewa shigo dasu kawai.
Suka shigo da sallama kamar, gaske, hajiya ta dago ido tana kallonsu da murnushi.
Duk abinda Hajiya Halima ta had'iyo sai taji tana shayin matar kuma tayi mata kwarjini, _mutum a gidansa kenan_
Sukayi shuru, bayan ta basu gurin zama, tare da musu tarbar da murmushi had'e da musu _sannu da zuwa._
Itama cikin son tuno ko ta sansu yasa take ta bin karamar da kallo, don ita tafi yi mata kama da _idon, sani._
Ta gaji da hasashen da kuma shurun da bak'in sukayi tace, cikin murmushi, _"Naso na shaidaku kuma na kasa, ko zaku min bayani."?_
Sai lokacin bakin Hajiya Halima ya bude, ta sami kwarin gwiwar yin abinda take ganin shiya dace, kuma zai jawo fasuwar al, amran."
Yes babu lallai ki sanmu, especially ma ni..
Hajiya ta zubo musu ido, don taji maganar kamar babu _salama_ cikin ta.
Kafin tace wani abu hajiya Halima ta nuna 'yarta,
Wannan 'yata ce Basma, itace danki yake shirin aure, to shine nazo na sanar muku gaskiya, _ni da ita bama son auren nan ubanta ne ke shirin kullawa,_ kinga kuwa gwara a hak'ura kada anayin batacciya don yata ba so take ba.
Ta kalli Basma, "Basma ko kina so."?
Duk rashin kunyar Basma sai taji tana shayin matar itama, kuma tayi mata wani irin kwarjini, amma don kada ta kunyata uwarta sai ta girgiza kai.
Hajiya Halima cike da k'warin guiwa ta dora, to kinji dai daga bakinta, yarinya bata so don, haka sai azan abinyi gaskiya, idan da zaki tambayi yaron ma, shi kanshi yasan...
Hajiya Rabi , bata bar Hajiya Halima ta k'arasa, zancen ta ba, ta daga mata hannu, sannan ta kafe ta da ido, da yanayin fuskarta da ta ke ta sauya zuwa kalar matsanancin fushi.
Abba yayi murmushi.
"Nasan zancen, na gamu dashi kuma har nace ya turo iyayenshi ma."
Bashir ya d'ago da sauri yana mamaki, Abba yayi murmushi.
Ba yace min yasan ka ba."?
Bashir ya labartawa Abba had'uwar su da Ukhashatu sannan ya dora da cewa, amma sun dad'e da aunty sunfi wata d'aya zasuyi biyu ma, kuma yace min zuwan shi na biyu kenan."
"To masha Allah Allah yayi jagora."
Bashir yace Amiiin, shima yaji dad`in abinda mahaifin nashi ya yanke.
____________________
Hafsah cikin tunani, barkatai da takaicin Ukhashatu ta kwanta, shiyasa tana ganin kiranshi amma ta share, takaicin ta d'aya matar daya boye mata yana dashi.
Har kwalla ta zubar, meyasa sai da ta fara sonshi sannan zaiyi mata wannan tozarcin, gaskiya maza basu da amana.
Share shin da take ya fara azabtar dashi, don haka ya shirya kalaman ban hakuri masu sanyaya zuciya da taushi ya turo mata.
_Kiyi hak'uri Queen idan nayi laifi, ni mai matuk'ar son ganin farincikinki ne, joking with you inpresses me ina son wasa dake amma wallah bani da mata bare 'ya na nuna miki k'anwata ne da 'yar yayana, am sorry dear na zabtu bzn kuma ba, kiyi picking call kiji wani abu kinji gimbiya.!!_
Sanda text d`in ya iso wayarta, da daddare ne, amma tana dubawa bazan san sanda ta saki wani dan ihu ba, da saida Zainab ta ankarar da ita _dare ne,_ sannan ta nade tabarmar kunya da hararar Zainab.
Zainab itama ta harare ta a wasa ta juya tana kus kus.
Ta jira kiranshi amma bai shigo ba, ita kuma tanajin kunyar kiranshi da kanta.
♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so*
*(Guba ne)*
💔💔
*By:*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah khareemerh)*
*Dedicated to Unique in your love heart group members.*
📄 *60*
#Not edited
*Kuyi hakuri da typing error.*
______________________________
*Farar* Safiya ce misalin k'arfe takwas na dare, gidan yayi shuru kasancewar _*Mazauna Gidan* (Haermebaererh novels_)
basa nan, Abba anyi mishi wata rasuwa ta Babban abokin sa, a daren jiya daya saka shi fitar sassafe don ya sami Jana'iza.
Ita kanta matar gidan ta fita, wani uzuri nata, yayin da sauran 'ya'yan gidan suka fita nasu harkokin. Sai su biyu da suka rage a gidan kamar idanu.
Ita kadaice a d'akin ta, jin shurun gidan ya k'aru ya tabbatar mata da cewa mutanen gidan basa nan.
Gani tayi wannan wata dama ce ta samu na gabatar da abinda take ganin maslaha ne gareta. Wanda kuma take ganin zai dakatar da abinda ake shirin yanke mata.
_Bata shirya amsar aure yanzu ba don haka bata jin zata yarda da katsalondon irin wannan._
Doguwar riga ce ajikin ta, ba tare da bata lokaci ba ta d'ora wani mayafi da taga yafi kusa da ita, kawai ta kwashi takalma a hannu cikin sand'a ta fara takowa tana waige waige kamar _barauniyar data shigo sata._
Cikin sa,a babu wanda taci karo da shi. Har zuwa kofar fita, shima a sa,a babu mai gadi a wajen, da Alama ya zagaya wani wajen.
Da gudu ta k'arasa ficewa sai lokacin taji ta sami sukunin watsar da takalman hannunta a k'asa sannan ta saka, jikin ta na rawa ta fara tafiya.
Cikin layin ta hango napep ta tsare amma ya girgiza kai alamun Aa, cikin k'osawa ta kara sauri tana mita, a zuci..
Ta d'anyi yar tafiya kafin ta hango wani, kamar ta kifa take tsayar dashi.. Aikuwa ya tsaya.
Ta kara sauri sannan ta afka ciki cike da jindadi, har da ajiyar zuciya.
Sannan ta sami sukunin sanar da shi inda zai kaita.
Tarauni zaka kaini.!!
Me Napep ya juyo ya kalleta, sanye yake cikin wata riga wacce ta dan dame shi, mara hannu, (sleeveless) blue color, sai farin wandon jeans iya gwiwa, (three-quater). Kanshi ya tara gashi. Yafi kama da matasa wadanda ake kira _'yan swagger._
Ta yatsina fuska ganin ya k'ura mata ido har da daga gira.
"Okey, yanmata."
Yace da ita, sannan ya juya ga tuk'insa.
Ta kuma yatsina ffuska, da takaicin kiranta da yanmata da yayi, sai kuma taji fargaba tuno cewa bata sami damar dakko kudi ba bare _purse._
Me Napep gudu dinga yi da ita, yanayi yana bin wakar daya kunna musu.
Da sauri suna isa, unguwar sannan tayi mishi nuni daya kaita cikin wani layi, babu musu ya kaita har k'ofar gida.
Sannan ta bude baki, cikin yauki' saboda taga ta dawo cikin nutsuwarta tace, "Am na manta kudi na a gida, so zan dan shiga ciki na amso maka kud'in."
Ya bita da kallo kafin ya jinjina kai babu magana.
Ta juya ta shiga gidan, shiko ya bita da kallo.
Kai tsaye dakin maman ta nufa, tana kala mata kira, Mama!! Mama!! Maman ta yi saurin fitowa suna had'u a palour, da sauri cikin faraa, ta rungumeta "Yawwa my daughter.!!
Cikin jin dadi itama ta k'ara rungume matar kafin tayi saurin sakinta tace, "Oh mum nabar Napep a waje so bani 500 na bashi."
Okey, inji matar, ta duba gefenta kan kujera, ta dauki Jakarta ta dakko ta bata. Da sauri ta fita, ta tarar da shi ta mik'a mishi, ya amsa yana lalubo chanji, yaga tana kokarin juyawa, "Wallahi kin burgeni fah."
Ta zaro ido lokaci guda tare da jan tsaki. Sannan ta juya da sauri, tana fad'in Nonsense.!!
Ta dawo cikin gida, abinda ya kawo ta ya fi karfin ta tsaya tuna abinda mai Napep din yayi mata.
Tana zama maman ta tare ta da tambaya.
Ya akayi kika fito."?
Sun fita ne duka, anyiwa Abba rasuwa.
Okey good.
Sannan ta saita murya itama ta yar ta bata hankali.
"Shawara daya na yanke wacce nake ganin itace matakin k'arshe.!!
Indai mukayi haka to dole a fasa auren nan, kuma zamu aiwatar da komai ne a yau, don bamu da wani lokacin daya dace idan ba yau ba."
'Yar ta jinjina kai, maman ta d'ora, "Ai kinsan gidansu koh."?
Ta jinjina kai.
Eh, ya taba kwatantamin.
"Can zamuje.!!
Ta fada kai tsaye.
Yar ta zaro ido, uwar ma ta kafe ta da nata idanuna, tare da nuna ta da yatsa.
_matukar baki yadda mun dauki wannan matakin ba, to sai dai ki zauna ki aure shi kuma kada ki sake, mini complain akan bakya sonshi._
Ta dire zancen cikin daga murya tace, ko kin fara sonshi ne, kin yadda zaki aure shi."?
Tayi saurin girgiza kai.
Uwar ta mike tare da sab'ar jakarta, sannan ta mik'o mata hannu.
"Taso muje."
Babu musu ta mike ta bita, suka shiga motar uwar suka dauki hanya.
Jikin yar duk a sanyaye ko menene dalili oho.
Lura da hakan da uwar tayi yasa ta shiga yi mata wasu jawabai.
_ina raye bazan zuba ido ayi miki auren dole ba, tunda shi ya rantse bazai janye kudurinsa ba, ni ina da yadda zanyi.
Idan su gidan su yaron suka ce basayi ko shi yaron su ai ba zai musu dole ba koh."?
Ki kwantar da hankalin ki, ayau zuwa gobe zakiji batun auren ki babu shi kinga sai ki auri duk wanda kike so koh."?
Sukayi murmushi a tare, sannan sukayi shuru kowa da nashi tunanin.
Sub iso unguwar, sai da suka had'a da tambaya sannan aka nuna musu gidan.
_"Babban gida kalar gidan manyan mutane.",_
Matar wacce zatayi kimanin shekaru Hamsin
ko da d'oriya, na zaune a palournta, tayi shuru a zuciyarta tana lissafin wani abu.
Wato batun auren babban d'anta dake k'aratowa.
Ita ba tunanin hidindumu ne ya dame ta ba, Aa sai dai wani rad'e-rad'i daya ke ta isowa ga kunnenta a kullum, Wato _wai kalar yarinyar da d'anta ya dakko._
Bataji wanda ya yabi yarinyar ba sam, Sai dai kushe, amma ta daure abun, tunda ta tambayi mijinta kuma ya bata yak'inin tabbas mahaifin yarinyar mutuminki kirki ne kuma ya bawa 'ya'yanshi tarbiyya. Don haka ta yanke wani hukunci cikin tunanin da take na, _zata tuntubi dan nata sannan zata sa itama ayi mata binciken sirri._
Tunda indai kaji anfiya batu kan abu guda toh akwai magana.
Tana tunanin ne ta sami sakon cewa, wai tayi bak'i, abinda, ta fara yi shine duba agogo.
K'arfe 11:00am, don haka sai tayi tambaya "Su wane"?
Dan aiken yace, Hajiya dana tambaye su cewa sukayi, su ba baki bane, surukaine don haka in barsu su shigo.
Kamar zata sake magana sai kuma k'aguwa ( _eager_ ) taga su waye, yasa tayi saurin cewa shigo dasu kawai.
Suka shigo da sallama kamar, gaske, hajiya ta dago ido tana kallonsu da murnushi.
Duk abinda Hajiya Halima ta had'iyo sai taji tana shayin matar kuma tayi mata kwarjini, _mutum a gidansa kenan_
Sukayi shuru, bayan ta basu gurin zama, tare da musu tarbar da murmushi had'e da musu _sannu da zuwa._
Itama cikin son tuno ko ta sansu yasa take ta bin karamar da kallo, don ita tafi yi mata kama da _idon, sani._
Ta gaji da hasashen da kuma shurun da bak'in sukayi tace, cikin murmushi, _"Naso na shaidaku kuma na kasa, ko zaku min bayani."?_
Sai lokacin bakin Hajiya Halima ya bude, ta sami kwarin gwiwar yin abinda take ganin shiya dace, kuma zai jawo fasuwar al, amran."
Yes babu lallai ki sanmu, especially ma ni..
Hajiya ta zubo musu ido, don taji maganar kamar babu _salama_ cikin ta.
Kafin tace wani abu hajiya Halima ta nuna 'yarta,
Wannan 'yata ce Basma, itace danki yake shirin aure, to shine nazo na sanar muku gaskiya, _ni da ita bama son auren nan ubanta ne ke shirin kullawa,_ kinga kuwa gwara a hak'ura kada anayin batacciya don yata ba so take ba.
Ta kalli Basma, "Basma ko kina so."?
Duk rashin kunyar Basma sai taji tana shayin matar itama, kuma tayi mata wani irin kwarjini, amma don kada ta kunyata uwarta sai ta girgiza kai.
Hajiya Halima cike da k'warin guiwa ta dora, to kinji dai daga bakinta, yarinya bata so don, haka sai azan abinyi gaskiya, idan da zaki tambayi yaron ma, shi kanshi yasan...
Hajiya Rabi , bata bar Hajiya Halima ta k'arasa, zancen ta ba, ta daga mata hannu, sannan ta kafe ta da ido, da yanayin fuskarta da ta ke ta sauya zuwa kalar matsanancin fushi.