Sashe 43
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da daren Hafsah suna kwance a d`akin Fateema, Hafsan tai jugum tana tunanin Basma da Yusuf. Su suna can suna jin dadin rayuwar su ita kuma sun barta nan cikin k`uncin zuciya.
"Aunty Fatee, Don Allah ara min wayarki."
Hafsah ta miqe kamar an tsikare ta tare da fad`in hakan.
"Okey ungo."
Fateema ta miqa mata wayar.
Hafsah ta zana number Yusuf a ciki sannan tayi saving. Kafin tace, "So nake kawai naga mai number d`innan a online."
"Hira zakuyi"?
Cewar Fateema.
Hafsah ta girgiza kai, "Aa dai kawai sa number zanyi, idan lokacin da za,ayi magana yayi zan miki magana.
"Tom."
Inji fateema.
Ai kuwa sai ga photon, shi a profile.
"Aa wannan ne me number."?
Fateema ta tambaya cikin zumud`i.
Hmm kawai Hafsah ta fad`a ta kafe photon da ido zuciyarta fal da bak`in ciki yaya ma za,ayi tayi sakacin da zata barwa Basma Yusuf, ai impossible.
"Gaskiya ya hadu fah."
Cewar Fateema, wacce fad`in hakan ya qara tun zira, Hafsah. Sai kawai ta miqa mata wayar ta kwanta cike da tashin hankali.
Dole ta nemi mafita, kuma ta tashi tsaye, tunda ana nema afi k`arfinta.
Wani abu ya maqale mata a mok`ogoro, zuciyarta ke wassafo mata basma, da irin rainin da tayi mata har yasa ta mata _Snatching_ mafi muni.
A kullum ta tuna bak`in ciki ne ke qara cika mata zuciya had`i da wata qiyayyar basma mara misaltuwa, bata taba jin ta tsani wani ba sai a kanta.
Nunkuwar tsanar kuma yana da alaqa da rashin samun damar daukar fansa _revenge_ ko yaya neh." Shiyasa abin ya tsaya mata arai, data tuna bata da wata dama fa. Kawai sai ta fashe da wani kuka me cin rai."
Fateema ma na cikin qarewa photon kallo kafin tabi Hafsah da kallo cikin mamaki, da damuwa, gaskiya akwai abinda ke damunta.
Cikin in,ina take fad`in "Ha.. Hafsah me menene."? Me akayi miki don Allah kiyi shuru.
Kukan take sosai ko zata sami relief.
Fateema tayi cilli da wayar ta matso kusa da ita tana lallashinta.
"Kiyi hakuri don Allah, me aka miki ko nice."?
Hafsah ta girgiza kai.
Mama ce."?
Nan ma ta girgiza kai.
Ya Nazeer ne."? Shima ta girgiza kai.
Sai da ta tambayeta
kowa na gidan amma tace babu kowa.
To wanene."?
Fateema an cuce ni, anzalince ni.!"
Ta kuma rushe wa da kuka.
Hakan ya qara rud`a
Fateema.
To wanene Hafsah kodai in kira mama ne."? Ta fada tana qoqarin miqewa.
Hafsah ta ruqo ta.
Cikin kuka tace, kada ki fada mata don Allah ki kyaleni kawai nina san abinda aka min."
"To ki daina kuka, ki fad`amin menene, ko kuma in kirata."
Da kyar dai Fateema ta samu Hafsah tayi shuri amma fir tak`i fad`a mata komai sai ajiyar zuciya take. "Ki bari kawai, take iya ce mata.
A haka sukayi bacci, wanda ga Hafsah ba bacci ne kad`ai ba, bacci ne me cike da mafarkai, na Yusuf da Basma, marasa dad`i.
Da safe Fateema, tayi shirin makaranta, dukan su na palour banda Hafsah da take ta bacci.
Fateema taso fad`awa mama as abinda Hafsah tayi da dare amma tana sauri.
Sai da yamma bayan ta dawo suna zaune ana hira kawai mama, ta tashi ta shige d`aki, minti kad`an kuma sai ta k`wallowa Fateema kira.
Fateema ta miqe ta bita d`akin.
"Ina son dama inja miki kunne tun jiya sai kuma na manta."
Maganar da mama ta fara da ita kenan.
Bbu shiri Fateema ta tattara dukkanin nutsuwar ta ga Maman.
Mama ta d`ora, "Koda wasa kada ki sake ki ara wa Hafsah wayarki ta kira wani, saura kuma kiyi sakaci ta d`auka."
Dam! gaban Fateema ya fad`i jin wata doka mai tsauri irin ta mama.
Anya ta sanar da ita gaskiya kuwa, cewa Hafsah ta riga da ta ari waya."?
Bare har ta fad`a mata zancen Kukan da Hafsan tasha jiya.
Idan hakane da akwai alamar tambaya kenan game da zuwan Hafsah gidansu, dama abin ya bata mamaki, don Hafsah bata wuce kwana d`aya a gidansu amma wannan zuwa na bazata, don mama sam bata musu zancen zuwan hafs
Idan haka ne Akwai abinda ya faru.
Don haka ta yanko tambaya tare da d`agowa don yiwa maman amma sai ta d`aga mata hannu.
📝
*HAJEEYAH KHAREEMERH*
♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Masoyin kwarai)
*Cigaban littafin Zazzafan so.*
*(Guba ne )*
💔💔
*By:*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah khareemerh)*
*Dedicated to Unique in your love heart group members.*
📄 *40*
*Kada* ki tambayeni komai."
Kawai ki bi abinda nace.
"To mama."
Fateema ta amsa cikin ladabi.
Tashi kije ki turo min Hafsan.
To mama.
Ta miqe ta fita, ta sanar da Hafsah kiran mama.
Ta shigo cikin nutsuwa, doguwar riga ce a jikinta ta atampha.
Ta durk'usa a gaban maman.
Mama gani.
Hajiya Nafeesa ta fad`ad`a fara,arta sosai.
"Hafsa na. Ya naga duk kin fad`a"?
Bata jira amsarta ba tace, "Ki saki jikinki kinji kuma ki daina sa damuwa a ranki.
Sannan ta qara kallonta, "Ai babu wanda yake takura miki a gidan nan koh."?
Hafsah ta girgiza kai da sauri. "Aa mama babu kowa."
Tayi murmushi, Yawwa idan ma akwai ki fada min duk wanda kika ga yana damunki ko da kuwa Nazeer ne."
Mama ta qarashe zancen tana dariya Hafsah ma dariya tayi.
So Maman take Hafsah ta saki jikinta da ita tana so ne ta saba hira da ita sosai a haka har ta saki jiki ta fada mata damuwar ta."
Tana son ta gano Menene matsalar ta ita da yaron.
"Ki bani labarin makarantar ku kinji Hafsah."?
Hafsah tayi d`an
Murmushin jin kunya.
Ko bazaki bani ba"? "Ba mamanku tace ke kike daukar 1st position ba ko ba haka bane."?
_Duk cikin sigar wasa take mata tambayoyin._
Hafsah ta d`aga kai.
"Gud girl.!!.
baki tab`a zuwa ko ta biyu bane."?
Ta girgiza kai.
"Kin taba zuwa."?
um, sau nawa sau biyu."
Na uku fa."?
Aa.
"To na hudu fah."?
Nan ma Hafsah ta girgiza kai.
Mama tana dariya tace "To sai na biyar."?
_Tana sane tayi mata tambayar don maman Hafsah ta fada mata komai._
Sai Hafsah taji kunya ta shiga boye fuskar ta cikin cinyoyi."
"Ahh, Hafsa kice kin taba zuwa ta biyar d`in."
"To garin yaya."?
Shuru babu amsa.
"Wasa kika tsaya."?
Nan ma shuru.
"Ki d`ago me yasa kike jin kunya."?
Hafsah ta dago tana noqe-noqe.
Kinaji nah."?
Ta d`aga kai.
"Ki daina yin abinda zaki zo kiji kunya, ko kizo kiyi dana sani."
_"Kinga yanzu kin bata record d'inki."_
"Kin ga da tuni, idan kina bawa Yaranki ('ya'yanki) labari, _you claim and proud that_ baki tab'a tsallake na biyu ba koh."? Amma yanzu kin bata abin."
Mama ta fada da muryar nuna damuwa.
Ran Hafsah ya cika da kishin abin, _Tabbas ta tafka asara ba komai bane kuma sai don dalilin biye wa basma da son farin cikin ganin Yusuf._
A hankali idonta ya cika da kwalla ganin sam bata ribaci hakan ba illa bata record dinta da sukayi kamar yadda mama ta fad'a.
Mama ta lura da kwallar, duk da Hafsah taki barin ta ta zuba.
A hankali ta girgiza kai tace, "Me abbanku yace miki a time d`in daya ga result d`in.
A kunyace tace, "Yayi min fad'a yace kada na sake sakacin yin hakan."
"To Ke me yasa kikayi hakan Uhum."?
"Kina tunanin wani abu neh."?
Hafsah ta girgiza kai.
"To menene.. fad`amin me yasa kakai failing a lokacin."
Ta qara yin shuru.
"Wasa kuke koh.? Kin chanja qawaye koh, kuna zaman hira."
Gaban Hafsah ya fad'i, ya akayi Maman ya Nazeer take neman baro jirginta."??
"Kinyi shuru Ko ba haka bane."?
Bata da amsa, sai kawai maman ta bar zancen ta shiga wani.
Me yasa kike batawa mamanki rai."?
A hankali ta girgiza kai, "babu komai.
Babu komai amma kike yin abinda bata so."?
Idan mama ta lura fuskar Hafsah tayi rauni lokacin.
"Me yasa kike fita bada saninta ba."?
Duk Cikin qasa da murya maman take magana.
"To rannan ina kukaje ke da qawarki."?
Gaban Hafsah ya fad'i, wannan fita ta zame mata jaraba. Sam ta tsani a tambaye ta ina taje."
Bayan inda taje d`in ba alkhairi ta ganowa kanta ba.
Ehe."? _Inji mama jin tayi shuru._
"Asibiti mukaje dubiya."
Wanne asibitin."?
Uhum.. A ina yake."?
_Hafsah bata iya qarya ba don haka ta kasa qirqiro amsa._
"Kin sami babu kyau sabawa iyayen koh."?
Tame daga kai.
To ki daina yin abinda zai b'atawa mama da Abba rai kinji.
"Tom."
_Ta fad'ad'a murmushi._
"Yawwa hafsy, gobe zaki raka ni wajen gyaran jiki na."
Ko Bakya son muje."?
Hafsah taji dad`in hakan sosai don haka cikin fara,a tace "Inaso mama."
"Yawwa jeki wajen su fateemah kuyi hira."
_Ta miqe ta fita mama ta bita da kallo._
Da daddare suna zaune suna kallo, Nazeer ya shigo ya zauna cikin su.
Abinda Mama ta lura dashi shine, kwana biyu Nazeer nason ya zauna cikin su ya dad'e musamman da daddare.
_Bata raya komai aranta ba._
A gurin Hafsah kuwa zaman nashi takura ce a wajenta. _Domin indai ya zauna sai ya tsokane ta, ko yayi ta janta da hira. Gashi tunda tazo gidan duk wata hidimar shi ita yake sakawa, Kama daga zuba mishi abincin, d`akkon kaza-da-kaza._
Amma banda haka tanajin dad`in zaman gidan sosai da sosai banda damuwar dake cikin ranta.
Yanzu ba yusuf ne kad'ai damuwarta ba, a,a harda damuwar Basma, so take ta d`auki fansar abinda tayi mata ko dan ta rage damuwar abin aranta.
_Da Wannan alwashin, ta kwana a ranta._
Gefe guda tana jin takaicin ledar kyautar ta da ke wajen maman Ya Nazeer, damuwar ta wayar dake ciki, da tana wajenta tabbas sai ta yi amfani da wayar ko mai zai faru kuwa, sai ta kira Basma ta huce fushinta akan ta.
Ita da zata ganta ma babu abinda zai hana ta illatata.
Ta rasa me ya hanata d'aukar mataki a lokacin. Ko kuma lokacin bata da kwarin guiwar yin hakan. Saboda taga abinda zuciyar ta bata tab`a wassafo mata faruwar abu mai kama da hakan ba.
Tayi kwafa, yayin da Fateema dake karatu, ta bi inda take kwance da kallo, sam ta zaci Hafsah bacci take.
Washegari da safe tun wajen qarfe 11:00 na rana, Hafsah ta shirya ita da Mama suka fice zuwa wajen gyaran jikin Maman.
"Aunty Fatee, Don Allah ara min wayarki."
Hafsah ta miqe kamar an tsikare ta tare da fad`in hakan.
"Okey ungo."
Fateema ta miqa mata wayar.
Hafsah ta zana number Yusuf a ciki sannan tayi saving. Kafin tace, "So nake kawai naga mai number d`innan a online."
"Hira zakuyi"?
Cewar Fateema.
Hafsah ta girgiza kai, "Aa dai kawai sa number zanyi, idan lokacin da za,ayi magana yayi zan miki magana.
"Tom."
Inji fateema.
Ai kuwa sai ga photon, shi a profile.
"Aa wannan ne me number."?
Fateema ta tambaya cikin zumud`i.
Hmm kawai Hafsah ta fad`a ta kafe photon da ido zuciyarta fal da bak`in ciki yaya ma za,ayi tayi sakacin da zata barwa Basma Yusuf, ai impossible.
"Gaskiya ya hadu fah."
Cewar Fateema, wacce fad`in hakan ya qara tun zira, Hafsah. Sai kawai ta miqa mata wayar ta kwanta cike da tashin hankali.
Dole ta nemi mafita, kuma ta tashi tsaye, tunda ana nema afi k`arfinta.
Wani abu ya maqale mata a mok`ogoro, zuciyarta ke wassafo mata basma, da irin rainin da tayi mata har yasa ta mata _Snatching_ mafi muni.
A kullum ta tuna bak`in ciki ne ke qara cika mata zuciya had`i da wata qiyayyar basma mara misaltuwa, bata taba jin ta tsani wani ba sai a kanta.
Nunkuwar tsanar kuma yana da alaqa da rashin samun damar daukar fansa _revenge_ ko yaya neh." Shiyasa abin ya tsaya mata arai, data tuna bata da wata dama fa. Kawai sai ta fashe da wani kuka me cin rai."
Fateema ma na cikin qarewa photon kallo kafin tabi Hafsah da kallo cikin mamaki, da damuwa, gaskiya akwai abinda ke damunta.
Cikin in,ina take fad`in "Ha.. Hafsah me menene."? Me akayi miki don Allah kiyi shuru.
Kukan take sosai ko zata sami relief.
Fateema tayi cilli da wayar ta matso kusa da ita tana lallashinta.
"Kiyi hakuri don Allah, me aka miki ko nice."?
Hafsah ta girgiza kai.
Mama ce."?
Nan ma ta girgiza kai.
Ya Nazeer ne."? Shima ta girgiza kai.
Sai da ta tambayeta
kowa na gidan amma tace babu kowa.
To wanene."?
Fateema an cuce ni, anzalince ni.!"
Ta kuma rushe wa da kuka.
Hakan ya qara rud`a
Fateema.
To wanene Hafsah kodai in kira mama ne."? Ta fada tana qoqarin miqewa.
Hafsah ta ruqo ta.
Cikin kuka tace, kada ki fada mata don Allah ki kyaleni kawai nina san abinda aka min."
"To ki daina kuka, ki fad`amin menene, ko kuma in kirata."
Da kyar dai Fateema ta samu Hafsah tayi shuri amma fir tak`i fad`a mata komai sai ajiyar zuciya take. "Ki bari kawai, take iya ce mata.
A haka sukayi bacci, wanda ga Hafsah ba bacci ne kad`ai ba, bacci ne me cike da mafarkai, na Yusuf da Basma, marasa dad`i.
Da safe Fateema, tayi shirin makaranta, dukan su na palour banda Hafsah da take ta bacci.
Fateema taso fad`awa mama as abinda Hafsah tayi da dare amma tana sauri.
Sai da yamma bayan ta dawo suna zaune ana hira kawai mama, ta tashi ta shige d`aki, minti kad`an kuma sai ta k`wallowa Fateema kira.
Fateema ta miqe ta bita d`akin.
"Ina son dama inja miki kunne tun jiya sai kuma na manta."
Maganar da mama ta fara da ita kenan.
Bbu shiri Fateema ta tattara dukkanin nutsuwar ta ga Maman.
Mama ta d`ora, "Koda wasa kada ki sake ki ara wa Hafsah wayarki ta kira wani, saura kuma kiyi sakaci ta d`auka."
Dam! gaban Fateema ya fad`i jin wata doka mai tsauri irin ta mama.
Anya ta sanar da ita gaskiya kuwa, cewa Hafsah ta riga da ta ari waya."?
Bare har ta fad`a mata zancen Kukan da Hafsan tasha jiya.
Idan hakane da akwai alamar tambaya kenan game da zuwan Hafsah gidansu, dama abin ya bata mamaki, don Hafsah bata wuce kwana d`aya a gidansu amma wannan zuwa na bazata, don mama sam bata musu zancen zuwan hafs
Idan haka ne Akwai abinda ya faru.
Don haka ta yanko tambaya tare da d`agowa don yiwa maman amma sai ta d`aga mata hannu.
📝
*HAJEEYAH KHAREEMERH*
♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Masoyin kwarai)
*Cigaban littafin Zazzafan so.*
*(Guba ne )*
💔💔
*By:*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah khareemerh)*
*Dedicated to Unique in your love heart group members.*
📄 *40*
*Kada* ki tambayeni komai."
Kawai ki bi abinda nace.
"To mama."
Fateema ta amsa cikin ladabi.
Tashi kije ki turo min Hafsan.
To mama.
Ta miqe ta fita, ta sanar da Hafsah kiran mama.
Ta shigo cikin nutsuwa, doguwar riga ce a jikinta ta atampha.
Ta durk'usa a gaban maman.
Mama gani.
Hajiya Nafeesa ta fad`ad`a fara,arta sosai.
"Hafsa na. Ya naga duk kin fad`a"?
Bata jira amsarta ba tace, "Ki saki jikinki kinji kuma ki daina sa damuwa a ranki.
Sannan ta qara kallonta, "Ai babu wanda yake takura miki a gidan nan koh."?
Hafsah ta girgiza kai da sauri. "Aa mama babu kowa."
Tayi murmushi, Yawwa idan ma akwai ki fada min duk wanda kika ga yana damunki ko da kuwa Nazeer ne."
Mama ta qarashe zancen tana dariya Hafsah ma dariya tayi.
So Maman take Hafsah ta saki jikinta da ita tana so ne ta saba hira da ita sosai a haka har ta saki jiki ta fada mata damuwar ta."
Tana son ta gano Menene matsalar ta ita da yaron.
"Ki bani labarin makarantar ku kinji Hafsah."?
Hafsah tayi d`an
Murmushin jin kunya.
Ko bazaki bani ba"? "Ba mamanku tace ke kike daukar 1st position ba ko ba haka bane."?
_Duk cikin sigar wasa take mata tambayoyin._
Hafsah ta d`aga kai.
"Gud girl.!!.
baki tab`a zuwa ko ta biyu bane."?
Ta girgiza kai.
"Kin taba zuwa."?
um, sau nawa sau biyu."
Na uku fa."?
Aa.
"To na hudu fah."?
Nan ma Hafsah ta girgiza kai.
Mama tana dariya tace "To sai na biyar."?
_Tana sane tayi mata tambayar don maman Hafsah ta fada mata komai._
Sai Hafsah taji kunya ta shiga boye fuskar ta cikin cinyoyi."
"Ahh, Hafsa kice kin taba zuwa ta biyar d`in."
"To garin yaya."?
Shuru babu amsa.
"Wasa kika tsaya."?
Nan ma shuru.
"Ki d`ago me yasa kike jin kunya."?
Hafsah ta dago tana noqe-noqe.
Kinaji nah."?
Ta d`aga kai.
"Ki daina yin abinda zaki zo kiji kunya, ko kizo kiyi dana sani."
_"Kinga yanzu kin bata record d'inki."_
"Kin ga da tuni, idan kina bawa Yaranki ('ya'yanki) labari, _you claim and proud that_ baki tab'a tsallake na biyu ba koh."? Amma yanzu kin bata abin."
Mama ta fada da muryar nuna damuwa.
Ran Hafsah ya cika da kishin abin, _Tabbas ta tafka asara ba komai bane kuma sai don dalilin biye wa basma da son farin cikin ganin Yusuf._
A hankali idonta ya cika da kwalla ganin sam bata ribaci hakan ba illa bata record dinta da sukayi kamar yadda mama ta fad'a.
Mama ta lura da kwallar, duk da Hafsah taki barin ta ta zuba.
A hankali ta girgiza kai tace, "Me abbanku yace miki a time d`in daya ga result d`in.
A kunyace tace, "Yayi min fad'a yace kada na sake sakacin yin hakan."
"To Ke me yasa kikayi hakan Uhum."?
"Kina tunanin wani abu neh."?
Hafsah ta girgiza kai.
"To menene.. fad`amin me yasa kakai failing a lokacin."
Ta qara yin shuru.
"Wasa kuke koh.? Kin chanja qawaye koh, kuna zaman hira."
Gaban Hafsah ya fad'i, ya akayi Maman ya Nazeer take neman baro jirginta."??
"Kinyi shuru Ko ba haka bane."?
Bata da amsa, sai kawai maman ta bar zancen ta shiga wani.
Me yasa kike batawa mamanki rai."?
A hankali ta girgiza kai, "babu komai.
Babu komai amma kike yin abinda bata so."?
Idan mama ta lura fuskar Hafsah tayi rauni lokacin.
"Me yasa kike fita bada saninta ba."?
Duk Cikin qasa da murya maman take magana.
"To rannan ina kukaje ke da qawarki."?
Gaban Hafsah ya fad'i, wannan fita ta zame mata jaraba. Sam ta tsani a tambaye ta ina taje."
Bayan inda taje d`in ba alkhairi ta ganowa kanta ba.
Ehe."? _Inji mama jin tayi shuru._
"Asibiti mukaje dubiya."
Wanne asibitin."?
Uhum.. A ina yake."?
_Hafsah bata iya qarya ba don haka ta kasa qirqiro amsa._
"Kin sami babu kyau sabawa iyayen koh."?
Tame daga kai.
To ki daina yin abinda zai b'atawa mama da Abba rai kinji.
"Tom."
_Ta fad'ad'a murmushi._
"Yawwa hafsy, gobe zaki raka ni wajen gyaran jiki na."
Ko Bakya son muje."?
Hafsah taji dad`in hakan sosai don haka cikin fara,a tace "Inaso mama."
"Yawwa jeki wajen su fateemah kuyi hira."
_Ta miqe ta fita mama ta bita da kallo._
Da daddare suna zaune suna kallo, Nazeer ya shigo ya zauna cikin su.
Abinda Mama ta lura dashi shine, kwana biyu Nazeer nason ya zauna cikin su ya dad'e musamman da daddare.
_Bata raya komai aranta ba._
A gurin Hafsah kuwa zaman nashi takura ce a wajenta. _Domin indai ya zauna sai ya tsokane ta, ko yayi ta janta da hira. Gashi tunda tazo gidan duk wata hidimar shi ita yake sakawa, Kama daga zuba mishi abincin, d`akkon kaza-da-kaza._
Amma banda haka tanajin dad`in zaman gidan sosai da sosai banda damuwar dake cikin ranta.
Yanzu ba yusuf ne kad'ai damuwarta ba, a,a harda damuwar Basma, so take ta d`auki fansar abinda tayi mata ko dan ta rage damuwar abin aranta.
_Da Wannan alwashin, ta kwana a ranta._
Gefe guda tana jin takaicin ledar kyautar ta da ke wajen maman Ya Nazeer, damuwar ta wayar dake ciki, da tana wajenta tabbas sai ta yi amfani da wayar ko mai zai faru kuwa, sai ta kira Basma ta huce fushinta akan ta.
Ita da zata ganta ma babu abinda zai hana ta illatata.
Ta rasa me ya hanata d'aukar mataki a lokacin. Ko kuma lokacin bata da kwarin guiwar yin hakan. Saboda taga abinda zuciyar ta bata tab`a wassafo mata faruwar abu mai kama da hakan ba.
Tayi kwafa, yayin da Fateema dake karatu, ta bi inda take kwance da kallo, sam ta zaci Hafsah bacci take.
Washegari da safe tun wajen qarfe 11:00 na rana, Hafsah ta shirya ita da Mama suka fice zuwa wajen gyaran jikin Maman.