Sashe 83
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Amma sai kuma tayi saurin ture wannan tunanin bisa wata ankararwa da wani bangare na zuciyar ta yayi mata.
_Hafsah kada kiyiwa Allah butulci hak'ika rayuwarki gaba-taci ba baya ba. Kuma yanzu you're engaged kin yiwa Yusuf nisa._
Ta daga kanta ta kalleshi ya kuwa k'ura mata ido kallon ta na tuno mishi abubuwa da dama.
Me ya kawo ka wajena."?
Ta fad'a da kaushin murya.
Bani da hanyar contacting dinki ina miki magana kina share ni kiyi hakuri, na zo ne na baki hak'uri... ya d'anyi shuru kafin yace _and to tell you that my father had died._
Tayi jimm sai yanxu taji d'an tausayin shi saboda a yadda tasan Yusuf da yadda yakeson iyayenshi kuma suma suke son shi.
"Ahankali tace Allah ya jik'anshi."
Yayi wani bushashshen murmurshi ta kuma lura da kwallar data taru a idanunshi.
"Amiin ya amsa sannan ya dora cikin sanyin muryar.
Please Hafsah ki yarda muyi aure mana wallahi na daina duk.."
Ta daga mishi hannu cike da b'acin rai.
Nooo never.!! Kada ka kara mini wannan zancen and kada ka kara zuwa wajena.."
Tana shirin juyawa gida taji cikin daga sauti yace...
Don Allah ki taimakeni Nasan kina sona fah Basma ne ta rabamu kuma nayi regret abinda ya faru..please Hafsah I lost my dad kada na rasa ki kema.."
Ga mamakin ta sai taga yana share hawaye ta tsaya jimm cikin takaicin abubuwan wacce kaddara ce ma tasa ya dawo gareta..ita ta manta dashi ta manta duk wata rayuwar da sukayi a baya imma dad'in ta da wahalar ta duk ta manta. To kuma me zaisa ya dawo mata da wannan zancen gani takeyi ma k'arya yake lokacin yayi tsaho ace da ragowar son ta a zuciyar shi..
Ko ita da tayi sha fama _Zazzafan son_ shi ta warke kuma ta manta bare kuma shi da take da yak'inin wasu abubuwa ne game da ita ke tafiya dashi bawai zallar sonta bane.
Tana tsaye har wata motar ta zo ta dallare ta har sai da ta kare idanunta da hannu motar ta zo gefenta tayi parking sannan aka zuge Glass din ta hango na ciki.
Gabanta ya yanke ya fad'i taji kamar ta sume don fargaba..meyasa abubuwa suke zuwar mata a haka ne."?
Babu shiri ta nemi hanyar barin wajen yayin da Yusuf ya biyo ta yana kira "please Hafsah.!!
Rasa inda zata dosa tayi wurinshi ko kuma gida sai ta tuno da akwai wata kwabar kuma sannan ta kuma kwaba wata jikin ta babu k'wari ta nufo motar babu wata wata ta buda zata shiga koma meye ayi ta ta k'are.
_Yau kawai tunda ya yini yakejin shi babu k'wari sakamakon rashin samun damar yin waya da ita da yake yaji a ranshi bai kyauta mata ba hakan yasa yau ya taho afujajen duk da yana ganin kamar dare yayi amma yayi niyya yazo minti goma ne yayi shidai yasa ta a idanunshi..amma kuma yayi bak'in gamo._
Duk da wani bangare na zuciyar shi na cewa ya mata uzuri ko abokin aikin ta ne amma kuma kishi da kuma abinda ya tayi mishi game da aikin nata ya hana wannan tunanin nashi tasiri. Wato dama saboda irin haka ne ba zata bar aikin ba kenan.!!
Ta kasa mishi ko da sallama sai zama da tayi sukayi jugum shi da ita kana kallon fuskar shi zaka karanci matuk'ar damuwa da bak'in ciki.
Yusuf yaga inda ta shiga kuma yaji shakkar binta don haka ya tsaya cak ya bata lokaci yana kallo motar tashi yayin da shi kuma Ukhashatu yake k'are mishi kallo shima.
Sai cam kuma Yusuf din ya matsa ya koma jikin motar shi yadda Ukhashatu baya iya hangoshi.
Matsawarshi tayi daidai da budewar bakin Ukhasha..
Ya kallo ta gami da zuba mata idanunshi da suka tsorata ta taga zallar kishi da fushi a cikinsu.
"Na sani nayi laifi tun farko nine na miki katsalondon ban tsaya na nemi yardarki ba kafin na zurfafa akan son aurenki amma ki sani ba laifi na bane kawai Allah ne yayi lokacin yazo."
Ya tsaya ya had'iye wani abu mai matuk'ar tauri. Sannan ya bayyana mata zallar abinda ke ranshi domin yanayin fuskar shi ya bayyana mata hakan.
Sai da ya kira sunanta ta bashi dukkan hankalinta kafin ya fara maganar kamar an tilasta mishi murya a dusashe.
_"Don Allah idan kina damuwa akan tarayyar mu ki fada min, in sha Allah zaki same ni mai hakuri.. Zan dauki kaddara don nasan indai Allah baiyi zamuyi aure ba ba zamuyi ba.. Don Allah kada ki damu idan kinji banyi miki ba a matsayin mijin da kikeso ki sanar dani koda a text ne wallahi zan janye.!!_
Yana kaiwa nan ya gimtse baki yana kauda kai don da kyar ya k'arasa zancen.
_Shurun shi daidai da rushewar kukanta lamarin daya daga mishi hankali gefe guda ya kuma b'ata mishi rai._
_Shi a ganinshi wannan ba wani abin tashin hankali bane ashekarunta ma ta wuce irin haka tana da zab'i dama abu ne na Eh ko Aa."_
Zuciyarshi ta hana shi koda kallonta ne saboda Ukhashatu yana da zuciya wani lokacin sai kawai ya kawar dakai yana jijjiga k'afa."
Amma ta wani fannin kukanta yana tasiri sai dai bai san yadda zaiyi mata bane kawai.
Tayi mamakinshi don haka ta rarrashi kanta cikin hawayen tace.
Kayi hakuri nima ba'a son raina komai ke faruwa ba."?
Ya juyo ya kalleta da fargaba da kuma neman karin bayani.
Hafsah tasa mayafi zata share hawaye yayi saurin mik'a mata Handkerchief d'inshi ta kuwa amsa.
Ta share hawayen sannan ta fuskance shi sosai. Ta yanke shawarar fada mishi komai don ta kauda shakku daga zuciyarshi.
_"Bansan za'a mana engagement ba ranar da akayi ma bana nan har lokacin daka kirani kake min zancen nabar qawayena da aiki nah..wallahi ba rashin daraja ka ne ko nuna baka isa ba yasa na fada maka abinda na fada maka ba..kawai dai naga kana fassara ni ne kan ba yadda nake ba kuma kana nuna kamar ina maka_
_boye boye amma kayi hakuri."_
Tare suka sauke ajiyar zuciya.
Ukhashatu yaji dadin batun da tayi shi a takaice amma ya wanke mishi zuciya jira yake kawai yaji matsayin shi a wajenta.
Cike da murmushi yace,
"Na yarda dake.!!
Tayi d'an takaitaccen murmurshi kafin tace..
"Kai zabina nane kuma zabin Abba nah.."
Farinciki mara misaltuwa ya bayyana a fuskar Ukhashatu yayi mata kyautar tsadadden murmurshi.
Nagode mai sunan Hajiyata."
Sai lokacin bakin shi ya bude ya samu damar tambaya. Cikin hadewar rai kamar bashi yayi mata murmurshi yanxu ba.
Waye wancen toh."?
Ta dan zaro ido kafin ta saduda tace "He's my ex!!
Don bata iya k'arya ba.
"Exxx"??
Ya tambaya yana jan kalmar.
Hafsah ta danyi murmurshi.. ina mamakin yadda kake had'uwa da mutanen da suka dade da barin rayuwa.
Ta tausasa murya believe me wallahi duk randa kuke had'uwa nima ranar nake qara ganinsu bayan tsahon lokaci.!!
Ya jinjina kai kafin yace "Zaki bani labari but ina zuwa.!!
Ta kalleshi da mamakin abinda yake shirin yi sanda ya fita.
Shiko gun Yusuf ya fita kai tsaye ya mishi sallama Don bazai iya bashi hannu ba saboda kishi.
_Yusuf wanda nutsuwa ta fara zuwar mai sai abinda ba'a rasa ba wanda ya zamar jiki_
Ya amsa asanyaye.
Babu bata lokaci yace.
Kaine kaxo wajen Hafsah koh."?
Yusuf ya jinjina kai da sauri yana k'ara kallon Ukhasha yana tunani ai kamar dai Hafsah bata da yaya namiji.
_"She was like she's the first born kamar dai haka ya santa ya manta dai."_
*"Kayi hakuri an mata miji kada ka sake zuwa neman ta!!*
Inji Ukhashatu cikin maganar shi mai kama da gargadi wanda ta girgiza Yusuf ya kasa katabus.
Ukhashatu na k'are zancen yabar mishi gurin.
Yana dawowa Hafsah ta zuba mishi ido.
Cikin mamaki ta tambaye shi "me kace mishi."?
Ya dan harare ta "ina ruwanki mai kuka."?
Ta kawar da kai cike da kunya..
Yayi kasa da murya.. me yasa a lokacin baki tambaye ni ba kin ce.
"Malam shin an baka ni ne da kake kafa min dokoki."?
Gaba-d'aya suka sa dariya.
Ukhashatu ya kalli hannunta dake bisa cinyarta babu zobe ko daya ajikin yatsun zai jan kunshi a iya yatsun daya saka sukayi kyau.. baisan sanda yakai hannu ba yayi kamar zai tab'a sai ya fasa ita kuma tayi saurin dauke hannanyen. Ya hada hannaye alamun Afwan ta dan hade rai.
Sannan yace "Ya baki saka zoben a hannunki ba ko baiyi miki ba."
"Ai baka ce nawa bane ta fad'a da zolaya."
Ya nunata da hannu. "Kinganki koh."?
To ki saka... ya rage murya ko sai na sa miki."?
Tayi saurin girgiza kai a kunyace shima yayi dariya sannan ya duba ya juya can sit din baya ya dakko wata leda ya mik'a mata yana fad'in "Ungo amarya.!!
Lokacin ita kam ta nutsa cikin tunani kan abunda suka faru yanxu.. wato attempting (yunkurin ) taba hannunta da yayi sai kuma cewar zai sa mata zobe da yayi.. abin ya tuno mata da da sanda Yusuf yasa mata zoben shi..
Ta tambayi kanta..
_"Me yasa abin yaso maimaita kansa"?_
Bata zargin Ukhashatu da komai tana mishi kyakyawan zato sai ta ta'allaqa hakan kan yadda suka kebe a guri mai irin mota su biyu. Dama addini ya hane mu da haka.
Astagfirullah!!
Ta motsa baki ta fada.
Acikin karamin sauti yace tunanin me kike neh uhum"?
Tayi saurin juyowa tasa hannu biyu ta amshi ledar da abinda ke ciki daya fi kama da ice-cream.
Bai magana ba ya bude motar.
Ya fita sannan ya zagayo ya bude mata itama ta fito suka fuskanci juna..
Bari na tafi kada dare yayi min amma in sha Allah gobe zanzo ki bani labarin kinji."?
Ta gyada kai sannan yasa hannu a aljihun shi ya ciro katina ya bata "Gashi wannan na bikin Qanwata maryam tace na kawo miki in sha Allah gobe zan taho dana Abba."
Shima tasa hannu ta amsa.
Ki shiga gida sai in tafi yace mata.
Ta mishi murmurshi sannan ta juya cike da farinciki ta wuce.
Yayi murmurshi shima komai kan idon Yusuf.
Har kwalla yaji ta zubo mishi.
Har Ukhashatu yabar wajen Yusuf tsaye.
Sai da ya gaji da kanshi yabar wajen.
_Hafsah kada kiyiwa Allah butulci hak'ika rayuwarki gaba-taci ba baya ba. Kuma yanzu you're engaged kin yiwa Yusuf nisa._
Ta daga kanta ta kalleshi ya kuwa k'ura mata ido kallon ta na tuno mishi abubuwa da dama.
Me ya kawo ka wajena."?
Ta fad'a da kaushin murya.
Bani da hanyar contacting dinki ina miki magana kina share ni kiyi hakuri, na zo ne na baki hak'uri... ya d'anyi shuru kafin yace _and to tell you that my father had died._
Tayi jimm sai yanxu taji d'an tausayin shi saboda a yadda tasan Yusuf da yadda yakeson iyayenshi kuma suma suke son shi.
"Ahankali tace Allah ya jik'anshi."
Yayi wani bushashshen murmurshi ta kuma lura da kwallar data taru a idanunshi.
"Amiin ya amsa sannan ya dora cikin sanyin muryar.
Please Hafsah ki yarda muyi aure mana wallahi na daina duk.."
Ta daga mishi hannu cike da b'acin rai.
Nooo never.!! Kada ka kara mini wannan zancen and kada ka kara zuwa wajena.."
Tana shirin juyawa gida taji cikin daga sauti yace...
Don Allah ki taimakeni Nasan kina sona fah Basma ne ta rabamu kuma nayi regret abinda ya faru..please Hafsah I lost my dad kada na rasa ki kema.."
Ga mamakin ta sai taga yana share hawaye ta tsaya jimm cikin takaicin abubuwan wacce kaddara ce ma tasa ya dawo gareta..ita ta manta dashi ta manta duk wata rayuwar da sukayi a baya imma dad'in ta da wahalar ta duk ta manta. To kuma me zaisa ya dawo mata da wannan zancen gani takeyi ma k'arya yake lokacin yayi tsaho ace da ragowar son ta a zuciyar shi..
Ko ita da tayi sha fama _Zazzafan son_ shi ta warke kuma ta manta bare kuma shi da take da yak'inin wasu abubuwa ne game da ita ke tafiya dashi bawai zallar sonta bane.
Tana tsaye har wata motar ta zo ta dallare ta har sai da ta kare idanunta da hannu motar ta zo gefenta tayi parking sannan aka zuge Glass din ta hango na ciki.
Gabanta ya yanke ya fad'i taji kamar ta sume don fargaba..meyasa abubuwa suke zuwar mata a haka ne."?
Babu shiri ta nemi hanyar barin wajen yayin da Yusuf ya biyo ta yana kira "please Hafsah.!!
Rasa inda zata dosa tayi wurinshi ko kuma gida sai ta tuno da akwai wata kwabar kuma sannan ta kuma kwaba wata jikin ta babu k'wari ta nufo motar babu wata wata ta buda zata shiga koma meye ayi ta ta k'are.
_Yau kawai tunda ya yini yakejin shi babu k'wari sakamakon rashin samun damar yin waya da ita da yake yaji a ranshi bai kyauta mata ba hakan yasa yau ya taho afujajen duk da yana ganin kamar dare yayi amma yayi niyya yazo minti goma ne yayi shidai yasa ta a idanunshi..amma kuma yayi bak'in gamo._
Duk da wani bangare na zuciyar shi na cewa ya mata uzuri ko abokin aikin ta ne amma kuma kishi da kuma abinda ya tayi mishi game da aikin nata ya hana wannan tunanin nashi tasiri. Wato dama saboda irin haka ne ba zata bar aikin ba kenan.!!
Ta kasa mishi ko da sallama sai zama da tayi sukayi jugum shi da ita kana kallon fuskar shi zaka karanci matuk'ar damuwa da bak'in ciki.
Yusuf yaga inda ta shiga kuma yaji shakkar binta don haka ya tsaya cak ya bata lokaci yana kallo motar tashi yayin da shi kuma Ukhashatu yake k'are mishi kallo shima.
Sai cam kuma Yusuf din ya matsa ya koma jikin motar shi yadda Ukhashatu baya iya hangoshi.
Matsawarshi tayi daidai da budewar bakin Ukhasha..
Ya kallo ta gami da zuba mata idanunshi da suka tsorata ta taga zallar kishi da fushi a cikinsu.
"Na sani nayi laifi tun farko nine na miki katsalondon ban tsaya na nemi yardarki ba kafin na zurfafa akan son aurenki amma ki sani ba laifi na bane kawai Allah ne yayi lokacin yazo."
Ya tsaya ya had'iye wani abu mai matuk'ar tauri. Sannan ya bayyana mata zallar abinda ke ranshi domin yanayin fuskar shi ya bayyana mata hakan.
Sai da ya kira sunanta ta bashi dukkan hankalinta kafin ya fara maganar kamar an tilasta mishi murya a dusashe.
_"Don Allah idan kina damuwa akan tarayyar mu ki fada min, in sha Allah zaki same ni mai hakuri.. Zan dauki kaddara don nasan indai Allah baiyi zamuyi aure ba ba zamuyi ba.. Don Allah kada ki damu idan kinji banyi miki ba a matsayin mijin da kikeso ki sanar dani koda a text ne wallahi zan janye.!!_
Yana kaiwa nan ya gimtse baki yana kauda kai don da kyar ya k'arasa zancen.
_Shurun shi daidai da rushewar kukanta lamarin daya daga mishi hankali gefe guda ya kuma b'ata mishi rai._
_Shi a ganinshi wannan ba wani abin tashin hankali bane ashekarunta ma ta wuce irin haka tana da zab'i dama abu ne na Eh ko Aa."_
Zuciyarshi ta hana shi koda kallonta ne saboda Ukhashatu yana da zuciya wani lokacin sai kawai ya kawar dakai yana jijjiga k'afa."
Amma ta wani fannin kukanta yana tasiri sai dai bai san yadda zaiyi mata bane kawai.
Tayi mamakinshi don haka ta rarrashi kanta cikin hawayen tace.
Kayi hakuri nima ba'a son raina komai ke faruwa ba."?
Ya juyo ya kalleta da fargaba da kuma neman karin bayani.
Hafsah tasa mayafi zata share hawaye yayi saurin mik'a mata Handkerchief d'inshi ta kuwa amsa.
Ta share hawayen sannan ta fuskance shi sosai. Ta yanke shawarar fada mishi komai don ta kauda shakku daga zuciyarshi.
_"Bansan za'a mana engagement ba ranar da akayi ma bana nan har lokacin daka kirani kake min zancen nabar qawayena da aiki nah..wallahi ba rashin daraja ka ne ko nuna baka isa ba yasa na fada maka abinda na fada maka ba..kawai dai naga kana fassara ni ne kan ba yadda nake ba kuma kana nuna kamar ina maka_
_boye boye amma kayi hakuri."_
Tare suka sauke ajiyar zuciya.
Ukhashatu yaji dadin batun da tayi shi a takaice amma ya wanke mishi zuciya jira yake kawai yaji matsayin shi a wajenta.
Cike da murmushi yace,
"Na yarda dake.!!
Tayi d'an takaitaccen murmurshi kafin tace..
"Kai zabina nane kuma zabin Abba nah.."
Farinciki mara misaltuwa ya bayyana a fuskar Ukhashatu yayi mata kyautar tsadadden murmurshi.
Nagode mai sunan Hajiyata."
Sai lokacin bakin shi ya bude ya samu damar tambaya. Cikin hadewar rai kamar bashi yayi mata murmurshi yanxu ba.
Waye wancen toh."?
Ta dan zaro ido kafin ta saduda tace "He's my ex!!
Don bata iya k'arya ba.
"Exxx"??
Ya tambaya yana jan kalmar.
Hafsah ta danyi murmurshi.. ina mamakin yadda kake had'uwa da mutanen da suka dade da barin rayuwa.
Ta tausasa murya believe me wallahi duk randa kuke had'uwa nima ranar nake qara ganinsu bayan tsahon lokaci.!!
Ya jinjina kai kafin yace "Zaki bani labari but ina zuwa.!!
Ta kalleshi da mamakin abinda yake shirin yi sanda ya fita.
Shiko gun Yusuf ya fita kai tsaye ya mishi sallama Don bazai iya bashi hannu ba saboda kishi.
_Yusuf wanda nutsuwa ta fara zuwar mai sai abinda ba'a rasa ba wanda ya zamar jiki_
Ya amsa asanyaye.
Babu bata lokaci yace.
Kaine kaxo wajen Hafsah koh."?
Yusuf ya jinjina kai da sauri yana k'ara kallon Ukhasha yana tunani ai kamar dai Hafsah bata da yaya namiji.
_"She was like she's the first born kamar dai haka ya santa ya manta dai."_
*"Kayi hakuri an mata miji kada ka sake zuwa neman ta!!*
Inji Ukhashatu cikin maganar shi mai kama da gargadi wanda ta girgiza Yusuf ya kasa katabus.
Ukhashatu na k'are zancen yabar mishi gurin.
Yana dawowa Hafsah ta zuba mishi ido.
Cikin mamaki ta tambaye shi "me kace mishi."?
Ya dan harare ta "ina ruwanki mai kuka."?
Ta kawar da kai cike da kunya..
Yayi kasa da murya.. me yasa a lokacin baki tambaye ni ba kin ce.
"Malam shin an baka ni ne da kake kafa min dokoki."?
Gaba-d'aya suka sa dariya.
Ukhashatu ya kalli hannunta dake bisa cinyarta babu zobe ko daya ajikin yatsun zai jan kunshi a iya yatsun daya saka sukayi kyau.. baisan sanda yakai hannu ba yayi kamar zai tab'a sai ya fasa ita kuma tayi saurin dauke hannanyen. Ya hada hannaye alamun Afwan ta dan hade rai.
Sannan yace "Ya baki saka zoben a hannunki ba ko baiyi miki ba."
"Ai baka ce nawa bane ta fad'a da zolaya."
Ya nunata da hannu. "Kinganki koh."?
To ki saka... ya rage murya ko sai na sa miki."?
Tayi saurin girgiza kai a kunyace shima yayi dariya sannan ya duba ya juya can sit din baya ya dakko wata leda ya mik'a mata yana fad'in "Ungo amarya.!!
Lokacin ita kam ta nutsa cikin tunani kan abunda suka faru yanxu.. wato attempting (yunkurin ) taba hannunta da yayi sai kuma cewar zai sa mata zobe da yayi.. abin ya tuno mata da da sanda Yusuf yasa mata zoben shi..
Ta tambayi kanta..
_"Me yasa abin yaso maimaita kansa"?_
Bata zargin Ukhashatu da komai tana mishi kyakyawan zato sai ta ta'allaqa hakan kan yadda suka kebe a guri mai irin mota su biyu. Dama addini ya hane mu da haka.
Astagfirullah!!
Ta motsa baki ta fada.
Acikin karamin sauti yace tunanin me kike neh uhum"?
Tayi saurin juyowa tasa hannu biyu ta amshi ledar da abinda ke ciki daya fi kama da ice-cream.
Bai magana ba ya bude motar.
Ya fita sannan ya zagayo ya bude mata itama ta fito suka fuskanci juna..
Bari na tafi kada dare yayi min amma in sha Allah gobe zanzo ki bani labarin kinji."?
Ta gyada kai sannan yasa hannu a aljihun shi ya ciro katina ya bata "Gashi wannan na bikin Qanwata maryam tace na kawo miki in sha Allah gobe zan taho dana Abba."
Shima tasa hannu ta amsa.
Ki shiga gida sai in tafi yace mata.
Ta mishi murmurshi sannan ta juya cike da farinciki ta wuce.
Yayi murmurshi shima komai kan idon Yusuf.
Har kwalla yaji ta zubo mishi.
Har Ukhashatu yabar wajen Yusuf tsaye.
Sai da ya gaji da kanshi yabar wajen.