Sashe 20
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*Cikin* in'ina tace "Am, um, Mama bamu ganta ba"
"Don Allah duba min ita" cewar mama ad'an rud'e.
Nasreen ta fita da sauri, ta nufi wajen parking d'in motoci har, tagama zagayenta bata ga motar Yusuf ba.. Ita bata kawo wani abu ba zatonta ko sun gama ne, Hafsah ta koma cikin Hall d'in'
Abakin wajen shiga ta tarar da Mama. Ta tareta da tambaya, "Kin ganta?
"A,a Mama, banganta ba"
Cikin rud'u mama tace" Subhaanallah, to Ina Hafsah ta tafi ne?"
"Mama may be fa tana cikin Hall"
Cewar Nasreen.
"Na duba kowanne table bata nan."
Mama ta Kalli Nasreen sosai sannan tace "Nasreen baku ganta da wani ba"??
Cikin Nasreen ya kad'a. Tayi saurin girgiza kai,
"A,a mama, Nidai sanda kuka zo tana wajenmu, sai dai idan tare da bashir suka fita, saboda d'azu muna tare yace sai shiga store d'in opposite nan ya..
Bata k'arashe maganar ba suka hango bashir d'in na nufosu, yana k'arasowa mama ta tare shi da tambaya "Bashir baka ga yayarku ba?
"Na ganta"
Mama ta zaro ido.
"A ina??
Sai kuma yayi wani tunani,
"Oh mama na daiga wata kamar ita."
Mama ta galla mishi harara "Kai bashir ka kiyayeni!?
"A ina ka ganta"
Ya d'an hau in'ina Um a.. a.. afa tiittin nan ne"
Ya fad'a yana nuna hanyar waje.
Cikin tsoro Mama ta furta
"In na lillahi wa inna ilaihiraji,un"
Nasreen ta yi tsuru,
Mama ta jinjina kai sannan ta juya zuwa cikin Hall hankalinta a tashe.
Tana shiga kiran Abba ya kuma fitowa da ita, ta d'aga kiran ga mamakinta ce mata yayi ,
Amina ina hafsah"
Dam gabanta ya fad'i, am ta d'an fita daga Hall d'in"..
"Ina taje? Ya katseta da wannan tambayar..
Ta.. ta. tafi ne Nemo min ruwa".
Muryarshi fal da takaici yace "Ok gani nan zuwa zan kawo hajiya."
Cikin far gaba tace "Ok sai kun iso"
Idon Abba har wani ja yayi, Allah yaso Hajiya bata ga Hafsan ba. Shine ya hangota sunfito daga layin wajen bikin. Sunyi b'arin dama yayin dashi yake daga b'arin hagu.
Babu abinda zuciyarshi bata raya mishi ba na game da Hafsan, tsoro da fargabar abinda zai sameta suka cika shi. Babu shakka ba don da Hajiyah, suke ba babu abinda zai hana shi binsu..
"Hasbunallahu, Yake ta maimaitawa acikin zuciyarshi.
Yana sauke Hajiyar, ya kirata ta fito.
Ta karanci halin b'acin ran daya chanja yanayinshi sosai,
"Wato Sakacinki ya kai har tabar cikin gurin nan baki sani bako??
Da kalmomin da ya tare ta kenan.
Wanda kafin ta gama tantancesu
Ya kuma jefo mata wata.
"Wallahi idan naji wani abu sab'anin tunani na, sai nayi mummunan sab'a miki.. "
Ya shige motar shi ya fizga da gudu..
Yabar Mama daskare a wajen.
Acan kuma Yusuf, bai tsaya ba sai a wani wajen shak'atawa, tun a mota take son mishi magana amma tsoron gudun da suke shek'awa ya hana bakinta bud'ewa.
Da kanshi ya fito ya bud'e mata motar. Ta fito a tsorace, bata gama tsorata ba, sai da suka fito, ya kamo hannunta cikin nashi ya rik'e, gam, ta dinga motsa hannunta da nufin ta k'wace amma ta kasa." Yana jin yadda take motsa hannun amma ya bagaras da ita, sai ma wani murmushin k'auna da yake mata... Haka bisa wajibi ta ta hak'ura, suke tafiya har suka isa wurin wasu kujeru, suka zauna.
Sunyi shiru, yayin da ita ahankali take sauke numfashi,..
Ahankali ta bud'e baki murya ak'asa tace cikin k'aguwa..
"Please Dear me, me muka zo yi nan ne?
Ya zubo mata fararen idanuwanshi, please ki kalla nan mana kowa na kulawa da babynshi amma, mu always kina had'a distance between us".. Please why?
Sai da ta sanya tunani da hankali sannan ta nemo inda zancen shi ya nufa... Alokacin tsoronta 'na ta baro Mama wajen party' ya gushe, sai taji alokacin ya dace tace wani abu da zai fahimtar da Yusuf, d'in manufarta akan soyyayyarsu.
Ta tattaro dukkan nutsuwarta, sai da ta kalleshi na fiye da mintuna 2, yayin da shima itan ya zubawa ido yana murmushin zaton yau buk'atar shi ta karb'u.
"Dear, ta furta ahankali.
Ya d'aga mata gira.
"Yess"
"I don't want to hurt you.. Don Allah mu daina maganar irin wannan relation, please let it be in our feature'..
Ya kalleta da alamar tambaya In Our feature?.. When ?
Cikin k'warin guiwa tace "I mean when we got married."
Yayi wata dariya wacce ita bata ga amfaninta ba.
"Hmm, baby you're talking about long time' let me tell you 'honest to God "I CAN'T WAIT".. So please allow me to get a solution to my self... Yai k'asa da murya, "Baby i promise to marry you but In sha Allah I will never beg you again!"..But kome ne ya faru kinsani kece kika ja...
Ta d'anyi shiru cikin nazarin maganarshi, ta kalli agogon hannunta, 5:30pm,
Ta mik'e da sauri, "Please let me go,.. "No, ki bari sai anjima mana.
Hankalinta gaba d'aya yayi can tace "No please let me go. And please dear when will you come to meet Abba"?
Yai murmushi hmm, Im afraid, but i will tell you soon."
Ya taso ya biyota ahankali suka fara tafiya..
"Baby ki karb'i wani wayar mana, i miss your goalding voice."
Ta d'anyi murmushin takaicin rashin wayarta, "No thank you dear."
Badon tsoron Abba ba babu abinda zai hanata karb'a
Ya bud'e mata motarshi, ya mata alama ta shiga.
Ta girgiza kai
"No barni na tafi"
"Please baby ki shiga na maidaki"
"No thank you.
"Ok,
"Please ki kirani idan kinje school."
"OK,
Ya rakata bakin titi, ta shiga mota sannan ya juya don shiga motarshi ya tafi.'
Tana fara tafiya a Napep d'in, taji fad'uwar gabanta ya tsananta. Allah yasa kada mama ta lura bata nan.
Tana isa ta fito ta bashi kud'in.
Ahankali take takawa, har cikin Hall d'in.
Da Amatullah ta fara cin karo, wacce ta tsoratata da cewa, "Hafsah, wai ina kika je ne? Mama sai Nemanki, take." "Innalillahi da gaske?
"Wallahi yanzu ma ta kuma fita nemanki."
Hafsah tayi shiru, amatullah ta ja hannunta suka yi ciki tana cewa, "Ansha rawa babu ke".. Har amarya da ango sunzo.
Filin rawar suka shiga 'yan matan family da samari anata chashewa."
Itama ta shiga akayi da ita, bashir ya matso dai dai kunnenta "yaya, wallahi Mama sai nemanki take, wai ina kuka fita?..nima na ganku fa!
tayi shiru kawai don bata da abin ce mishi.
Wajen mintinta 20mins, da dawowarta mama ta dawo. Tana hango ta tazo ta finciko ta, suka yi waje.
Mari Maman ta wanka mata.
"Ina kika je?
Ta rik'e kunci. Tayi shiru..
"Bazaki fad'amin ba, Mama ta fad'a tana shirin k'ara mata wani marin."
Cikin kuka ta ke mata bayani
"Banje ko ina ba"
"K'arya zaki yi min"?
Wallahi Hafsah ki shiga hankalinki zan tattaka ki anan wajen.."
Haba Amina, menene nayin hayaniya a nan wajen, ai bai dace ba."
Haba yaya wannan yarinyar idan kinga maganar da take d'akkomin sai kin tausaya min, ya zata dinga ja min laifi a wajen sa..
"Ya isa haka,.. Ta matso ta dafa kafadar Maman, kiyi ha'kuri kuje gida sai kiyi mata fad'a Allah ya shirya mana su."
Aunty Nafeesah ce 'Yayar Mama' wacce su Hafsah ke ce mata (Maman ya Nazeer,) daga ita sai baffa usman abbansu (Amatullah) sai Maman su Hafsah.
'Tana aiki ne a 'Ministry of women affairs' sannan malama ce ita a fannin addini, tana kuma da wajen gyaran jikin amare,
wanda yaranta keyi.'
Ala dole mama tayi shiru. Tana aunawa Hafsah uwar harara.
'Maman ya Nazeer, taja hannun Hafsah suka koma ciki, yayin da Mama wayar ta tayi k'ara kiran Abba ne.
"Hello"
"Ya ta dawo?
Eh, to maza ki tattarosu ku tawo.
"Tom"
Dama an kusa tashi, biki kuma yayi dad'i ga wad'anda hankalinsu ke kwance irin su 'Nasreen'
Ba Hafsah ba bashir ma yasha jinin jikinshi. Aunty Nafeesah ce tasa drivernta ya dawo dasu.'
'Hafsah dai sai rab'e tab'e take.'
Suna yin sallama ta shige d'aki.
Fatanta Allah yasa mama bata fad'awa Abba ba.'
Tana cikin bed room d'in tajiyo fad'an Abba a palour yana cewa,
"Ina take?? Ta fad'a miki inda taje?..
Mama tace cikin tsoro itama tana d'akinta..
Bata rufe baki ba, ya nufi d'akin Gadan -Gadan, Hafsah na shirin danna key taji ya banko k'ofar da k'arfi. sunayin ido biyu, ya shiga dukanta da bulalar hannunshi.
Ihu Hafsah take ba na wasa ba, saboda abba laftar ta yake sosai kamar wani k'aton yake duka..
Tana ta bashi hak'uri "Don Allah abba kayi hak'uri wallahi bazan sake ba" na shiga uku, wayyo mama, Abba, Innalillahi.."wayyo zan mutu"!!
Kamar zuga shi takeyi. Wato bakya jin magana koh? So kike ki lalace ne?, saboda kin zama 'yar kanki koh, shine har zaki dinga fita da wani, wato duk nasihar da nake miki bakiji ba ko?
Gidan uban wa kika je??
Ihu ta kuma, saki tama kasa magana sai karkarwa da muryarta take wall lahi.. Abb.. Abba"..
"Mufida har kuka ta fara tana, rik'e hannun Abba. Yaran ma sai hak'uri suke bashi.
'Mama tayi rok'on amma ina yak'i kyaleta.'
Ganin yana shirin kashe mata 'ya yasa ta yi azamar fincike ta, da karfi, tana haki muryarta na rawa take cewa, "Wallahi sai mu bar maka gidan, kashe min ita, zakayi?.. Ko me tayi ba sai ka kyaleta ba?" wasu Maganganun ma bata san tana fad'ar su ba.
Abba ya tsallake Hafsah, dake kwance shame -shame, ya fice daga d'akin ko kallon mama baiyi ba.
Cikin azama mama ta figi mayafinta da jakarta, tacewa bashir,
"Kamota mu fita da ita..
Sai gunjin kukan Hafsa kawai akeji. Ya kamata, ta mik'e da k'yar, ya rirrik'eta da k'yar take takawa, sukayi har yar gate' Mufida ta biyo su, mama zan biku"
Maman ta daka mata wata uwar tsawa daya sa ta koma babu shiri..
👏🏼👏🏼👏🏼
*Hajeeyah Kareemerh ce*
👍🏼👍🏼👍🏼
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah khareemerh)*
*Dedicated to:*
*Unique in your Love Heart Group members.*
📄 *24*
"Don Allah duba min ita" cewar mama ad'an rud'e.
Nasreen ta fita da sauri, ta nufi wajen parking d'in motoci har, tagama zagayenta bata ga motar Yusuf ba.. Ita bata kawo wani abu ba zatonta ko sun gama ne, Hafsah ta koma cikin Hall d'in'
Abakin wajen shiga ta tarar da Mama. Ta tareta da tambaya, "Kin ganta?
"A,a Mama, banganta ba"
Cikin rud'u mama tace" Subhaanallah, to Ina Hafsah ta tafi ne?"
"Mama may be fa tana cikin Hall"
Cewar Nasreen.
"Na duba kowanne table bata nan."
Mama ta Kalli Nasreen sosai sannan tace "Nasreen baku ganta da wani ba"??
Cikin Nasreen ya kad'a. Tayi saurin girgiza kai,
"A,a mama, Nidai sanda kuka zo tana wajenmu, sai dai idan tare da bashir suka fita, saboda d'azu muna tare yace sai shiga store d'in opposite nan ya..
Bata k'arashe maganar ba suka hango bashir d'in na nufosu, yana k'arasowa mama ta tare shi da tambaya "Bashir baka ga yayarku ba?
"Na ganta"
Mama ta zaro ido.
"A ina??
Sai kuma yayi wani tunani,
"Oh mama na daiga wata kamar ita."
Mama ta galla mishi harara "Kai bashir ka kiyayeni!?
"A ina ka ganta"
Ya d'an hau in'ina Um a.. a.. afa tiittin nan ne"
Ya fad'a yana nuna hanyar waje.
Cikin tsoro Mama ta furta
"In na lillahi wa inna ilaihiraji,un"
Nasreen ta yi tsuru,
Mama ta jinjina kai sannan ta juya zuwa cikin Hall hankalinta a tashe.
Tana shiga kiran Abba ya kuma fitowa da ita, ta d'aga kiran ga mamakinta ce mata yayi ,
Amina ina hafsah"
Dam gabanta ya fad'i, am ta d'an fita daga Hall d'in"..
"Ina taje? Ya katseta da wannan tambayar..
Ta.. ta. tafi ne Nemo min ruwa".
Muryarshi fal da takaici yace "Ok gani nan zuwa zan kawo hajiya."
Cikin far gaba tace "Ok sai kun iso"
Idon Abba har wani ja yayi, Allah yaso Hajiya bata ga Hafsan ba. Shine ya hangota sunfito daga layin wajen bikin. Sunyi b'arin dama yayin dashi yake daga b'arin hagu.
Babu abinda zuciyarshi bata raya mishi ba na game da Hafsan, tsoro da fargabar abinda zai sameta suka cika shi. Babu shakka ba don da Hajiyah, suke ba babu abinda zai hana shi binsu..
"Hasbunallahu, Yake ta maimaitawa acikin zuciyarshi.
Yana sauke Hajiyar, ya kirata ta fito.
Ta karanci halin b'acin ran daya chanja yanayinshi sosai,
"Wato Sakacinki ya kai har tabar cikin gurin nan baki sani bako??
Da kalmomin da ya tare ta kenan.
Wanda kafin ta gama tantancesu
Ya kuma jefo mata wata.
"Wallahi idan naji wani abu sab'anin tunani na, sai nayi mummunan sab'a miki.. "
Ya shige motar shi ya fizga da gudu..
Yabar Mama daskare a wajen.
Acan kuma Yusuf, bai tsaya ba sai a wani wajen shak'atawa, tun a mota take son mishi magana amma tsoron gudun da suke shek'awa ya hana bakinta bud'ewa.
Da kanshi ya fito ya bud'e mata motar. Ta fito a tsorace, bata gama tsorata ba, sai da suka fito, ya kamo hannunta cikin nashi ya rik'e, gam, ta dinga motsa hannunta da nufin ta k'wace amma ta kasa." Yana jin yadda take motsa hannun amma ya bagaras da ita, sai ma wani murmushin k'auna da yake mata... Haka bisa wajibi ta ta hak'ura, suke tafiya har suka isa wurin wasu kujeru, suka zauna.
Sunyi shiru, yayin da ita ahankali take sauke numfashi,..
Ahankali ta bud'e baki murya ak'asa tace cikin k'aguwa..
"Please Dear me, me muka zo yi nan ne?
Ya zubo mata fararen idanuwanshi, please ki kalla nan mana kowa na kulawa da babynshi amma, mu always kina had'a distance between us".. Please why?
Sai da ta sanya tunani da hankali sannan ta nemo inda zancen shi ya nufa... Alokacin tsoronta 'na ta baro Mama wajen party' ya gushe, sai taji alokacin ya dace tace wani abu da zai fahimtar da Yusuf, d'in manufarta akan soyyayyarsu.
Ta tattaro dukkan nutsuwarta, sai da ta kalleshi na fiye da mintuna 2, yayin da shima itan ya zubawa ido yana murmushin zaton yau buk'atar shi ta karb'u.
"Dear, ta furta ahankali.
Ya d'aga mata gira.
"Yess"
"I don't want to hurt you.. Don Allah mu daina maganar irin wannan relation, please let it be in our feature'..
Ya kalleta da alamar tambaya In Our feature?.. When ?
Cikin k'warin guiwa tace "I mean when we got married."
Yayi wata dariya wacce ita bata ga amfaninta ba.
"Hmm, baby you're talking about long time' let me tell you 'honest to God "I CAN'T WAIT".. So please allow me to get a solution to my self... Yai k'asa da murya, "Baby i promise to marry you but In sha Allah I will never beg you again!"..But kome ne ya faru kinsani kece kika ja...
Ta d'anyi shiru cikin nazarin maganarshi, ta kalli agogon hannunta, 5:30pm,
Ta mik'e da sauri, "Please let me go,.. "No, ki bari sai anjima mana.
Hankalinta gaba d'aya yayi can tace "No please let me go. And please dear when will you come to meet Abba"?
Yai murmushi hmm, Im afraid, but i will tell you soon."
Ya taso ya biyota ahankali suka fara tafiya..
"Baby ki karb'i wani wayar mana, i miss your goalding voice."
Ta d'anyi murmushin takaicin rashin wayarta, "No thank you dear."
Badon tsoron Abba ba babu abinda zai hanata karb'a
Ya bud'e mata motarshi, ya mata alama ta shiga.
Ta girgiza kai
"No barni na tafi"
"Please baby ki shiga na maidaki"
"No thank you.
"Ok,
"Please ki kirani idan kinje school."
"OK,
Ya rakata bakin titi, ta shiga mota sannan ya juya don shiga motarshi ya tafi.'
Tana fara tafiya a Napep d'in, taji fad'uwar gabanta ya tsananta. Allah yasa kada mama ta lura bata nan.
Tana isa ta fito ta bashi kud'in.
Ahankali take takawa, har cikin Hall d'in.
Da Amatullah ta fara cin karo, wacce ta tsoratata da cewa, "Hafsah, wai ina kika je ne? Mama sai Nemanki, take." "Innalillahi da gaske?
"Wallahi yanzu ma ta kuma fita nemanki."
Hafsah tayi shiru, amatullah ta ja hannunta suka yi ciki tana cewa, "Ansha rawa babu ke".. Har amarya da ango sunzo.
Filin rawar suka shiga 'yan matan family da samari anata chashewa."
Itama ta shiga akayi da ita, bashir ya matso dai dai kunnenta "yaya, wallahi Mama sai nemanki take, wai ina kuka fita?..nima na ganku fa!
tayi shiru kawai don bata da abin ce mishi.
Wajen mintinta 20mins, da dawowarta mama ta dawo. Tana hango ta tazo ta finciko ta, suka yi waje.
Mari Maman ta wanka mata.
"Ina kika je?
Ta rik'e kunci. Tayi shiru..
"Bazaki fad'amin ba, Mama ta fad'a tana shirin k'ara mata wani marin."
Cikin kuka ta ke mata bayani
"Banje ko ina ba"
"K'arya zaki yi min"?
Wallahi Hafsah ki shiga hankalinki zan tattaka ki anan wajen.."
Haba Amina, menene nayin hayaniya a nan wajen, ai bai dace ba."
Haba yaya wannan yarinyar idan kinga maganar da take d'akkomin sai kin tausaya min, ya zata dinga ja min laifi a wajen sa..
"Ya isa haka,.. Ta matso ta dafa kafadar Maman, kiyi ha'kuri kuje gida sai kiyi mata fad'a Allah ya shirya mana su."
Aunty Nafeesah ce 'Yayar Mama' wacce su Hafsah ke ce mata (Maman ya Nazeer,) daga ita sai baffa usman abbansu (Amatullah) sai Maman su Hafsah.
'Tana aiki ne a 'Ministry of women affairs' sannan malama ce ita a fannin addini, tana kuma da wajen gyaran jikin amare,
wanda yaranta keyi.'
Ala dole mama tayi shiru. Tana aunawa Hafsah uwar harara.
'Maman ya Nazeer, taja hannun Hafsah suka koma ciki, yayin da Mama wayar ta tayi k'ara kiran Abba ne.
"Hello"
"Ya ta dawo?
Eh, to maza ki tattarosu ku tawo.
"Tom"
Dama an kusa tashi, biki kuma yayi dad'i ga wad'anda hankalinsu ke kwance irin su 'Nasreen'
Ba Hafsah ba bashir ma yasha jinin jikinshi. Aunty Nafeesah ce tasa drivernta ya dawo dasu.'
'Hafsah dai sai rab'e tab'e take.'
Suna yin sallama ta shige d'aki.
Fatanta Allah yasa mama bata fad'awa Abba ba.'
Tana cikin bed room d'in tajiyo fad'an Abba a palour yana cewa,
"Ina take?? Ta fad'a miki inda taje?..
Mama tace cikin tsoro itama tana d'akinta..
Bata rufe baki ba, ya nufi d'akin Gadan -Gadan, Hafsah na shirin danna key taji ya banko k'ofar da k'arfi. sunayin ido biyu, ya shiga dukanta da bulalar hannunshi.
Ihu Hafsah take ba na wasa ba, saboda abba laftar ta yake sosai kamar wani k'aton yake duka..
Tana ta bashi hak'uri "Don Allah abba kayi hak'uri wallahi bazan sake ba" na shiga uku, wayyo mama, Abba, Innalillahi.."wayyo zan mutu"!!
Kamar zuga shi takeyi. Wato bakya jin magana koh? So kike ki lalace ne?, saboda kin zama 'yar kanki koh, shine har zaki dinga fita da wani, wato duk nasihar da nake miki bakiji ba ko?
Gidan uban wa kika je??
Ihu ta kuma, saki tama kasa magana sai karkarwa da muryarta take wall lahi.. Abb.. Abba"..
"Mufida har kuka ta fara tana, rik'e hannun Abba. Yaran ma sai hak'uri suke bashi.
'Mama tayi rok'on amma ina yak'i kyaleta.'
Ganin yana shirin kashe mata 'ya yasa ta yi azamar fincike ta, da karfi, tana haki muryarta na rawa take cewa, "Wallahi sai mu bar maka gidan, kashe min ita, zakayi?.. Ko me tayi ba sai ka kyaleta ba?" wasu Maganganun ma bata san tana fad'ar su ba.
Abba ya tsallake Hafsah, dake kwance shame -shame, ya fice daga d'akin ko kallon mama baiyi ba.
Cikin azama mama ta figi mayafinta da jakarta, tacewa bashir,
"Kamota mu fita da ita..
Sai gunjin kukan Hafsa kawai akeji. Ya kamata, ta mik'e da k'yar, ya rirrik'eta da k'yar take takawa, sukayi har yar gate' Mufida ta biyo su, mama zan biku"
Maman ta daka mata wata uwar tsawa daya sa ta koma babu shiri..
👏🏼👏🏼👏🏼
*Hajeeyah Kareemerh ce*
👍🏼👍🏼👍🏼
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah khareemerh)*
*Dedicated to:*
*Unique in your Love Heart Group members.*
📄 *24*