Sashe 42
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Muje zuwa.👍🏼
♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so (Guba ne)*
💔💔
*By*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Khareemerh)*
*Dedicated to unique in your love heart*
📄 *38*
*Zaman* ta gidan Maman Ya Nazeer, zama ne da zata iya fassara shi da "Zaman qaruwa da qarin ilimi tare da samun experience akan rayuwa.
Zama ne wanda bata samu takura ba sam a yayinsa, sai ma tattalinta da aka dinga yi sam baa son kukanta.
Idan Hafsah zatayi lissafin mutane muhimmai wad`anda suka taka rawa a rayuwarta to tabbas daga abbanta, sai mamanta sai kuma yayar mahaifiyarta wato maman Ya Nazeer, kamar yadda suke karanta..
Bawai don sun dauki tsahon lokaci tare ba, a,a sai dai taimakon da ta bata na tsahon wata uku kacal, amma shine zatace ya tallafi rayuwarta har kawo yanzu, wanda badon ita ba da tuni ta zama wata abu ta daban ba Hafsar da take ayanzu ba."
To dama hakane, wad`ansu mutanen suna da irin wannan baiwar, wad`anda zama kad`an zakayi amma ka qaru da abinda zai tallafe ka har qarshen rayuwa.
Maman ya Nazeer, ta jata a jiki, ta dawo da ita hayyacinta lokacin da ta fita daga cikin shi, ta nuna mata cewa tana da da ma lokacin da tayi losing duk wai hope nata, _she lost hope and she's completely broke._
Bata taba tunanin zata iya rayuwar da babu Yusuf cikinta ba, sai gashi maman ta nuna mata cewa zata iya kuma ta koyar da ita yadda zata iya d`in, kuma gashi ta iya d`in.
Dole ne ta gode mata bisa wannan d`au ki data kawo mata cikin rayuwa wanda bata da abinda zata saka mata dashi banda addu,a.
Shiyasa wani lokacin Hafsan, ke tuhumar kanta da laifin _butulci_ na bujerewa Soyayyar Gudan jinin matar da ta tallafi rayuwarta.
Amma takanji sassauci idan ta tuna cewar kai tsaye, Maman bata da masaniya bisa hakan sai dai hasashe, kuma baza,a iya cewa tak`i Nazeer kai tsaye bane, sai dai ace tak`i bada fuska gareshi yadda zai shigar da buk`atar sa, har ya gaji ya haqurar wa zuciyarshi.
Ahankali take tuno abinda ya faru.
#TUNANIN #BAYA
Wato bayan isar su gidan ita da Mama a wancan lokacin sun isa gidan babu kowa cikin sa, kasancewar yaran sun tafi makaranta.
Driver ne ya shigo mata da kayanta, inda Maman ta nuna mata wani dak`i mallakin yarta Fatima tace "Kai kayan naki wancan dakin."
Ta miqe a hankali, ta ja trolley din ta nufi d`akin.
Sun yini su biyu ita da maman cikin nishad`i har Maman ta sa ta tayi musu girki, sai wajen qarfe biyu da rabi sannan yaran gidan suka fara dawowa.
Da farko Nazeer ne ya shigo wanda shine babban d`a a gidan, sai fateema mai binshi, sai Al,ameen, sai Nour, sai Siddiqa.
Hafsah ce kadai a palourn ta qurawa TV ido, Ahankali yayi sallama, da takarda a hannunshi ta dago kai ta kalli mai shigowa, ta amsa sallamar, sannan ta kauda kan ta.
Murmushishi ya fad`ad`a, "Hafsy ce yau a gidan namu."?
Tayi murmushi, Nice "Ya Nazeer ina wuni."? Ta gaidashi tana mai dan duk`awa daga kujerar da take.
Ya sakar mata murmushi sosai, yarinyar akwai tarbiyya ga Ladabi, lpia lau, Hafsah, ya mama Ina su zainab"?
"Suna lpia lau."
Ya qara kallon ta.
"Ina Mama nah"?
Ta kalleshi so take ya qara bayani ko zata fahimci zancen, wacce maman yake nufi.
Taji abinne banbarakwai babba dashi yana cewa Mamanshi.
"Ina Mamy nah nace."?
"Uhum. Maman ku."?
Yayi `yar dariya.
"Yes, mamy nah, ai mamie tawa ce ni kad`ai k`wace min akayi aka min rubdugu."
Hafsah bata ankara ba sai jinta tayi tana k`yak`yata dariya, a zuciyarta tana cewa dama haka Ya Naseer din yake da hira.?
Ta sani dai yana zuwa gidansu, amma bai fiya jimawa haka ba, kuma ita bata cika zuwa gidansu ta kwana ba, idan ma tazo yawanci yana school.
Dariyar su Mama ta jiyo ta fito zuwa a palourn. "Oh dama nasani ai sai kai."
Ta fad`a tana kallon Nazeer d`in.
Yayi kanshi mazauni a kujera kafin yace a shagwab`e Mama wai Taraba suka tura ni."
"Taraba"?
Mama ta maimaita,
Kuma kana so."?
Ya girgiza kai, gaskiya A,a Mama nafison koda jigawa neh."
Okay zanyi yiwa sunusi magana, tana nufin qaninta wanda shi maman su Hafsah ke bi."
"Okay mamy na Nagode."
"Mamy yunwa nakeji." ya fada yana dan shafa ciki."
Sannan ya miqe ya nufi, Kofar fita daga palourn domin dakinshi yana daga waje ne.
Mama ta bishi da kallo, sannan ta kalli Hafsah.
"Ikon Allah kinga ya fice, tashi ki zuba mishi abincin kafin ya dawo kinji."?
Toh Mama ta miqe ta nufi kitchen din.
Plask ta samu guda biyu, ta zuba abinci a babban dayan kuma tasa miya, sannan ta shirya komai kan tray, lokacin data fito Maman bata palourn kawai sai ta ajye akan dinning, kusan minti uku bai dawo ba, sai ta jiyo muryar Mama nacewa, "Hafsah ki miqa mishi abincin kinji don da kyar idan zai dawo.
"To, kawai tace, ta kinkimi tray din tayi dakin shi.
Ad`an ka re taga k`ofar don haka tura wa kawai tayi ta shiga da sallama.
Daga cikin wani daki a dan palourn ta jiyo an amsa inda ya fito ya tarar da ita da kayan tray a hannu, aiko yace me zaiyi idan ba dariya ba.
Ya k`ame yana kallonta yana ta qyaqyata dariya yana nuna ta har Hafsah ta tsorata.
Sannan ya gimtse ya fara magana, cike da shaqiyanci,
"La-la-la-la, gaskiya kina so mama ta zane ni kenan.
ta kalleshi ad`an tsorace sannan ta qara kallon tray d`in.
Ya sa Hannu ya amshi tray d`in ya ajye sannan ya cigaba da magana k`asa-k`asa.
"Wa yace miki anan Mama ke zuba min abinci."?
"Ai Matsayina bai wuce wannan ba."
Ya d`auki plate daga kan tray d`in yana nuna mata.
"Anan ake zuba min abinci kin manta bani ne mai gidan ba." Ya Qarashe zancen yana zaro idanunshi.
D`an murmushi tayi a qagauce, saboda gaba d`aya ji take kamar akan qaya take.
"Bata saba ba sam, ace wai gata ga wani namiji, tsaye irin haka daga ita sai shi, idan aka cire Yusuf, da shi kuma ta bashi wani Matsayi na daban.
Bata da yayye maza, sannan ba wasu mazaa ke shigo musu gida ba har su sami damar hira dasu, idan ka d`auke auncle Abdullah, sai shi Nazeer d`in, sai wad`and`a ba,a rasa ba cikin `ya`yan `yan uwa suma kuma jefi-jefi ne. Su a familynsu ma mata sunfi yawa.
Sannan bata son maman ya Nazeer, taga ta dad`e, don haka ta motsa K`afarta da niyyar juyawa ta tafi amma sai ya katse mata hanzari da cewa.
"Ni al,majiri ne a gidan." Ya fad`a da marainiyar murya.
"Please zubamin, a plate sai ki tafi da sauran."
Ranta bai so hakan ba amma bata da zab`i tana bashi girma a matsayinshi na Yayansu.
Ta tsuguna, da sauri sauri, take zubawa, ta cika plate d`in.
"Kaii ai bazan cinye ba rage min."
Ta kwashe wajen kwatar (quarter) abincin.
"Yawwa ko kefa."
bata ce komi ba tasa mishi miya da nama tasa mishi salad.
Sannan ta d`auke ruwan da ke kan tray d`in ta ajye mishi sannan ta d`auki tray d`in.
Tana lura da kafe ta da Ido da yayi.
"Thank you Qanwaty!
Taji ya fad`a
Bata ce komai ba ta juya tana sak`e sak`e a ranta.
_"Anya kuwa zata yarda, tayi koda kwana uku ne agidan nan bare kuma sati, matuqar za,a dinga zata ayyukan hidima irin wad`annan."??_
📝
*HAJEEYA KHAREEMERH*
♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so (Guba ne)*
💔💔
*By*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Khareemerh)*
*Dedicated to unique in your love heart*
📄 *39*
*Tana* komawa palour, fateema ta shigo ita ma da sallama, Hafsah ta amsa cike da farin cikin ganinta.
Itama da gudu ta qaraso ta rungume Hafsah tana murna da ganinta.
"Hafsy yau kece a Gidan namu."?
Hafsah tayi murmushi ita ma, Nice wallah auntie Fateema."
Fateema ta sake ta tana fad`in "Gaskiya naji dadie."
A palourn suka zauna suna hira, Fateema ta miqe taje ta zubo abinci ta dawo tana fad`in.
"Wata irin yunwa nakeji wallah."
"Sannunki.!!"
Hafsah ta fad`a tana qara kallonta.
"Level 3 kike koh auntie."?
( _Da ke ta girmi Hafsah da wajen shekaru uku._)
Eh, wata test mukayi mai zafi wallah."
Ta fad`a tana kai lomar abinci bakinta.
"Ke fa, kinyi candy kema koh."?
"Eh result nake jira."
To Allah ya bada sa,a.
"Amin."
Suna hirar, Ya nazeer ya qara shigowa, kamar tare suka shigo shida ragowar yaran gidan. Wad`anda murnar ganin Hafsah yasa suka cika gidan da hayaniya.
Ya Nazeer, shima da tashi hayaniyar ya fara musu magana, "Haba cai cai cai cai, kun dawo ai."
Mama ce ta fito itama, lokacin Fateema na tambayar Hafsah.
Amma dai kwana zakiyi koh."?
Mama ta cafe, "Ai Hafsah nan da sati biyu ma tana nan."
Wani murmushi Nazeer yayi, "Kice mun qaru a gidan."
Mama, tace sosai ma, ai kasan tayi candy fah."
Ya qara yin murmushi "Allah Mama."?
Sannan ya kalli Hafsah, sam bashi take kallo, ba. "Congratulations sister."
"Thank you."
Tace mishi nan aka barke da hira.
Mama ta kalle su, zan d`an fita.
"Fateema, Hafsah ku kula da gidan."
"To mama a dawo lpia."
"Tare Mama suka fice, ita da Nazeer don shi zai driving dinta.
Fateema taja Hafsah d`akin ta suka kule suna hirar Yaushe gamo."
Har dare mama bata dawo ba, sun gaji da hira sun dawo palour, suna kallo.
Sai can maman tayi sallama ita da Nazeer da kayi niqi niqi irin na amfanin gida.
Mama kenan _mace me kamar mazaa_, a kalla zatayi shekara Arba'in da biyar.
Mijin ta Alhaji Dalhatu ya rasu shekaru uku kenan da suka wuce, ya barta da yara biyar, uku mata biyu mazaa.
To kasancewar a gajiye maman ta dawo bata samu zaman hira sosai da su Hafsah ba, taje ta kwanta babu jimawa bacci ya d`auke ta.
♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so (Guba ne)*
💔💔
*By*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Khareemerh)*
*Dedicated to unique in your love heart*
📄 *38*
*Zaman* ta gidan Maman Ya Nazeer, zama ne da zata iya fassara shi da "Zaman qaruwa da qarin ilimi tare da samun experience akan rayuwa.
Zama ne wanda bata samu takura ba sam a yayinsa, sai ma tattalinta da aka dinga yi sam baa son kukanta.
Idan Hafsah zatayi lissafin mutane muhimmai wad`anda suka taka rawa a rayuwarta to tabbas daga abbanta, sai mamanta sai kuma yayar mahaifiyarta wato maman Ya Nazeer, kamar yadda suke karanta..
Bawai don sun dauki tsahon lokaci tare ba, a,a sai dai taimakon da ta bata na tsahon wata uku kacal, amma shine zatace ya tallafi rayuwarta har kawo yanzu, wanda badon ita ba da tuni ta zama wata abu ta daban ba Hafsar da take ayanzu ba."
To dama hakane, wad`ansu mutanen suna da irin wannan baiwar, wad`anda zama kad`an zakayi amma ka qaru da abinda zai tallafe ka har qarshen rayuwa.
Maman ya Nazeer, ta jata a jiki, ta dawo da ita hayyacinta lokacin da ta fita daga cikin shi, ta nuna mata cewa tana da da ma lokacin da tayi losing duk wai hope nata, _she lost hope and she's completely broke._
Bata taba tunanin zata iya rayuwar da babu Yusuf cikinta ba, sai gashi maman ta nuna mata cewa zata iya kuma ta koyar da ita yadda zata iya d`in, kuma gashi ta iya d`in.
Dole ne ta gode mata bisa wannan d`au ki data kawo mata cikin rayuwa wanda bata da abinda zata saka mata dashi banda addu,a.
Shiyasa wani lokacin Hafsan, ke tuhumar kanta da laifin _butulci_ na bujerewa Soyayyar Gudan jinin matar da ta tallafi rayuwarta.
Amma takanji sassauci idan ta tuna cewar kai tsaye, Maman bata da masaniya bisa hakan sai dai hasashe, kuma baza,a iya cewa tak`i Nazeer kai tsaye bane, sai dai ace tak`i bada fuska gareshi yadda zai shigar da buk`atar sa, har ya gaji ya haqurar wa zuciyarshi.
Ahankali take tuno abinda ya faru.
#TUNANIN #BAYA
Wato bayan isar su gidan ita da Mama a wancan lokacin sun isa gidan babu kowa cikin sa, kasancewar yaran sun tafi makaranta.
Driver ne ya shigo mata da kayanta, inda Maman ta nuna mata wani dak`i mallakin yarta Fatima tace "Kai kayan naki wancan dakin."
Ta miqe a hankali, ta ja trolley din ta nufi d`akin.
Sun yini su biyu ita da maman cikin nishad`i har Maman ta sa ta tayi musu girki, sai wajen qarfe biyu da rabi sannan yaran gidan suka fara dawowa.
Da farko Nazeer ne ya shigo wanda shine babban d`a a gidan, sai fateema mai binshi, sai Al,ameen, sai Nour, sai Siddiqa.
Hafsah ce kadai a palourn ta qurawa TV ido, Ahankali yayi sallama, da takarda a hannunshi ta dago kai ta kalli mai shigowa, ta amsa sallamar, sannan ta kauda kan ta.
Murmushishi ya fad`ad`a, "Hafsy ce yau a gidan namu."?
Tayi murmushi, Nice "Ya Nazeer ina wuni."? Ta gaidashi tana mai dan duk`awa daga kujerar da take.
Ya sakar mata murmushi sosai, yarinyar akwai tarbiyya ga Ladabi, lpia lau, Hafsah, ya mama Ina su zainab"?
"Suna lpia lau."
Ya qara kallon ta.
"Ina Mama nah"?
Ta kalleshi so take ya qara bayani ko zata fahimci zancen, wacce maman yake nufi.
Taji abinne banbarakwai babba dashi yana cewa Mamanshi.
"Ina Mamy nah nace."?
"Uhum. Maman ku."?
Yayi `yar dariya.
"Yes, mamy nah, ai mamie tawa ce ni kad`ai k`wace min akayi aka min rubdugu."
Hafsah bata ankara ba sai jinta tayi tana k`yak`yata dariya, a zuciyarta tana cewa dama haka Ya Naseer din yake da hira.?
Ta sani dai yana zuwa gidansu, amma bai fiya jimawa haka ba, kuma ita bata cika zuwa gidansu ta kwana ba, idan ma tazo yawanci yana school.
Dariyar su Mama ta jiyo ta fito zuwa a palourn. "Oh dama nasani ai sai kai."
Ta fad`a tana kallon Nazeer d`in.
Yayi kanshi mazauni a kujera kafin yace a shagwab`e Mama wai Taraba suka tura ni."
"Taraba"?
Mama ta maimaita,
Kuma kana so."?
Ya girgiza kai, gaskiya A,a Mama nafison koda jigawa neh."
Okay zanyi yiwa sunusi magana, tana nufin qaninta wanda shi maman su Hafsah ke bi."
"Okay mamy na Nagode."
"Mamy yunwa nakeji." ya fada yana dan shafa ciki."
Sannan ya miqe ya nufi, Kofar fita daga palourn domin dakinshi yana daga waje ne.
Mama ta bishi da kallo, sannan ta kalli Hafsah.
"Ikon Allah kinga ya fice, tashi ki zuba mishi abincin kafin ya dawo kinji."?
Toh Mama ta miqe ta nufi kitchen din.
Plask ta samu guda biyu, ta zuba abinci a babban dayan kuma tasa miya, sannan ta shirya komai kan tray, lokacin data fito Maman bata palourn kawai sai ta ajye akan dinning, kusan minti uku bai dawo ba, sai ta jiyo muryar Mama nacewa, "Hafsah ki miqa mishi abincin kinji don da kyar idan zai dawo.
"To, kawai tace, ta kinkimi tray din tayi dakin shi.
Ad`an ka re taga k`ofar don haka tura wa kawai tayi ta shiga da sallama.
Daga cikin wani daki a dan palourn ta jiyo an amsa inda ya fito ya tarar da ita da kayan tray a hannu, aiko yace me zaiyi idan ba dariya ba.
Ya k`ame yana kallonta yana ta qyaqyata dariya yana nuna ta har Hafsah ta tsorata.
Sannan ya gimtse ya fara magana, cike da shaqiyanci,
"La-la-la-la, gaskiya kina so mama ta zane ni kenan.
ta kalleshi ad`an tsorace sannan ta qara kallon tray d`in.
Ya sa Hannu ya amshi tray d`in ya ajye sannan ya cigaba da magana k`asa-k`asa.
"Wa yace miki anan Mama ke zuba min abinci."?
"Ai Matsayina bai wuce wannan ba."
Ya d`auki plate daga kan tray d`in yana nuna mata.
"Anan ake zuba min abinci kin manta bani ne mai gidan ba." Ya Qarashe zancen yana zaro idanunshi.
D`an murmushi tayi a qagauce, saboda gaba d`aya ji take kamar akan qaya take.
"Bata saba ba sam, ace wai gata ga wani namiji, tsaye irin haka daga ita sai shi, idan aka cire Yusuf, da shi kuma ta bashi wani Matsayi na daban.
Bata da yayye maza, sannan ba wasu mazaa ke shigo musu gida ba har su sami damar hira dasu, idan ka d`auke auncle Abdullah, sai shi Nazeer d`in, sai wad`and`a ba,a rasa ba cikin `ya`yan `yan uwa suma kuma jefi-jefi ne. Su a familynsu ma mata sunfi yawa.
Sannan bata son maman ya Nazeer, taga ta dad`e, don haka ta motsa K`afarta da niyyar juyawa ta tafi amma sai ya katse mata hanzari da cewa.
"Ni al,majiri ne a gidan." Ya fad`a da marainiyar murya.
"Please zubamin, a plate sai ki tafi da sauran."
Ranta bai so hakan ba amma bata da zab`i tana bashi girma a matsayinshi na Yayansu.
Ta tsuguna, da sauri sauri, take zubawa, ta cika plate d`in.
"Kaii ai bazan cinye ba rage min."
Ta kwashe wajen kwatar (quarter) abincin.
"Yawwa ko kefa."
bata ce komi ba tasa mishi miya da nama tasa mishi salad.
Sannan ta d`auke ruwan da ke kan tray d`in ta ajye mishi sannan ta d`auki tray d`in.
Tana lura da kafe ta da Ido da yayi.
"Thank you Qanwaty!
Taji ya fad`a
Bata ce komai ba ta juya tana sak`e sak`e a ranta.
_"Anya kuwa zata yarda, tayi koda kwana uku ne agidan nan bare kuma sati, matuqar za,a dinga zata ayyukan hidima irin wad`annan."??_
📝
*HAJEEYA KHAREEMERH*
♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so (Guba ne)*
💔💔
*By*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Khareemerh)*
*Dedicated to unique in your love heart*
📄 *39*
*Tana* komawa palour, fateema ta shigo ita ma da sallama, Hafsah ta amsa cike da farin cikin ganinta.
Itama da gudu ta qaraso ta rungume Hafsah tana murna da ganinta.
"Hafsy yau kece a Gidan namu."?
Hafsah tayi murmushi ita ma, Nice wallah auntie Fateema."
Fateema ta sake ta tana fad`in "Gaskiya naji dadie."
A palourn suka zauna suna hira, Fateema ta miqe taje ta zubo abinci ta dawo tana fad`in.
"Wata irin yunwa nakeji wallah."
"Sannunki.!!"
Hafsah ta fad`a tana qara kallonta.
"Level 3 kike koh auntie."?
( _Da ke ta girmi Hafsah da wajen shekaru uku._)
Eh, wata test mukayi mai zafi wallah."
Ta fad`a tana kai lomar abinci bakinta.
"Ke fa, kinyi candy kema koh."?
"Eh result nake jira."
To Allah ya bada sa,a.
"Amin."
Suna hirar, Ya nazeer ya qara shigowa, kamar tare suka shigo shida ragowar yaran gidan. Wad`anda murnar ganin Hafsah yasa suka cika gidan da hayaniya.
Ya Nazeer, shima da tashi hayaniyar ya fara musu magana, "Haba cai cai cai cai, kun dawo ai."
Mama ce ta fito itama, lokacin Fateema na tambayar Hafsah.
Amma dai kwana zakiyi koh."?
Mama ta cafe, "Ai Hafsah nan da sati biyu ma tana nan."
Wani murmushi Nazeer yayi, "Kice mun qaru a gidan."
Mama, tace sosai ma, ai kasan tayi candy fah."
Ya qara yin murmushi "Allah Mama."?
Sannan ya kalli Hafsah, sam bashi take kallo, ba. "Congratulations sister."
"Thank you."
Tace mishi nan aka barke da hira.
Mama ta kalle su, zan d`an fita.
"Fateema, Hafsah ku kula da gidan."
"To mama a dawo lpia."
"Tare Mama suka fice, ita da Nazeer don shi zai driving dinta.
Fateema taja Hafsah d`akin ta suka kule suna hirar Yaushe gamo."
Har dare mama bata dawo ba, sun gaji da hira sun dawo palour, suna kallo.
Sai can maman tayi sallama ita da Nazeer da kayi niqi niqi irin na amfanin gida.
Mama kenan _mace me kamar mazaa_, a kalla zatayi shekara Arba'in da biyar.
Mijin ta Alhaji Dalhatu ya rasu shekaru uku kenan da suka wuce, ya barta da yara biyar, uku mata biyu mazaa.
To kasancewar a gajiye maman ta dawo bata samu zaman hira sosai da su Hafsah ba, taje ta kwanta babu jimawa bacci ya d`auke ta.