Sashe 61
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*'WANI B'ANGAREN'*
_________________________
'Tana kwance, shiru ita kad'ai tayi tagumi fuskarta cike da damuwa fal sam bata son ta ina zata fara ba, amma dole ne ta samarwa kanta mafita tunda bata da ishashshen lokaci.'
'Ta janyo wayarta, ta danno number shi, ta samu da
kyar ta shiga.
'Wayar tayi ta ringing amma ba,a d'aga ba, har ta gaji ta hak'ura, sai kuma ta tuna cewa lokaci yana k'ure mata.'
'Don haka ta shiga Email ta fara tura mishi sak'o..'
"I called you but u didn't picked my call.. WHY??
Please ka kirani sai muyi magana."
'Bayan ta aika ne bbu jimawa kuma yai mata reply da "Okey" kawai.
'Tayi ta jiran kiran nashi amma babu kiran.'
'Abinda bata sani ba shine, shi yanzu gaba-d'aya ba ta ita yake ba sam, don shi ya gama yayinta.'
'Sai can dare kiran nashi ya shigo, da sauri ta d'aga.
"Hello
"Hi
"How are you
"Am fine, um naga kin kin min Email mene ya faru ne."
'Hum tayi ajiyar zuciya.' sannan ta marairaice ta fara magana.'
"Akwai damuwa ne fah. Yesterday, Dad ya kira ni, yace min in fito da wanda nake so amana aure.. If not kuma yace akwai wanda ya mishi magana so zai bashi dama kawai."
"Tunda ta fara yake sauraronta har tazo nan sannan yace,
"To yanzu what's solution."?
Cikin takaici tace,
"Hmm you already knew that ba zan iya auren wani ba idan ba kaiba koh.."?
"What.. what are you saying..??
'Wutar kanta ta d'auke ta tsaya cak, au tambayarta yake me take fad'a ma."?
Sai kuma taga asarar ta k'yaleshi don haka tayi k'arfin halin cewa, "Yusuf nasan kaji me nake fad'a maka, amma kake nunamin baka ji ba koh."?
"Hmm.. Yai wani murmushin rainin hankali.. "naji mana... kuma aini murna ma zan miki zakiyi aure koh."?
"Hum, Okey haka kace koh."?
"Hmm, so ya kike so nace en mata."?
"Hmm, thanks
thank you very much."
'Ta fad'a cike da rashin sanin matakin d'auka.'
"Okay, yace kawai sannan ya katse wayar.'
"Ta saki wayar ta fad'i k'asa, ta dafe kanta da hannu biyu, bata da wani abinyi sam..
'Kogin tunani ta fad'a akan yadda rayuwarsu ta baya ta kasance..'
'Idan ta k'irga zata ga a daddafe tayi shekara d'aya da rabi rabon da taga Yusuf ido da ido.'
'Ta sani, asanda ta mallaki Yusuf ta mallakeshi sosai har tsahon shekaru kusan uku ta shimfida mulki a rayuwarshi tayi sa,ar rabashi da wasu abubuwa muhimmai cikin rayuwarshi misali "HAFSAH."
Tun a wancan lokacin ta tabbatar wa da kanta cewa, "Lallai soyayyar da Yusuf ke yiwa Hafsah, ta gaskiya ce, domin sunsha fad'a akan ambaton Hafsah da Yusuf ke yawanyi tare da zargin kansa akan _'Ya ci Amanarta'_
Yusuf ya kashe mata kud'ad'e da ita kanta bata isa ta kirga su ba, sun shimfida rayuwa mara dad'in bada tarihi.. Don tun tana abubuwan ta ab'oye har takai mamanta ta sani, lokacin hankalin maman ya tashi, amma ta gaza iya yin komai don ta bari sai da abin yafi k'arfinta.'
'Alokacin ta yanke shawarar maida Basman wajen mahaifinta, wanda mamakin hakan ya sashi shakkar karb'arta.
'Da kyar ya yarda ta koma gidan nashi, ya kuma saka ido sosai akanta, ahankali ya fara gano cewa tabbas tarbiyyar 'yartashi ta dade da rugujewa.'
Sanda Allah ya dubeshi sai akayi sa,ar barin Yusuf K'asar gaba-d'aya ya sami aiki.'
Lokacin neh Abban Basma yaga tab'ara kala-kala, wato Basma ta sha auna tserewa daga gida a nufinta na sai tabi Yusuf duk inda zai tafi, akan wani alk'awarin k'arya da Yusuf d'in yayi mata wato zai aure ta acan k'asar da zai koma.'
Lokacin tana level 200, a makaranta
Bayan tafiyar Yusuf d'inne, lokacin Basma ta fara ganin sauyi daga gareshi, sannan ta fara fahimtar cewa lallai sahun giwa ne ya fara take na rakumi, _wato yaje can ya had'u da dai-dai shi.'_
Lokacin kuma ta fara fuskantar rashin kulawa daga gareshi har takai sai su shafe sati bai waiwayeta ba.'
'Ayanzun ma da ta nemeshin, sun shafe fiye da wata d'aya, basuyi magana ba koda a waya kuwa.'
'Ta sani bata da wani tsayayye, wanda zata iya kawo mishi zancen ya aureta, duk tarin samarin nata irin kalar Yusuf d'inne wadanda suka maye mata gurbin shi bayan tafiyarshi.'
'Nour' shine Abba ke son had'ata dashi, duk da bai kamata ta kira hakan amatsayin 'Auren had'i' ba, domin Abba ba d'akko shi yayi yace zai bashi ba, ganinshi yayi a wajenta kuma dake ya gaji da irin take- taken ta sai yai mishi izinin ya turo iyayenshi kawai, kuma akayi dacen shima hakan ne manufarshi.'
'Bashi da wata makusa, d'an manyan mutanene, shekarunshi ba zasu wuce 30, ba, bai wani girmi Basma sosai ba, amma yana da nutsuwa sosai.'
'Basma ta ja tsaki, sanda ta tuno shi, wai ita ake shirin yiwa aure ba tare da son ranta ba.'
'Ta rarumi wayarta ta danna kiran wata k'awarta.'
"Hello Basma."
"Teemah, babu lafiya fa."
"Meya faru kuma."
"Kinga na kira Yusuf yaki ma ya saurareni yadda ya dace bare muyi magana."
"Kinsan me zan fad'a miki k'awata."?
"Ina jinki."
"Wallahi mu,amalarku tayi k'arko keda Yusuf."
"Bangane me kike nufi ba."
"Hmm, ina nufin yadda kuka dad'e tare keda shi, kema kin sani samarin yanzu ba amana ce dasu ba, bare shi da yanzu ma bakwa kusa keda shi."
"Hmm, Teemah, ahakan kike fad'ar haka."?..kin san rabona da Yusuf kusan 2years kenan."?
Koma yayane nidai ina fad'a miki kun dad'e keda Yusuf, kuma ni yanzu shawaran da zan baki shine kawai ki yarda kiyi aurenki don banajin Yusuf zai aureki.!!
"Ke Teemah, bana son wulak'anci, ai ke auren kikayi da kike cewa inyi aure kuma a rainin hankalinki zaki ce in auri wani ba Yusuf ba."??
"Hmm, ni dai gaskiya na fad'a miki, kuma ni ko ayanzu na sami wanda yazo yacemin yana sona da aure, wallahi auren shi zanyi kindai san babu yadda za,ayi kuyi irin rayuwar da kuke da Yusuf sannan kuma yace zai aureki.!!
"Kada ki fad'a min maganar banza, har ni zaki zaga, kice muna rayuwar banza, kema ba irin ta kikeyi ba."?
"Hmm, Basma ni ba cemiki nayi ba ita nakeyi ba, amma kinsan ni bankaiki ba don, ban watsar da mutunci na atiti ba, _kefa dakanki kika fad'amin kin bawa Yusuf komai saboda haka kisan da sani Yusuf ba zai aureki ba zaki ce na fad'a miki.."_
"Ta katse wayar, tabar, Basma na zage-zage tana fad'in k'aryane bazai yiwu ba."
Daga bisani ta mik'e ta nufi, d'akin abbanta, fuskarta babu annuri don amsa kiran da yayi mata.
Tayi sallama a ciki-ciki sannan ta shige ciki.
Yana zaune, akan kujera, yana kallon TV, ta nemi guri ta zauna.
Cikin nutsuwa ya juyo ya kalleta, ta k'ara tamke fuska.
"Basma, ya muke ciki a maganar mu."?
Ta keb'e fuska kamar zatayi kuka, batace komai ba sai kallonshi da takeyi.
"Tambayarki nake don kada na yanke hukunci ki ga anyi miki ba daidai ba."
Bataga alamun wasa a tattare dashi ba don haka ta shiga hankalin ta kada ta tsaya wasa tayi wa kanta.
Ta bude baki ta fara magana, cikin shagwab'a.
"Abba fa munyi magana da Yusuf d`in yace zai zo k'asar nan nan da wata d'aya.
"Wata d'aya."?
"Eh Daddy"
"Hmm Basma ki shiga hankalinki dani, ba maganar wasa nake miki ba, kuma bazan tab'a zaman jira sai wata d'aya yayi zan yanke hukunci ba."
Ta d'ago da sauri ta kalleshi, cikin damuwa, "Allah abba da gaske zai zo."
Cikin fad'a ya fara mata magana,
"Wai ma waye Yusuf d'innan da kike ta fad'arsa, kullum daga anyi magana sai ki kawo zancen wanda baya nan, waye ubansa, ki fad'amin ni naje na same shi."
Gabanta yayi wata muguwar Fad'uwa,
"Ta d'ago ta kalleshi.
"Eh, na gaji da wasa da hankalin da kike min, idan ma k'arya kike babu wani Yusuf ai zan sani ne."
Kawai yaro, yazo da magana amma kina sani ina ta magana biyu, to baki isa ba, kuma kada na sake ganin kin fita daga gidan nan bada sani na ba."
Na baki sati daya idan banga Yusuf a gidannan ba, to dole ki karbi, zabina, shashashar banza kinfi gane kiyi ta gantali ko."?
Hankalinta tashe ta nufi d'akinta, sam ta rasa sanin abinyi, gashi wai har wata dokar hana fita aka sa mata wanda tabbas tasan ba zai yiwu ba.
Kamar an tsikareta ta fizgo wayarta babu shiri, ta danna kiran mamanta, tana d'agawa Basma ta fara kuka, cikin tashin hankali take tambayarta "Lafiya meya faru."?
"Ba kece kika kama kin dawo dani gidannan sai wulak'anta suke gashi sun zuga abba wai aure zaiyi min.!!
Duk da tasan za,a runa, amma maganar ta shigeta da taji cewa, ba zab'in 'yar tata za,a bata ba.'
"Aure, kuma..??
Tab to wa zai aura miki."?
Wani ne daga yazo gurina ya ganshi shine yace ya turo iyayenshi."
"Okay ki kwantar da hankalinki zamuyi maganar da shi bazata yiwu ba."
Ta danji sanyi aranta don haka tace "To Mama."
Maman ta d'ora da cewa, "Wato hajiya Salman ce ke zuga shi ko."? Shikenan dani take zancen, dama ke kika jawo wa kanki ai, badon haka ba me zai kaiki gidannan da zama, I hope bata takura miki ita da samarin 'ya'yan nan nata."?
Basma tasan Indai gaskiya zata bi hajiya Salma a 'ya ta d'auketa, yayyenta maza su uku ne biyu, sunyi aure sai kuma mace guda d'aya "Aunty Meenat."
Sai Basman wacce uwarta ita kad'ai mamanta ta haifa sannan ta fita, sai na'imah sai autar hajiya Salma wato Nuratu.'
"A,a ni bana ma shiga harkarsu, yaya Abdul ne yake samin ido komai nayi sai yayi magana."
"Tab bazai yiwu ba, dole zan mishi magana babu wanda ya isa ya takura miki gida, gidan ubanki ne kema."
"Thank you mum."
Kuma ki maida hankali akan karatun ki, yawon nan da kike yi idan ma baki daina ba gaki ga Dad din naki nan ai."
_________________________
'Tana kwance, shiru ita kad'ai tayi tagumi fuskarta cike da damuwa fal sam bata son ta ina zata fara ba, amma dole ne ta samarwa kanta mafita tunda bata da ishashshen lokaci.'
'Ta janyo wayarta, ta danno number shi, ta samu da
kyar ta shiga.
'Wayar tayi ta ringing amma ba,a d'aga ba, har ta gaji ta hak'ura, sai kuma ta tuna cewa lokaci yana k'ure mata.'
'Don haka ta shiga Email ta fara tura mishi sak'o..'
"I called you but u didn't picked my call.. WHY??
Please ka kirani sai muyi magana."
'Bayan ta aika ne bbu jimawa kuma yai mata reply da "Okey" kawai.
'Tayi ta jiran kiran nashi amma babu kiran.'
'Abinda bata sani ba shine, shi yanzu gaba-d'aya ba ta ita yake ba sam, don shi ya gama yayinta.'
'Sai can dare kiran nashi ya shigo, da sauri ta d'aga.
"Hello
"Hi
"How are you
"Am fine, um naga kin kin min Email mene ya faru ne."
'Hum tayi ajiyar zuciya.' sannan ta marairaice ta fara magana.'
"Akwai damuwa ne fah. Yesterday, Dad ya kira ni, yace min in fito da wanda nake so amana aure.. If not kuma yace akwai wanda ya mishi magana so zai bashi dama kawai."
"Tunda ta fara yake sauraronta har tazo nan sannan yace,
"To yanzu what's solution."?
Cikin takaici tace,
"Hmm you already knew that ba zan iya auren wani ba idan ba kaiba koh.."?
"What.. what are you saying..??
'Wutar kanta ta d'auke ta tsaya cak, au tambayarta yake me take fad'a ma."?
Sai kuma taga asarar ta k'yaleshi don haka tayi k'arfin halin cewa, "Yusuf nasan kaji me nake fad'a maka, amma kake nunamin baka ji ba koh."?
"Hmm.. Yai wani murmushin rainin hankali.. "naji mana... kuma aini murna ma zan miki zakiyi aure koh."?
"Hum, Okey haka kace koh."?
"Hmm, so ya kike so nace en mata."?
"Hmm, thanks
thank you very much."
'Ta fad'a cike da rashin sanin matakin d'auka.'
"Okay, yace kawai sannan ya katse wayar.'
"Ta saki wayar ta fad'i k'asa, ta dafe kanta da hannu biyu, bata da wani abinyi sam..
'Kogin tunani ta fad'a akan yadda rayuwarsu ta baya ta kasance..'
'Idan ta k'irga zata ga a daddafe tayi shekara d'aya da rabi rabon da taga Yusuf ido da ido.'
'Ta sani, asanda ta mallaki Yusuf ta mallakeshi sosai har tsahon shekaru kusan uku ta shimfida mulki a rayuwarshi tayi sa,ar rabashi da wasu abubuwa muhimmai cikin rayuwarshi misali "HAFSAH."
Tun a wancan lokacin ta tabbatar wa da kanta cewa, "Lallai soyayyar da Yusuf ke yiwa Hafsah, ta gaskiya ce, domin sunsha fad'a akan ambaton Hafsah da Yusuf ke yawanyi tare da zargin kansa akan _'Ya ci Amanarta'_
Yusuf ya kashe mata kud'ad'e da ita kanta bata isa ta kirga su ba, sun shimfida rayuwa mara dad'in bada tarihi.. Don tun tana abubuwan ta ab'oye har takai mamanta ta sani, lokacin hankalin maman ya tashi, amma ta gaza iya yin komai don ta bari sai da abin yafi k'arfinta.'
'Alokacin ta yanke shawarar maida Basman wajen mahaifinta, wanda mamakin hakan ya sashi shakkar karb'arta.
'Da kyar ya yarda ta koma gidan nashi, ya kuma saka ido sosai akanta, ahankali ya fara gano cewa tabbas tarbiyyar 'yartashi ta dade da rugujewa.'
Sanda Allah ya dubeshi sai akayi sa,ar barin Yusuf K'asar gaba-d'aya ya sami aiki.'
Lokacin neh Abban Basma yaga tab'ara kala-kala, wato Basma ta sha auna tserewa daga gida a nufinta na sai tabi Yusuf duk inda zai tafi, akan wani alk'awarin k'arya da Yusuf d'in yayi mata wato zai aure ta acan k'asar da zai koma.'
Lokacin tana level 200, a makaranta
Bayan tafiyar Yusuf d'inne, lokacin Basma ta fara ganin sauyi daga gareshi, sannan ta fara fahimtar cewa lallai sahun giwa ne ya fara take na rakumi, _wato yaje can ya had'u da dai-dai shi.'_
Lokacin kuma ta fara fuskantar rashin kulawa daga gareshi har takai sai su shafe sati bai waiwayeta ba.'
'Ayanzun ma da ta nemeshin, sun shafe fiye da wata d'aya, basuyi magana ba koda a waya kuwa.'
'Ta sani bata da wani tsayayye, wanda zata iya kawo mishi zancen ya aureta, duk tarin samarin nata irin kalar Yusuf d'inne wadanda suka maye mata gurbin shi bayan tafiyarshi.'
'Nour' shine Abba ke son had'ata dashi, duk da bai kamata ta kira hakan amatsayin 'Auren had'i' ba, domin Abba ba d'akko shi yayi yace zai bashi ba, ganinshi yayi a wajenta kuma dake ya gaji da irin take- taken ta sai yai mishi izinin ya turo iyayenshi kawai, kuma akayi dacen shima hakan ne manufarshi.'
'Bashi da wata makusa, d'an manyan mutanene, shekarunshi ba zasu wuce 30, ba, bai wani girmi Basma sosai ba, amma yana da nutsuwa sosai.'
'Basma ta ja tsaki, sanda ta tuno shi, wai ita ake shirin yiwa aure ba tare da son ranta ba.'
'Ta rarumi wayarta ta danna kiran wata k'awarta.'
"Hello Basma."
"Teemah, babu lafiya fa."
"Meya faru kuma."
"Kinga na kira Yusuf yaki ma ya saurareni yadda ya dace bare muyi magana."
"Kinsan me zan fad'a miki k'awata."?
"Ina jinki."
"Wallahi mu,amalarku tayi k'arko keda Yusuf."
"Bangane me kike nufi ba."
"Hmm, ina nufin yadda kuka dad'e tare keda shi, kema kin sani samarin yanzu ba amana ce dasu ba, bare shi da yanzu ma bakwa kusa keda shi."
"Hmm, Teemah, ahakan kike fad'ar haka."?..kin san rabona da Yusuf kusan 2years kenan."?
Koma yayane nidai ina fad'a miki kun dad'e keda Yusuf, kuma ni yanzu shawaran da zan baki shine kawai ki yarda kiyi aurenki don banajin Yusuf zai aureki.!!
"Ke Teemah, bana son wulak'anci, ai ke auren kikayi da kike cewa inyi aure kuma a rainin hankalinki zaki ce in auri wani ba Yusuf ba."??
"Hmm, ni dai gaskiya na fad'a miki, kuma ni ko ayanzu na sami wanda yazo yacemin yana sona da aure, wallahi auren shi zanyi kindai san babu yadda za,ayi kuyi irin rayuwar da kuke da Yusuf sannan kuma yace zai aureki.!!
"Kada ki fad'a min maganar banza, har ni zaki zaga, kice muna rayuwar banza, kema ba irin ta kikeyi ba."?
"Hmm, Basma ni ba cemiki nayi ba ita nakeyi ba, amma kinsan ni bankaiki ba don, ban watsar da mutunci na atiti ba, _kefa dakanki kika fad'amin kin bawa Yusuf komai saboda haka kisan da sani Yusuf ba zai aureki ba zaki ce na fad'a miki.."_
"Ta katse wayar, tabar, Basma na zage-zage tana fad'in k'aryane bazai yiwu ba."
Daga bisani ta mik'e ta nufi, d'akin abbanta, fuskarta babu annuri don amsa kiran da yayi mata.
Tayi sallama a ciki-ciki sannan ta shige ciki.
Yana zaune, akan kujera, yana kallon TV, ta nemi guri ta zauna.
Cikin nutsuwa ya juyo ya kalleta, ta k'ara tamke fuska.
"Basma, ya muke ciki a maganar mu."?
Ta keb'e fuska kamar zatayi kuka, batace komai ba sai kallonshi da takeyi.
"Tambayarki nake don kada na yanke hukunci ki ga anyi miki ba daidai ba."
Bataga alamun wasa a tattare dashi ba don haka ta shiga hankalin ta kada ta tsaya wasa tayi wa kanta.
Ta bude baki ta fara magana, cikin shagwab'a.
"Abba fa munyi magana da Yusuf d`in yace zai zo k'asar nan nan da wata d'aya.
"Wata d'aya."?
"Eh Daddy"
"Hmm Basma ki shiga hankalinki dani, ba maganar wasa nake miki ba, kuma bazan tab'a zaman jira sai wata d'aya yayi zan yanke hukunci ba."
Ta d'ago da sauri ta kalleshi, cikin damuwa, "Allah abba da gaske zai zo."
Cikin fad'a ya fara mata magana,
"Wai ma waye Yusuf d'innan da kike ta fad'arsa, kullum daga anyi magana sai ki kawo zancen wanda baya nan, waye ubansa, ki fad'amin ni naje na same shi."
Gabanta yayi wata muguwar Fad'uwa,
"Ta d'ago ta kalleshi.
"Eh, na gaji da wasa da hankalin da kike min, idan ma k'arya kike babu wani Yusuf ai zan sani ne."
Kawai yaro, yazo da magana amma kina sani ina ta magana biyu, to baki isa ba, kuma kada na sake ganin kin fita daga gidan nan bada sani na ba."
Na baki sati daya idan banga Yusuf a gidannan ba, to dole ki karbi, zabina, shashashar banza kinfi gane kiyi ta gantali ko."?
Hankalinta tashe ta nufi d'akinta, sam ta rasa sanin abinyi, gashi wai har wata dokar hana fita aka sa mata wanda tabbas tasan ba zai yiwu ba.
Kamar an tsikareta ta fizgo wayarta babu shiri, ta danna kiran mamanta, tana d'agawa Basma ta fara kuka, cikin tashin hankali take tambayarta "Lafiya meya faru."?
"Ba kece kika kama kin dawo dani gidannan sai wulak'anta suke gashi sun zuga abba wai aure zaiyi min.!!
Duk da tasan za,a runa, amma maganar ta shigeta da taji cewa, ba zab'in 'yar tata za,a bata ba.'
"Aure, kuma..??
Tab to wa zai aura miki."?
Wani ne daga yazo gurina ya ganshi shine yace ya turo iyayenshi."
"Okay ki kwantar da hankalinki zamuyi maganar da shi bazata yiwu ba."
Ta danji sanyi aranta don haka tace "To Mama."
Maman ta d'ora da cewa, "Wato hajiya Salman ce ke zuga shi ko."? Shikenan dani take zancen, dama ke kika jawo wa kanki ai, badon haka ba me zai kaiki gidannan da zama, I hope bata takura miki ita da samarin 'ya'yan nan nata."?
Basma tasan Indai gaskiya zata bi hajiya Salma a 'ya ta d'auketa, yayyenta maza su uku ne biyu, sunyi aure sai kuma mace guda d'aya "Aunty Meenat."
Sai Basman wacce uwarta ita kad'ai mamanta ta haifa sannan ta fita, sai na'imah sai autar hajiya Salma wato Nuratu.'
"A,a ni bana ma shiga harkarsu, yaya Abdul ne yake samin ido komai nayi sai yayi magana."
"Tab bazai yiwu ba, dole zan mishi magana babu wanda ya isa ya takura miki gida, gidan ubanki ne kema."
"Thank you mum."
Kuma ki maida hankali akan karatun ki, yawon nan da kike yi idan ma baki daina ba gaki ga Dad din naki nan ai."