← Book details Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 71 OF 88

Sashe 71

Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tana fitowa palourn kai tsaye hanyar kitchen tayi. Basheer ya bita da kallon Takaici, ta zubo mata snacks da dambun nama da basa rabo dashi a, ta had'o da lemo da ruwa. Sai da tazo zata wuce su Bashir yayi mata magana murya a dak'ile.
"Yaya.!
Bata amsa ba ta juyo.
"Yanzu sai da kika gayyato wannan gidannan koh..."?

Jin abinda yake fitowa daga bakin shi ya sata yin gaba, don bata son ma ta saurare shi.

Basheer ya cije leb'e don matuk'a ta bata mishi rai, ya zabura zai mik'e ya bi bayanta amma mama ta hana shi.

Ta daga mishi hannu, "Bari Basheer kada ka bita."

Ranshi ya k'ara b'aci ya zauna shuru ya jingina sosai jikin kujera, bai fi minti d'aya ba, ya mik'e yayi waje mama ta bishi da kallo.

Niyyar ficewa yayi daga gidan gaba d'aya don haka ya nufi hanyar waje kai tsaye.

Yana bud'e k'ofar gate d`in wani Napep na tsayawa a k'ofar gidan nasu.
Bashir na k'arasa fita yaga kamar ana d'ago mishi hannu ta ciki. Don haka ya dan dakata har mutumin ya fito, me Napep yayi gaba, shi kuma mutumin ya nufo wajen Basheer.

Basheer yaso gane shi, sannan yana mamakin irin murmushin da yake mishi.

Yana k'arasowa ya k'ara fad'ad'a murmushinshi, sannan ya mik'wa Basheer hannu suka gaisa.

Cikin fara,a yace mishi, Allah ya sake had'amu koh."?
Basheer yayi murmushi tana kallon shi da mamaki.

Kafin yace, "Ai ni sai yanzu na gano ka."
Shima murmushin ya mayar mishi.

Bashir dai kallonshi yake da buk'atar k'arin bayani, kuma yaga kamar bai da niyyar k'ara cewa komai. Don haka yayi gajen hakuri yace. "Ka kira number ta baka samu ba koh."?
"Hmm, kai dai bari nasha wahala fah,
Ya dafa kafad'ar Basheer, yana murmushi, "Ka wahalar dani abokina, meya faru ne."? Cewar Ukhasha.

Bashir ya taya shi murmushin,
"Wallah a ranar aka d`auke min waya."
Ayya Allah ya kikaye gaba. Ukhasha ya fad'a cike da alhini.

"Amiin inji Bashir, sannan cikin son tabbatar wa yace, "Naga kamar nan gidan kazo koh."?

Ukhashatu yayi murmushi mai sauti, sannan yace, "Eh."
"Nan na zo."!!
Bashir ya mishi kallon mamaki kafin yace, "Gurin abbanmu,? kar dai ka sanshi dama."
Ukhasha yayi 'yar dariya, sannan yace, kai tsaye, "A,a gurin Hafsah nazo.!!

Bashir najin haka ya fad'ad'a murmushi sannan ya mishi nuni, "Aa shigo, zo mu shiga ciki don inason k'arin bayani.

Sukayi dariya dukkansu, sannan yabi Bashir suka samu kujeru suka zauna, Bashir ya bude baki zaiyi magana Ukhasha ya dakatar dashi.

"Eh dama na santa, na ganta wajen bikin aboki na, so ta hanyar shi na sami contact d'inta a wajen matarshi, bayan na kasa samunka a waya."

Tare suka sheke da dariya, don yanayin amsar tashi ya baiwa Basheer dariya.
"Ai nasan abinda zaka tambaya kenan a ina na santa koh."?
Cewar Ukhasha.
Basheer ya jinjina kai "Yes.!

Basheer nason yi mishi k'arin tambayoyi amma baya son ya dameshi.

Da kanshi ya kuma cewa, "Ai nazo wajenta fiye da sati d'aya daya wuce, kawai dai bamu had'u da kai bane."

Bashir yace, "Hakane, sai yau Allah yayi.

Sosai Basheer yake yi mishi wata fara,a ta musamman domin har cikin ranshi murna yake kuma yana godiya ga Allah da Hafsah ta samu Ukhasha a matsayin mai sonta, don komai ya had'a, kudi, kyau, ga ilimi.

Bari naje na kira maka ita koh."?
Inji Bashir.

Ukhasha yayi murmushi, "Nagode dama na kira number ta tun kafin na sauka ba,ayi picking ba.

Bashir yayi shuru yadai mik'e, amma a zuciyar shi yana cewa, _"Ya zaayi tayi picking tana tare da wannan banzar kawar tata.?_

Ya nufi ciki Ukhasha ya bishi da kallo, gaba-d`aya yaron yayi mishi kuma yaji ya k'ara samun nutsuwa da Hafsah dama gidansu da komai nata..

Allah-Allah yake kawai ta fito ya k'ara ganinta yaji sanyi a ranshi, don tunda ta tabbatar mishi ta amshi soyayyarshi, yake jin wani irin abu na musamman game da ita fiye da na da..

________________________
A cikin gidan kuwa, komawar Hafsah d'akin kenan ta ajyewa Jamila kayan data kawo mata tana murmushi take ce mata, "Ga ruwa fah."
Jamila tayi murmushi, ta k'ara bin Hafsah da kallon da take ta bin ta dashi tun zuwanta gidan.

"Thank you! tace mata, sannan ta d'ora "Nayi missing dambun nama nan naku da snacks d'innan."
Jamila mamaki ta bawa Hafsah, amma sai tayi, murmushin yak'e kawai tanajin ciwon abin cikin zuciyarta.

"An kira wayarki fah." Jamila ta fad'a sanda ta debo dambun nama zataci.

Hafsah ta d`auki wayar tana dubawa,
sai taga sunan Ukhasha, ta tsaya jimm, da zata bi kiran amma sai ta fasa. Don tana da yak'inin zai sake kira kuma bata son katse hirar su, kuma bata son tayi waya dashi a gaban Jamila.

"Kinsan da agidanmu aka bani abubuwan nan bazan ci ba.."? Ta dan tsaya, Hafsah kuma ta zubo mata ido.
"Nan ma don na mugun yarda da ke neh."!!

Inji Jamila tana wani irin murmushi.

Lamarin daya bawa Hafsah matuk'ar mamaki ta kalli Jamila da neman k'arin bayani.

Jamila ta jinjina kai. "Yes, ba komai ake bani a ko'ina nake ci ba musamman ma idan nazo gidanmu, don zan iya ce miki rabona da ko da ruwan gidanmu ne za,ayi shekara biyar ko shidda."

Hafsah ta zaro ido, lamarin ya ba ta mamaki, mamakin dalilin Jamila na kin yarda da abincin gidansu. _Wannan wacce irin jaraba ce!!_
Ta fad'a a zuciyarta.
Kafin tayi magana, Jamila tace, _"Saboda zasu iya min kiranye ni kuma ban shirya komawa gidan ba.!!_

Hafsah ta dan zaro ido, abin yafi k'arfinta. Ashe duk abinda take tunani mafarki ne kawai, Jamila bata da tunanin sauyawa. Saitaji tana shakkar yi mata wasu tambayoyi da, da tayi niyyar duk randa jamilar tazo zatayi mata su. Don a ganinta Jamila Itace dai wacce ta sani a da, kuma tafi kowa sanin ta, sannan tana ganin ta isa da ita da har zata yi mata kowacce irin tambaya.

Ashe ba haka bane, tunaninta ne ita a haka, Jamila tayi nisa kuma ta riga ta chanja tsarin rayuwa.....

📝
*HAJEEEYAH KHAREEMERH*
[17/03, 2:53 p.m.] UMAIMA BASHEER: ♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so*
*(Guba ne)*
💔💔

*By:*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah khareemerh )*
*Dedicated to Unique in your love heart group members.*

*HELLO FANS KU K'ARA HAKURI DANI BISA RASHIN POSTING... IN SHA ALLAH, ZAN TAK'AITA LITTAFIN*
_BANA SAMUN LOKACIN TYPING NE SOSAI._👏🏼👏🏼

*NOT EDITED*✏️

📄 *58*

*Suka* shuru ita da Jamila na dan wani lokaci kafin Jamila ta k'ara kallon Hafsah.

"H. hameeed, naga kamar shirin fita kike yi koh."?

Hafsah ta d'anyi jimm, kafin tace, "Eh akwai wanda zan gani ne."

Jamila ta kafe ta da ido tana mata wani irin kallo, "Hmm kice an kusa mu fara shiri."

Hafsah ta d'anyi wani d'an murmushi. "Hmm Jamila kenan ina fah.."? Wannan _manager_ inda nake aiki ne, zaizo zamuyi wata magana."

Sanin Hafsah bata k'arya yasa Jamila yarda da zancenta.

Kafin daga bisani Jamila tace, "To gaskiya kiyi kwalliya a fuskar ki don naga bakiyi kwalliya ba."
You know mazaa akwai rainin hankali, musamman manyan ma,aikatan nan."

Abin ya bawa Hafsah dariya.
Yes nake fad'a miki, inji Jamila tana zuge jakarta ta dakko wata powder.

Ta mik'e tana cewa, "ungo shafa ko in shafa miki."!!

Kawai sai ta hau shafawa Hafsan. Haka kawai Hafsah taji tana d'ard'ar d`in hakan, taji tana kyankyamin Jamila ta tab'a ta amma babu yadda zatayi.

_Powder ce mai tsada Jamila ta shafa mata wacce a k'alla kud'inta zai kai 5k, ta kuwa amshi fuskar Hafsah sosai, dama ta farare ce, tunda Jamila ta zama fara sosai itama duk da dama can tana da hasken fata._

Jamila ta ajye powder a gefe, ta kwance daurin d'ankwalin kan Hafsah, bak'in gashin ta mai tsaho ya bayyana.
Jamila ta yarfe dan kwalin tana cewa, "Gashin nan dai na nan yadda na sanshi sai baki daya k'ara.!!

Hafsah tayi dariya, sosai.

Jamila kenan, kina son gashin nan, gashin da naki ma yafi shi yawa "?

"Ta fara zarga mata d'auri tana cewa, Hmm ai nawa fushi ne dashi gashi ba gaba-d`aya ya tafi ba wani yafi wani tsaho."

Ganin suna hira haka ya bawa Hafsah k'warin guiwa wajen yin tambayar data dami zuciyarta. Dama bata son had'a ido da Jamila tayi mata ne, yanzu kuwa tana mata d'auri.

"Jamila wa zaki raka Dubai please."
Hafsah ta dake murya ta tambaye ta.

Jamila tayi murmushi.
"Hmm, H hameeed kenan."

________________________________

A parlour, Basheer ne ya shigo, har yanzu mama na zaune a parlourn, ita kanta ji take bata aminta da shigewar Hafsah da Jamila d'aki ba. Tunda bata san me Jamilan zata fad'a mata ba.

Sallama Basheer kawai yayi ya nufi inda d'akin Hafsah yake.

Mama ta kira sunan shi, "Basheer."?
Ya dakata, sannan ya juyo, "Naam mama."?

"Me zaka shiga d'akin kayi."?
Ya dan shagwabe murya, Kai mama babu komai fah, Ya Hafsah ce tayi bak'o zan fad'a mata."

"Hmm, da gaske."?
Ya saki murya.
"Allah mama.!
Mama ta maimaita, Bak'o."? "Jeka fad'a mata toh.

Mama a ranta itama bata so bakon Hafsah yaga Jamila ba.

Basheer ya wuce, ya nufi k'ofar d'akin.

_____________________________

"Ai Hafsah badon kina da abinyi ba akwai labari.. Cikin muryar tausayi ta cigaba.

"Bansan ya akayi na yada ke ba, amma cikin in sha Allah idan na dawo daga tafiyar nan zanzo zamu tattauna don ke kad'ai ce zan fadawa magana ki yarda kuma ki bani Shawara tsakani da Allah."

Hafsah tayi shuru tana sauraron ta jikinta ya k'ara sanyi.

Ita har yanzu Jamila bata bata amsar abinda take son ji ba.

Sai ta ji Jamila na cewa,
"Aunty zan raka, Kinsan yanzu duk duniya bata da kamata Nima bani da ya ita sai dai akwai Matsala guda d'aya nida ita.."!!

Ji sukayi an turo k'ofar babu ko sallama.
Jamila ta juyo, Hafsah kuma ta d'ago.

Yaya."?
Kira sunanta rai a cunkushe.
Ran Hafsah ya b'aci.
Mene."?
Tace mishi.
Ita kuma Jamila ta cigaba da gyara mata d'aurin.

"To kizo kiji mana."
Inji Bashir.

Hafsah ta bude baki cikin fushi.
Bazan zo ba, Basheer ni kake disgracing koh agaban kawata koh ni kake wa haka."?

Muryata tayi rauni, "Shikenan bazan zo ba, ko ma mene bazan zo ba inyaso ka rufe ni da duka.."
Chapter 71 · 0% Book details