Sashe 56
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
___________________
Ta tsammaci kiran Jamila amma shuru, sai yau da daddare, sai ga kira, da wata number.
"Hello,
Hafsah ma tace Hello,
"Kina magana da Jamila ne."
Murna ta cika Hafsah, "Oh ya kike.?
"Lafiya lau, wannan ne number sai kiyi save."
Okey Hafsah ta fad'a.
"Bye bye."
Jamila tace, tare da katse wayar.
Hafsah bataji dad'in takaitacciyar wayar da sukayi ba, taso suyi 'yar hira, don ta gano wane mataki Jamilan ke kai."?
Amma kuma taji dad`in samun number, tayi saving d'inta da nufin gaba ita zata kira..
Ukhasha, yayi juriya, har ya bari akayi Kwanaki uku, da bikin Jabeer ( _kafin ya fara mishi zancen Hafsah_ )
Duk kwatancen da yayi mishi kuma, sam Jabeer ya kasa gano wacece..
Kuma yaga alamun Ukhasha d`in ya damu sosai.
"Wai Aboki na baka san sunanta ba neh."?
Um kai dai bari JB wallah, na fada maka har ganinsu na karayi ranar dinner d'inka, ( _Ya bashi labarin yadda abin ya faru._) ka ga amma kullum sai nayi trying number amma har yau _is switched off._
Kasan taimakon da zanyi maka."
JB ya fad'a.
"A,a"
Kaga nan da k'arshen sati zamu, d'aga (_zasu bar k'asar_) so kazo gobe kawai akwai photos da video na biki ko za,a dace.!!
Murna ta cika ukhasha, kuma fa JB ya kawo shawara.
"Wow thank you angon Aisha, gobe da asuba zaku ganni.
"Hah, kazo d`in kaga mana."
"Nagode kai dai."
"Okay UK ana tare fah."
Sukayi sallama, suka katse wayar.
Ya tashi ya nufi d'akin hajiyarshi.
Suna zaune ita da su maryam da Fadwa suna kallo.
Ya nemi guri a k'asa ya zauna, Hajiya ta kalleshi a zubo maka abinci."?
Ya daga kai alamar "eh.
Maryam jeki zubo mishi abinci.
"To Hajiya."
Sannan ta mik'e ta mik'e, ta fita.
Sai lokacin kuma ya kalli Tv, d`in, wani shiri ake gabatarwa, dama an hasko wata mata ne tana ta jawabi, sai yanzu aka hasko mai gabatar da shirin.
Gabanshi, ya fad'i, saboda bayyanar fuskar da yake ta bulahin nema.
Ya ware ido, yana kallonta, yanayinta, kamannin ta, Itace dai daya gani a zahiri.
Zata fara magana, kenan d'if TV ta d`auke da alama NEPA ne suka d`auke wuta.
Ranshi yayi bak'i ya mik`e zai fice, shi ko jira ma a kunna solar ko yaje ya kunna ma baiyi ba.
Hajiya ta kalleshi. Ina kuma zakaje."?
Ina zuwa Hajiya.
Ya fice ya nufi d'akinshi.
Number JB ya kira.
_"Ya akayi kuma."?_
"Kaii yarinyar nan zata zautani fah."
_Meya faru."?_
Wallahi a TV na ganta yanzunnan tana gabatar da program.
"Hmm, kaii UK kodai zaucewar ce ta sa take maka gizo."?
"Ka manta, ai ban zama _majnoon_ d`in ba tukuna.
Jabeer yayi dariya, "ah to naga abin naka yayi over ne, ni ka dameni ma fah.
Hmm, to ya zakayi dani, ni nace ku gayyatota bikin ku."?
"Hmm, haka kace koh."?
"Aa sorry Yayana tuba nake."
Abin ya bawa JB dariya, _"Lallai, su Mubarak su zo akwai labari._
A,a JB kada kamin haka plz ka san halinsu bazan iya dasu ba.
Shikenan toh, amma ko ban fad'a ba zasuji labari kaidai sai kazo.
Washe-gari daya je, Gidan JB, bai bata lokaci ba ya k'ara mishi jawabi, amarya na zaune na jinsu, sai da angon yayi tambayeta sannan ta magantu, _"Aysha kin gane ta._?
"Ina tunanin ko H Hamid, ko kuma Ummi nuhu, sune suke service a gidan tv."
Please ki taimaka bari naga photos d`in.
Photo album, na bikin suka miko mishi, sai da yaje kusan tsakiya kowanne photo kallon k'urilla yake mishi, ango nata zolayar shi shida amarya. Sannan da kyar yaga wani photo, ta gefe, fuskarta bata fito sosai ba, anyi, musu tana lik'i.
"Wannan ce.!!
Ya fad'a da sauri kuma da k'arfi.
ango ya karb'a ya mik'awa amaryar.
"Eh Itace.
Tare suka hada baki shida JB wajen cewa, "wacce daga ciki."?
"Hafsah H. Hamid ce."
Azuciyar shi ya maimaita sunan _Hafsah_ sunan hajiyarshi kenan fah.!!
"Duba don Allah ki taimaka min da number ta."
"Ai kasan chanjin layin nan da nayi Allah yasa akwai contact d`in."
Ta fada tana duba cikin wayar, kaf babu number aciki.
Ta dube shi itama ya dan bata tausayi wallah kaga babu.
_Innalillahi."!!_
JB ya dafa shi, kada ka damu, ai bazamu bar k'asar nan ba, sai an samar maka solution, don bazan zuba ido a zautar min da UK ba.!!
Ukhasha, yaso ya tambayi amaryar _"ko tasan gidansu ta kwatanta mishi.?_ Amma sai ya fasa, yaji nauyin hakan, kada suga kamar ya takura musu.
Abisa tilas ya hak'ura, ya dawo gida a sanyaye, don kafin ya taho ma, sai da aysha ta gwada number wata k'awarsu, don ta turo musu number amma wayar tak'i shiga..
_Sun rabu akan, ana samu JB zai turo mishi. Yayi musu godiya sosai, sannan yabar gidan.._
A takaice dai sai ranar alhamis da dare, sannan number tazo, wajen ukhasha, shima da daddare wajen k'arfe shad'aya, duk zumud'inshi, dole ya hak'ura zuwa da safe. Yayi godiya ga Allah ba adadi.
Washegari sakayau yake jin shi, cikin nishad`i da karsashi yayi shirin fita office.
Ya nufi d'akin hajiyarshi ya mata sallama, sannan ya fito. Har ya isa bakin motar shi zai sa mata _Key_ yaji an kwalo mishi kira. _Yaya Ukhasha!!_
Mahseem ce autarsu cikin uniform.
Ta Kara'so da gudu ta d'ane shi.
"Muhaseem zaki karya ni fah.
Tayi dariya. Sannan ta sake shi.
"Yaya don Allah na bika ka sauke ni a school."?
"Eh muje." Ya zagaya ya bud'e mata k'ofar ta shiga. Sannan shima ya dawo ya shiga ya zauna. Ya tada motar aka bude musu gate, suka fita.
Suna tafiya tana damunshi da hira, "Yaya, wai yau Friday koh."?
Eh, ya akayi."?
"Zaka je dani Masjid d`in abba."?
"Waya ce miki mata na zuwa masjid."?
"Our islamiyya teacher, kuma su yaya Maryam suna zuwa wataran, amma sunki suje dani."
"To zanje dake, amma ni ba masallacin Abba nayi niyyar zanje ba, amma tunda kinaso to zamuje sai ki shirya da wuri, nima zan dawo da wuri."
"Thank you, Yaya."
Tayi shuru, sannan ta kuma samun abun cewa, "Yaya wai aunty Fadwa tace wai an kusa bikinka."?
Yayi murmushi me sauti, _"Kai fadwa ta raina shi, wato abin ma har ya kai a gaban Mahseem suna gulmar shi._?
Ta katse mishi tunani "Eh Yaya."?
Ya d'aga mata kai, alamar Eh."
"To ya sunanta."?
Ahankali yace mata, "Sunan Hajiya ne da ita."
"Yehhh, yaya mu dinga ce mata hajiya itama."
"To, kiyi mana addu,a idan mukaje masallaci."
"Yaya me zance toh."
_Kice Ya Allah ka taimaki Yaya ukhasha!!._
"To yaya zanyi, dama "Abba kullum sai yace mu dinga yin addu,a."
"Yawwa, 'yar autar mama, nagode.
Yayi parking, sannan ta fito, don anzo k'ofar makarantar su.
"Yaya adawo lafiya, zan shirya da wuri.
Ya daga mata hannu. Yana gani ta hango wasu k'awayenta ta tafi da gudu wajensu, sai ta bashi dariya ma.
Sanda ya dawo har Mahseem ta gama shiryawa, lokacin, shikuma, yana d'akinshi ya gama shafa mai, tazo bakin k'ofa ta tsaya.
Yana jiyo, hayaniyar su Zainab daga cikin gida, suna tsokanarta, _"Inyeh yau za,a masallacin Abbah!!_
"Salamu alaikum. Tayi sallama daga waje, yayo mata magana daga ciki, don bazai bata izinin shigowa ba, "Mahseem ki jirani kinji, kije d'akin Hajiya."
Ta koma ciki shi kuma, ya cigaba da shi shirin shi, cikin nutsuwa, gefen zuciyarshi da tunanin Hafsah, so yake sai ya dawo daga masallacin sannan ya gwada kira. Yana so ne sai yayi addu,a sosai ya nemi d'aukin Allah da alkhairansa cikin abin.
Yayi kyau cikin farar shaddar shi, da bak'ar hula, bakin takalmi, da kuma agogo.
Ya nufi d'akin hajiyar, shi kanshi daya ga Mahseem sai da dariya tazo mishi, taci hijabi har k'asa, ga tasbaha a hanunta.
hajiyar bata nan ma. Tana ganinshi ta taso da gudu ta rik'e hannunshi.
Shima ya kama nata, idon Fadwa akansu, zatayi magana irin ta zolayar data saba ya kafe ta da ido. "
Zoki mana photo, sai kiji dad`in kallon mu sosai."
"Kai Yaya ni baku nake kallo ba.!
Ta matso ta amshi wayar, tayi musu, sannan ta mik'a mishi kayarshi.
_Ya karb'a sannan yaja hannun Mahseem, suka fita, tana mishi hira.._
📝
*HAJEEYAH KHAREEMERH*
Ta tsammaci kiran Jamila amma shuru, sai yau da daddare, sai ga kira, da wata number.
"Hello,
Hafsah ma tace Hello,
"Kina magana da Jamila ne."
Murna ta cika Hafsah, "Oh ya kike.?
"Lafiya lau, wannan ne number sai kiyi save."
Okey Hafsah ta fad'a.
"Bye bye."
Jamila tace, tare da katse wayar.
Hafsah bataji dad'in takaitacciyar wayar da sukayi ba, taso suyi 'yar hira, don ta gano wane mataki Jamilan ke kai."?
Amma kuma taji dad`in samun number, tayi saving d'inta da nufin gaba ita zata kira..
Ukhasha, yayi juriya, har ya bari akayi Kwanaki uku, da bikin Jabeer ( _kafin ya fara mishi zancen Hafsah_ )
Duk kwatancen da yayi mishi kuma, sam Jabeer ya kasa gano wacece..
Kuma yaga alamun Ukhasha d`in ya damu sosai.
"Wai Aboki na baka san sunanta ba neh."?
Um kai dai bari JB wallah, na fada maka har ganinsu na karayi ranar dinner d'inka, ( _Ya bashi labarin yadda abin ya faru._) ka ga amma kullum sai nayi trying number amma har yau _is switched off._
Kasan taimakon da zanyi maka."
JB ya fad'a.
"A,a"
Kaga nan da k'arshen sati zamu, d'aga (_zasu bar k'asar_) so kazo gobe kawai akwai photos da video na biki ko za,a dace.!!
Murna ta cika ukhasha, kuma fa JB ya kawo shawara.
"Wow thank you angon Aisha, gobe da asuba zaku ganni.
"Hah, kazo d`in kaga mana."
"Nagode kai dai."
"Okay UK ana tare fah."
Sukayi sallama, suka katse wayar.
Ya tashi ya nufi d'akin hajiyarshi.
Suna zaune ita da su maryam da Fadwa suna kallo.
Ya nemi guri a k'asa ya zauna, Hajiya ta kalleshi a zubo maka abinci."?
Ya daga kai alamar "eh.
Maryam jeki zubo mishi abinci.
"To Hajiya."
Sannan ta mik'e ta mik'e, ta fita.
Sai lokacin kuma ya kalli Tv, d`in, wani shiri ake gabatarwa, dama an hasko wata mata ne tana ta jawabi, sai yanzu aka hasko mai gabatar da shirin.
Gabanshi, ya fad'i, saboda bayyanar fuskar da yake ta bulahin nema.
Ya ware ido, yana kallonta, yanayinta, kamannin ta, Itace dai daya gani a zahiri.
Zata fara magana, kenan d'if TV ta d`auke da alama NEPA ne suka d`auke wuta.
Ranshi yayi bak'i ya mik`e zai fice, shi ko jira ma a kunna solar ko yaje ya kunna ma baiyi ba.
Hajiya ta kalleshi. Ina kuma zakaje."?
Ina zuwa Hajiya.
Ya fice ya nufi d'akinshi.
Number JB ya kira.
_"Ya akayi kuma."?_
"Kaii yarinyar nan zata zautani fah."
_Meya faru."?_
Wallahi a TV na ganta yanzunnan tana gabatar da program.
"Hmm, kaii UK kodai zaucewar ce ta sa take maka gizo."?
"Ka manta, ai ban zama _majnoon_ d`in ba tukuna.
Jabeer yayi dariya, "ah to naga abin naka yayi over ne, ni ka dameni ma fah.
Hmm, to ya zakayi dani, ni nace ku gayyatota bikin ku."?
"Hmm, haka kace koh."?
"Aa sorry Yayana tuba nake."
Abin ya bawa JB dariya, _"Lallai, su Mubarak su zo akwai labari._
A,a JB kada kamin haka plz ka san halinsu bazan iya dasu ba.
Shikenan toh, amma ko ban fad'a ba zasuji labari kaidai sai kazo.
Washe-gari daya je, Gidan JB, bai bata lokaci ba ya k'ara mishi jawabi, amarya na zaune na jinsu, sai da angon yayi tambayeta sannan ta magantu, _"Aysha kin gane ta._?
"Ina tunanin ko H Hamid, ko kuma Ummi nuhu, sune suke service a gidan tv."
Please ki taimaka bari naga photos d`in.
Photo album, na bikin suka miko mishi, sai da yaje kusan tsakiya kowanne photo kallon k'urilla yake mishi, ango nata zolayar shi shida amarya. Sannan da kyar yaga wani photo, ta gefe, fuskarta bata fito sosai ba, anyi, musu tana lik'i.
"Wannan ce.!!
Ya fad'a da sauri kuma da k'arfi.
ango ya karb'a ya mik'awa amaryar.
"Eh Itace.
Tare suka hada baki shida JB wajen cewa, "wacce daga ciki."?
"Hafsah H. Hamid ce."
Azuciyar shi ya maimaita sunan _Hafsah_ sunan hajiyarshi kenan fah.!!
"Duba don Allah ki taimaka min da number ta."
"Ai kasan chanjin layin nan da nayi Allah yasa akwai contact d`in."
Ta fada tana duba cikin wayar, kaf babu number aciki.
Ta dube shi itama ya dan bata tausayi wallah kaga babu.
_Innalillahi."!!_
JB ya dafa shi, kada ka damu, ai bazamu bar k'asar nan ba, sai an samar maka solution, don bazan zuba ido a zautar min da UK ba.!!
Ukhasha, yaso ya tambayi amaryar _"ko tasan gidansu ta kwatanta mishi.?_ Amma sai ya fasa, yaji nauyin hakan, kada suga kamar ya takura musu.
Abisa tilas ya hak'ura, ya dawo gida a sanyaye, don kafin ya taho ma, sai da aysha ta gwada number wata k'awarsu, don ta turo musu number amma wayar tak'i shiga..
_Sun rabu akan, ana samu JB zai turo mishi. Yayi musu godiya sosai, sannan yabar gidan.._
A takaice dai sai ranar alhamis da dare, sannan number tazo, wajen ukhasha, shima da daddare wajen k'arfe shad'aya, duk zumud'inshi, dole ya hak'ura zuwa da safe. Yayi godiya ga Allah ba adadi.
Washegari sakayau yake jin shi, cikin nishad`i da karsashi yayi shirin fita office.
Ya nufi d'akin hajiyarshi ya mata sallama, sannan ya fito. Har ya isa bakin motar shi zai sa mata _Key_ yaji an kwalo mishi kira. _Yaya Ukhasha!!_
Mahseem ce autarsu cikin uniform.
Ta Kara'so da gudu ta d'ane shi.
"Muhaseem zaki karya ni fah.
Tayi dariya. Sannan ta sake shi.
"Yaya don Allah na bika ka sauke ni a school."?
"Eh muje." Ya zagaya ya bud'e mata k'ofar ta shiga. Sannan shima ya dawo ya shiga ya zauna. Ya tada motar aka bude musu gate, suka fita.
Suna tafiya tana damunshi da hira, "Yaya, wai yau Friday koh."?
Eh, ya akayi."?
"Zaka je dani Masjid d`in abba."?
"Waya ce miki mata na zuwa masjid."?
"Our islamiyya teacher, kuma su yaya Maryam suna zuwa wataran, amma sunki suje dani."
"To zanje dake, amma ni ba masallacin Abba nayi niyyar zanje ba, amma tunda kinaso to zamuje sai ki shirya da wuri, nima zan dawo da wuri."
"Thank you, Yaya."
Tayi shuru, sannan ta kuma samun abun cewa, "Yaya wai aunty Fadwa tace wai an kusa bikinka."?
Yayi murmushi me sauti, _"Kai fadwa ta raina shi, wato abin ma har ya kai a gaban Mahseem suna gulmar shi._?
Ta katse mishi tunani "Eh Yaya."?
Ya d'aga mata kai, alamar Eh."
"To ya sunanta."?
Ahankali yace mata, "Sunan Hajiya ne da ita."
"Yehhh, yaya mu dinga ce mata hajiya itama."
"To, kiyi mana addu,a idan mukaje masallaci."
"Yaya me zance toh."
_Kice Ya Allah ka taimaki Yaya ukhasha!!._
"To yaya zanyi, dama "Abba kullum sai yace mu dinga yin addu,a."
"Yawwa, 'yar autar mama, nagode.
Yayi parking, sannan ta fito, don anzo k'ofar makarantar su.
"Yaya adawo lafiya, zan shirya da wuri.
Ya daga mata hannu. Yana gani ta hango wasu k'awayenta ta tafi da gudu wajensu, sai ta bashi dariya ma.
Sanda ya dawo har Mahseem ta gama shiryawa, lokacin, shikuma, yana d'akinshi ya gama shafa mai, tazo bakin k'ofa ta tsaya.
Yana jiyo, hayaniyar su Zainab daga cikin gida, suna tsokanarta, _"Inyeh yau za,a masallacin Abbah!!_
"Salamu alaikum. Tayi sallama daga waje, yayo mata magana daga ciki, don bazai bata izinin shigowa ba, "Mahseem ki jirani kinji, kije d'akin Hajiya."
Ta koma ciki shi kuma, ya cigaba da shi shirin shi, cikin nutsuwa, gefen zuciyarshi da tunanin Hafsah, so yake sai ya dawo daga masallacin sannan ya gwada kira. Yana so ne sai yayi addu,a sosai ya nemi d'aukin Allah da alkhairansa cikin abin.
Yayi kyau cikin farar shaddar shi, da bak'ar hula, bakin takalmi, da kuma agogo.
Ya nufi d'akin hajiyar, shi kanshi daya ga Mahseem sai da dariya tazo mishi, taci hijabi har k'asa, ga tasbaha a hanunta.
hajiyar bata nan ma. Tana ganinshi ta taso da gudu ta rik'e hannunshi.
Shima ya kama nata, idon Fadwa akansu, zatayi magana irin ta zolayar data saba ya kafe ta da ido. "
Zoki mana photo, sai kiji dad`in kallon mu sosai."
"Kai Yaya ni baku nake kallo ba.!
Ta matso ta amshi wayar, tayi musu, sannan ta mik'a mishi kayarshi.
_Ya karb'a sannan yaja hannun Mahseem, suka fita, tana mishi hira.._
📝
*HAJEEYAH KHAREEMERH*