← Book details Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 88

Sashe 63

Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sai lokacin Basma tayi murmushi jin dad'i duk da dai tasan akwai aiki a gabanta, amma ta d'anji sanyi cikin ranta.

"Mama ta mik'e bari in tafi zanyi bak'i."
Ina fatan dai baki da matsala da waccen matar."

Basma ta girgiza kai, "No mama sai dai ta isheni da wa,azi."

"Hahh, hajiya Halima ta sheke da dariya, _"Makira Salma kenan.!"_
Ta nuna, Basma da yatsa alamar gargad'i.
"Kada dai ta baki wani abin kisha."
Basma ta d'aga kai alamar, "Toh"
"Tashi ki raka ni kinji."
Basma ta goge fuskarta suka fito.

Suna tafiya, Hajiya Halima, na k'ara tsara mata yadda za,tayi."

"Ki shawara da Teemah take kowa, K'awar nan taki."
"To Mama."
Yawwa sai kace ba Basma na ba kina 'yar zamani juya namiji ya gagareki."?
Basma tayi murmushi an fasa mata kai.

Har bakin motar mama ta raka maman, sannan ta shige tana d'aga mata hannu.
"Taja ta ta tafi."

Basma ta dawo gida, ta dad'e cikin shiru domin nemar wa kanta mafita, amma ta rasa.

Tana kwance wayarta tayi k'ara, kirane ya shigo ta duba da sauri, lokaci guda taja tsaki har kiran ya katse.
Yana katsewa wani kiran ya k'ara shigowa cike takaici ta danna _Dismiss,_ tayi _rejecting_ kiran.

"Aikin banza aikin hofi.!!
Ta fad'a.

Basma bata so abinda Teemah tayi mata ba kuma tayi, mamaki da tak`i bata shawara, sai goyon bayan hukuncin abba da take, kuma tana karanta mata ta kyale Yusuf, don haka taji bazata k'ara yi mata zancen ba.
Nan ta shiga tunani, sai ta tuno da wata k'awarta "Hala."

Wacce bayan dawowarta gidan abbah ne duk gayyar tasu ta watse suka daina had'uwa a gida sai dai duk sanda Basma ta sami dama ta lek'a club to suna had'uwa."

Nan da nan ta rarumi wayarta, zata kira Hala, sai taci karo da text akan wayar tata.

_"Problem"!_
Shine sunan Nour awayar tata.

Ta danna don taga abinda ya rubuto mata.

*Basma abinda kke min bai dace ba, ki tsaya mu fahimci juna don Allah..*
*I luv u..*

"Mts, taja tsaki.
Sannan ta nemo number Hala ta doka kira.

Tana d'agawa tace,
"Basma jama,ar Duniya kina nan kuwa.!!

Cikin damuwa tace, "Yes Hala, ai ni abu ne ke neman kwab'e mini."

"Wanne abu kuma, ke da naga kwanaki kinyi Babban kamu?."

Basma ta d'anyi yak'e, "wanne irin Babban kamu"."?

Gayen da kuka had'u recently mana."
"Hmm, Inji Basma sannan tace, Akwai matsala k'awata.
"Wacce irin matsala kuma."?
Hala ta tare ta da mamaki.
"Ba zaki gane ba but please gobe idan zaki sami dama kizo please da akwai magana."

"Zan sami time kuwa Basma."?

"Please k'awata wallahi akwai _big problem ne ina cikin damuwa fah."_

Basma ta fad'a cikin raunin murya.

Hala tace,
Basma zuwa gidanku yanzu _is not easy_ kin sani kema _your brother_ d'innan Abdul yake ko wa,? bana son kallon rainin da yake min."

" _Sorry_ Hala ba zaku had'u ba ma."

"Okey to zanzo, but ki fad'amin abinda ke faruwa mana."?

_"I can't,_ duk a rud'e nake, abin bazai fad'u a waya ba fa."
Hala tayi ajiyar zuciya, "Okey zaki ganni toh."
"Thank you my friend."
"Byee"
Sukayi sallama...

📝
*HAJEEYAH KHAREEMERH*

♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so (Guba ne)*
💔💔

*By*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Khareemerh)*
*Dedicated to unique in your love heart*

📄 *52*

*Washe garin* tunda wuri Hala ta iso gidan su Basma, kai tsaye ta wuce sashin da d'akin Basman yake, babu ruwanta da duk wanda taci karo da shi bare su gaisa.

Sanye take cikin riga da skirt na atamfa, sai wani bak'in glass a fuskar ta, sai jaka a hannunta, kana ganinta ka ga yarinya 'yar hutu.

_Sun had'u da Basma ne wajen partyn wani abokin Basman, sun zauna sit d'aya a wajen, bayan sun gama shawa juna k'amshi sai kuma suka jone, ta dalilin wani da yazo wajen Basma ta yarfa shi. Hakan ya burge Hala, don tana son mace da aji (class.)_ Daga nan ta bud'i baki, _"Kin burgeni k'awata."_
Suka tafa ita da Basma.
"Allah kuwa bana son rainin hankali wasu mazan akwai tsaurin ido fa yasan ke fa ba _type_ d'inshi bace."
Suka sheke da dariya har da k'ara tafawa.
_To daga nan abotarsu ta fara, sai kuma akayi dacen halinsu yazo d'aya._
_Shekaru biyu kenan da had'uwar su tun Yusuf bai bar k'asar ba, yana saura k'iris ya tafi. Don haka bai san Hala sosai ba._

Cikin yauk'i Haala ta shigo falon da Basma take.

Ta nemi guri ta zauna, tana k'arewa ko ina kallo.

Basma ta fito jin alamun an shigo, kana kallon ta zaka karanci damuwa cikin fuskarta.

Tana ganin Haala tazo da gudu suka rungume juna cikin farin ciki.

Bayan sun saki juna ne, Haala ta kalli Basma tana yatsina fuska. Da mamaki take cewa.

"Big girl kinga yadda kika koma kuwa, meya sameki ne haka"?

Basma tayi narai narai da ido, kamar zatayi kuka, cikin damuwa ta fara karantowa Haala damuwarta.
Har zuwan mamanta da abinda maman tace sai da tafad'a mata ta k'are da cewa, _"Haala na rasa yadda zanyi wallahi ban san Nour zai zaman min k'arfen k'afa ba wallahi.."_

Haala ta dad'e cikin shiru, kafin daga baya ta fara magana.

"Ki daina damuwa k'awata, wannan ba abu bane da zaki damu kanki akai, ai kina da matakin d'auka. Tunda dai Abba ya nuna aure dole to za,ayi, amma fa da Yusuf.!!"
"Basma ta kalleta da mamaki."
Ta k'ara kallon Basma, _"Ko kin shirya escaping kuma toh."?_
Basma ta waro ido. "Noo rufamin asiri, ina zanje.."? So kike na tonawa kaina asiri.."? After that duk inda zani ma sai abba ya nemo ni.!!

Haala bata ce komai ba illa wayarta data d'auka. "To bani number Yusuf.

Tace da Basma, babu musu Basma tasa mata number.

Kasak'e Basma tayi tana kallon Haala yayin da ta saka wayar a kunnenta.

Cikin wata irin murya mai daukar hankali Haala tace,
"Hello."
Hello akace daga d'aya b'angaren.

"My DEar!
Ta fad'a cikin shagwab'a.
"How're you."?
Yace mata.

Cikin kissa tace, "Baby ka tafi, baka fad'amin ba, then kana tambaya na, ya nake koh."

_Ya shiga rud'ani_
"Am sorry Baby.
"Bangane muryanki ba pls tell me wace ne."?

"You say what "?
"Sweet nine ka manta ko."?

Nan ya dan rud'e saboda sunan da ta kirashi _'sweet'_ ta tuna mishi da wata yarinya da yake ji da ita, kafin tafiyar shi ne yayi _missing contact_ din yarinyar, gashi had'uwa irin tasu bai san gidan su ba. _May be_ a irin goge-gogen da Basma take mishi ne a waya ta goge mishi lambar.

"Please Baby tell me mana kinji."
Haala ta k'ara shagwab'e murya, wallahi I won't tell u, tunda ka manta ni shikenan, dama ce maka zanyi na dawo N'ija cikin satinnan."

"Oh Baby am sorry I missed you over, kiyi hak'uri kinji Honey plz."

"Hmm, ban hakura ba fa, ka sami 'yan mata ka manta ni nagode."

"Haba _Honey plz_ kinji mana, wallah _I missed your contact that's why._Amma ina kewanki sosai Honey."

Hmm, Okey naji zan hak'ura amma fa don kaine.

"Oh Baby thank you Muah." yai mata kiss ta waya.

"Hmm sweet like kana missing me d'innan."

Yes, baby wallahi I do."

"Wai Baka dawo bane."?
Honey naji dad'i da kika kirani fa, da nan da _2weeks_ zanzo nija amma yanzu zanzo nan da _1week_ saboda ke.

"Wow sweet, Allah kawo ka kaji."

Okey Baby, please amma ki saki jiki idan nazo kinji."

Baka da matsala sweet."

"Wow Baby kin biya ni fa i miss you."
Ina aiki ki jira ni da dare zamuyi video call.
"Okey sweet."
Tace mishi.
Sukayi sallama.

"Basma ta rungume Haala tana ihu." Duk da tana dan kishin wayar da sukayi.

"Kinga cikin sauki yana dira muma muyi gidan nasu koh"?

"Yes inji basma, Kinga ranar saura 1day lokacin da Dad ya dibar min."

"Kada ki wani damu k'awata." Inji Haala.

"But kada ki kira Yusuf ke, ki share shi a zuwan kin bar zancen shi.

Okay k'awata.
Daga nan Haala ta cigaba da tsarawa Basma yadda zasuyi da Yusuf d'in.

B'angaren Haala kuwa cikin kwanakin ta samu damar Yusuf sosai, duk da cewa, daga baya Yusuf ya gano ta amma, saboda gudun kada ya kub'ce mata sai ta fad'a mishi cewa ta tsinci number dinshi ne cikin wayarta kuma tabbas ada sunyi rayuwa amma ba su dad'e ba ya bar k'asar.

Kan Yusuf ya kulle, to abu ne dayawa, yana da 'yanmatan da bai san adadinsu ba shi kanshi. Don haka sai ya yi mata wata tambaya guda d'aya don ya tabbatar.
"Kin san wata yarinya Basma."?
"Wa ce Basma kuma."?
Ta mayar mishi da tambaya ita ma.

"Hmm, kin santa mana."
Yace mata.

Yes she's my friend. Ta bashi amsa kai tsaye.
"Hmm, Zatayi aure koh."?
"Yes.!
Haala ta bashi amsa babu wani kwane-kwane.

Yayi ajiyar zuciya.
"Bana son idan nazo N'ija, ta sani.!!

"Hmm, saboda me."?

"Zata dameni ne.. Yai wani murmushi "Hmm yarinyar tana so ta batamin rai ne."
"Kamar Yaya"? Haala ta tambaya.
( _Kamar bata san abinda ke faruwa ba._)

"So take wai na aureta a nata haukar."

Haha Haala ta shek'e da wata dariya.
"Me zai hana ka."?
Hmm, babu aure a schedule d'ina sai nan da 3years idan ma auren ne. And sam bata cikin 'yan mata da zan iya aura.!!
"Hmm.. Haala tace.
"Yes, kota aiko ki ne domin ki sani aurenta koh."?

Ya fad'a kai tsaye yana mata wani dariyar na-gano ku daga baya.!!

Babu b'oye-b'oye Haala, tace mishi "Yes.
"Hmm sai kuma kika yarda zaku iya koh"?

"Yusuf kana so Basma."?
Ta tambaye shi maimakon ta bashi amsa.
"Hmm, ki tambayeta ai, we're just friends ba soyayya muke ba.

"Hahh.. Do you know why I accepted her request data ce nayi convinced naka ka dawo Nija."?

"Hmm ashe hakan ne ko."? So na gane ku ai."
"No..no.. no.. no, I just came for my own reason."
"Idan zaka yarda nima mu zama friends mana."

Ta fad'a kai tsaye babu wata shakka.

Yusuf yaji dad'i a ranshi ko ba komai ya sami wajen zuwa idan ya dawo k'asar.

"Hmm you're welcome."
Yace ita.
Chapter 63 · 0% Book details