← Book details Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 88

Sashe 28

Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*Kimamin* sati d'aya kenan dayin birthday d'in, Basma, kullum Hafash zuba idon ganin Yusuf take yi, amma shiru.'
'Duk da tasan ita take hana shi zuwa, amma sai zuciyarta ta fara raya mata 'kodai ya manta da ita ne'? ('Zuciya kenan')
'Ita a yadda tayi kewarshi batak'i yazo d'in ba, idan yaso sai, tace wa Abba, 'Zuwa yayi ya amsa kiran da yayi mishi'...😅😅
'B'angaren su Basma kuwa, abu yayi nisa ita da Yusuf, kullum sai sunyi waya, kuma Basman ce ke kiranshi, shi kuma baya k'in d'aga wa
'Yau da sukayi waya ne, take tambayar shi, 'Wai shin yau zaije club ne? Yace mata bashi da niyya, amma idan zataje shima zaije, taji dad'in hakan da yace, 'wato idan hakane tana iya samun alfarma kenan a wajenshi?..
'To kwa tabbas zata gwada sa,arta.'
'Aranar da suka had'u a club d'in bayan sunsha rawa sosai, basma ta nemi dasu k'ebe tana so su tattauna, ya rik'o hannunta, ('Wanda zuwa lokacin k'aramin abune a wajen su su rik'e hannun juna') suka fito daga cikin hayaniyar zuwa harabar wajen inda aka ajye kujeru domin zama.'
'Kafin ta fara magana ya riga ta, don shima d'in yana da abin cewar da yake ganin bazai iya hak'uri har ta fad'i nata ba.'
"Please basma help me" ta kalleshi da mamaki, "With what?
'Ya marairaice please ki daure kije gidansu Hafsah, ki bata wayanki ina so muyi magana ne please"!
'Take yanayinta ya chanja wanda shima sai da yaga hakan, har ya karanta mata alamun tambaya a fuskarshi, sai tayi saurin wayancewa ta k'irkiro murmushin dole ta d'ora akan fuskarta.'
'Hmm, banyi maka promise ba, but zanje cikin satin nan. 'Yai ajiyar zuciya tare da ce mata "please basma help me, kinji,' na kuma bata waya ne, so i think Abbansu ya kuma k'wace wa.'" ta d'an cije lebe sannan ta daure tace mishi, "Ok don't worry"
Yai murmushi sannan yace, "Thank you"
'Ya kuma tattaro hankalinshi gurinta, sannan yace, "What about yours?
'Tayi wani murmushi sannan ta gyara zamanta tace cikin wata marainiyar murya,
"Nawa yana da wahala, bana jin zaka yarda."
'Ya girgiza mata kai had'i da cewa, "No, please tell me, zanyi miki kinji"
'Sai lokacin ta sami k'warin guiwar fad'amishi abinda ke ranta.'
"Um, tun lokacin da muka rabu da ex ena, yake min abubuwan da banjin d'ad'i, yana min maganganu a status, sannan yace wai ban isa na sami saurayi wanda ya kaishi ba, so ina son in nuna mishi k'arya yakeyi..' Tayi shiru data zo nan a zancen, yayin da shikuma ya bata duk hankalinshi, da yaji tayi shiru, yai mata alamar, 'Yana sauraronta ta, ta cigaba.'
"So please ina so ne ka dinga acting like you're my boyfriend.."
"What? Ya fad'a yana girgiza mata kai,
"No, I can't, am not like that, please am sorry to say 'bazan iya ba!"
'Basma ta d'ora mishi ido ta kasa d'aukewa, daman tasan hakan zai iya faruwa.'
'Sai ta shiga kawo mishi hujjoji marasa tushe, yadda zata gamsar dashi har ya yarda.'
"Am sorry if I hurt you, but ina cikin wani hali wallahi, nasan kuma Hafsah Kake tunani, to ka daina, I have an assurance that 'bazamu sami sab'ani da ita ba, ta fahimceni, kuma nima zanyi mata bayani, please help me"..
'Yai ajiyar zuciya, sannan ya fara magana cikin nutsuwa, "I can't gaskiya, kinga bani son in sami matsala ni da hafsah, 'sannan ex enki ina baki shawaran ki cancel duk wani abu da yake connecting enki dashi, kuma ki zuba shi a dustbin, ki daina damuwa da zancen shi, kawai, that's my advice"
'Tayi shiru, batason ta nuna nacinta a wajen shi, sai ta share kawai tace "Ok thank you, my friend" yai murmushi sannan ya maimaita
"Your friend"?
Ta d'aga mishi gira, "Yes, as your girlfriend's friend so we are friends" isn't it?
Yai murmushi that's true"
'Sannan ya kuma mik'a mata rok'on shi, da ya tabbatar mata cewa ya damu sosai "So please yaushe zaki je gidan"?
ita ko lokacin haushin shi, takeji ma, amma sai ta kanne tace " zan tambayi mum enmu, kuma yanzu yawanci bata gida ita Hafsan, so banso inje bata nan"
"Please kiyi k'ok'ari kinji"
Ataik'aice tace "Ok"
Yai murmushi sosai "Thank you"
'To basma tana iya k'ok'arinta wajen yin, duk abinda tasan idan tayi zata ja ra,ayin Yusuf, misali 'Yanzu suna yawan had'uwa a gurare da yawa irin na shak'atawa, saboda haka duk inda ta sami dama tana k'okarin ta nuna mishi tabbas, ita ba irin hafsah bace, a fannin wayewa.'
'Takan mik'a mishi hannu su gaisa aduk sanda suka had'u, sannan idan hira ta had'asu tana k'ok'arin nuna mishi cewa ita fa tana cikin 'kewa'..
'Shi kuma har yanzu ya kasa fahimtar manufarta..
'Amma shima a nashi b'angaren akwai wani b'ahagon tunani a cikin zuciyarshi..
Amma da yake ance so sone, amma son Kai yafi, Yusuf, sai kawai ya yardarwa kanshi abinda zuciyarshi ta dad'e tana karanta mishi.'
A ganinshi sam baza,a kira hakan da yaudara ko cin amana ba.'
'Yanzu, 'kwance yake a d'akin shi, gaba d'aya yau babuy kowa acikin gidan nasu, shi kad'aine.'
'Ji yake komai yayi mishi zafi, har yake jin abin yau yafi na kullum.' ya tuno rabonshi da hakan tun yana makaranta, sai abinda ba,a rasa ba, kuma, ba wai rasa 'yan matan yayi ba, amma shi kawai yafi son 'yan matan can k'asar bawai na nan ba.'
'Hafsah ce kawai yaji yana so, kuma yaji zai ta dace da shi.' 'Shine ma dalilin da yasa, har ya d'auki wannan lokacin, wai yana jiran ta yarda dashi ne, to kuma yaga bata da niyyar hakan.. Gashi su 'yan matan nasa nacan, sunyi nisa dashi, sai dai a waya, kawai, shi kuma hakan sam baya wadatar dashi.'
'Yai shiru, yana tunanin abinyi, basma ce ta fad'o ranshi, yayi saurin d'aukar wayarshi ya danna kiranta, tana ganin shine ta share don zatonta zancen Hafsah zai mata, har ta tsinke, sai a kira na uku ne ta d'auka, yanayin da taji muryarshi, tasan akwai magana, a d'an sama-sama suka gaisa, tana shirin tambayar shi, make damunshi' ya riga ta,
"Please basma kina gida ne?"
Tace mishi, 'Eh"
"Please kizo gidanmu yanzu,"?.cikin mamaki tace gidanku, kuma"?
"Yes, please ina son muyi magana ne"
Ta d'anyi shiru, sai kuma wani tunani yazo mata na 'gwara ta dinga mishi alfarma ko shima zai yarda da buk'atarta"
Tace "Ok"
Yace "Zan turomiki address"
'Nan da nan tayi shiri, cikin wasu, da wando da suka matseta sosai, itama Maman tata bata nan, tana gama shiryawa text d'in ya shigo na address d'in, ta mik'e ta d'auki jakarta, tana fitowa harabar gidan ta gamu da Aysha tahir, taja tsaki a zuciyarta, wato zata b'ata mata shiri.' A d'an share suka gaisa,
"A,a basma ina zuwa haka?
"Hmm kinji ki da k'wak'wafi, to some where"
"Aysha ta kalleta sosai sannan tace "Oh lallai kin fa had'u sosai," Basma, tayi murmushi,
"Thank you"
"Muje tare mana, inji Aysha, wacce ta zuba wa basma ido, tana karantar yanayinta sosai,"
'Basma ta d'an had'e rai kad'an, "No, am sorry gaskiya, bazaki bini ba"
'Aysha ta rik'e baki, tana mamakin alamun tsoron data gani cikin idanun basma, da kuma sauyawar da tayi, 'sai ta jefa mata tambayar son gano, abinda take b'oye mata,
"Am lallai ma basma wa kika samu ne da har kike nuna min wariyar launin colour"
"Am um, kinga, am sorry ba haka bane, kawai dai, yau muka had'u dashi ne, so kinga ba zamu fara zuwa mu biyu ba."
'Aysha tayi wani murmushi, "Ok, hakane, kice kinyi babban kamu."
'Suka shek'e da dariya duka har da tafawa.'
'Anan Aisha taga asarar ta bar basma ta wuce ba tare da ta tabbatar da zarginta ba, don haka tace cikin siyasa.'
"Please basma kada kice na tsayar da ke wani application, nekeson zan tura, a wayarki, saboda shi nazo ma."
Basma tace,
"Oh, sauri nake amma ungo ki tura."
'Aysha na karbar wayar taga text, akai sai kawai ta shiga ta duba, Address ta gani, tayi saurin matse wayar zuwa silent, sannan tayi screenshots, ta shiga zendar ta tura, sannan ta zab'i application guda d'aya ta tura, ta goge history na photon 'screenshot' data tura, sannan ta dawo gallery ta goge shi, sanna ta duba logs taga wata number, wadda akayi kira baifi mintuna 25mins, ba da suka wuce, ta kalli number sosai sannan ta mik'awa Basma, wayarta, wacce ke ta faman gyara fuska da powder tun sanda ta bawa Aysha wayar.'
"Thank you"
'Inji Aysha basma ta karb'a suka jera suka fita, acikin layin basma ta sami 'Napep' ta hau tabar 'Aysha tsaye' tana d'aga mata hannu.'
'Aysha ce cikin daidaita' sahu' (Keke Napep) ta zaro wayarta ta kalli number da ta turo text a wayar basma, ta rik'e number, sannan ta saka a wayarta, number Yusuf, ce ta fito, wacce ita rabon daya kirata tun ranar da sukayi final papper, da tana tunanin, goge number d'in ma, 'sau uku tana saka wa, amma abinda ke fitowa a wayar kenan, mamaki ya cikata, da gida zata,' tace aranta 'Dole ne fa ta sanar da Hafsah, abinda ke faruwa, idan ba haka ba itama taci amanar Hafsan'
'Bata tab'a zuwa gidan su hafsar ba, amma, ta rik'e kwatancen da Hafsa ta tab'a yi mata.' 'Amma zata fara zuwa gida, ta d'akkowa Hafsa kyautar da yusuf d'in yai mata...
Ta isa gidan a gurguje ta ce wa Mamansu, zasu, je duba Hafsah ne ita da Basma, ta d'akko ledar sannan ta fito ta tarar mai adaidaitan yana jiranta, dama tsayar dashi tayi, ta fad'a mishi sunan unguwar da kuma, layin, ta shiga suka tafi, tana jinjina cin amana irin na Basma...

_Muje zuwa.._

*Hajeeyah Kareemerh ce* 👌🏼
[1/11, 12:11 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔

Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to: Unique In Your*
*Love Heart Members*

*'Masoya na kune silar yin murmushi nah'*💃🏼💃🏼💃🏼😘😘😘😍😍😍 _Mom samhat, pretty, aysha Abdullahi (aysha sheka), Ayshaatou ('yan boarding book) ina yinku_ 💯

📄 *31*
Chapter 28 · 0% Book details