Sashe 15
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
.
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to:*
*Unique In Your Love Heart Members.*
📄 *18*
Ahankali yayi sallama, mama ta amsa tana shirin mik'ewa ta karb'i jakar shi, taga ya nufi hanyar d'akin shi, tayi mamakin hakan.
Baya shiga d'akin shi daga dawowarshi, sai dai idan suna fushi da juna..
Ta Kalli yaran hankalinsu na kan kallo. Ta mik'e a sanyaye ta bishi.
Da sallama ta shiga, yana zaune akan gadonshi ya zubawa carpet d'in d'akin ido.
Ahankali ta nemi guri kusa da shi ta zauna.
"Sannu da zuwa"
Bai mata magana ba kuma bai d'ago ba.
Ta d'an sha jinin jikinta.
Ta d'an yi shiru, Mintuna kamar biyu sai tayi tunanin ta kawo masa ruwa.
Ta mik'e kenan ta fara tafiya taji ya kirata a hankali.
"Amina!!
Ta juyo ta dawo ta zauna wajen da take da.
"Me yasa kakai min haka?
Mamaki ne ya cika ta har yasa ta bud'a baki tace
"Menayi abban..
Ya tare ta cikin b'acin rai.
"Ok me kikayi kike tambayata koh? To
zaki fahimta idan na d'auki mummunan mataki akanku!!
😳
Subhaanallah ta fad'a a hankali.
Sannan ta kwantar da murya,
Haba Abban Hafsah, don Allah kayi hak'uri, Allah ya wuci zuciyarka."
"Hmm dole ki ce haka mana, amma fa kin bani mamaki wallahi.."
"Please kayi hak'uri don Allah, ka fad'amin Meyake faruwa?
"Hum"
Kawai yace.
Sai kuma yayi wani tunani.
'Ya lura ta kasa sanin meye laifinta, shi kuma ba shi da lokacin b'atawa wajen zaman fad'amata'
Don haka yace:
"Sai ki kirata tunda ai da sanin ki takeyin komai."
Ba zata ce bata fahimci da wa yake ba don tasan da 'Hafsah yake'
Ta mik'e cikin azama ta nufi d'akin Hafsah, abinda ya so firgita ta,
'waya ta ganta tana yi.
Ta Kai mata duka, ta sami wayar ta fad'i ak'asa.
Hafsah ta juyo a razane,
Maman ta watsa mata harara sannan tace,
"Sai ki taso abbanku na nemanki"
Hafsah ta razana da jin kiran.
Tuni ita maman ta fice.
Ko hijab bata sa ba itama ta nufi d'akin Abban.
Tayi sallama ta zauna.
Bata ga fuskar gaida shi ba.
"Ke waye ya baki waya??
Tambayar taso ta ruguza kanta kamar saukar aradu haka taji tambayar.
"Da ke nake"
Abban ya fad'a yana nuna ta da yatsanshi.
Hawaye ne ya fara biyo kankuncinta.
Shikenan yau ta kad'e. wacce k'addara ce ke neman afka mata Ayau.
"Zaki yi min magana ko kuwa sai nayi ball da ke a wajen nan."
Abban ya fad'a lokacin da yake kawo mata wani bahagon duka da hannunshi.
Mama tayi azamar tare hannun nashi. Abinda ya hana dukan sauka akan fuskar Hafsah kenan. Don la shakka daya sauka da babu abinda zai hana hak'oranta zubewa.😳😂
Abba ya juyo a fusace, yana huci b'acin ranshi ya nunku, ya kalleta fuskarshi cike da b'acin rai..
👏🏼👏🏼👏🏼
*Am sorry kuyi haquri da wannan*
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to :Unique In Your Love Heart Members.*
😘😘😘😘😘😘
*Kai jama,a, ni mai zance da masoya wannan novel ne??*🤔🤔
*Sai dai in gode muku kawai*👌🏻
*INA GODIYA DA ALFAHARI DAKU INA MUKU FATAN ALKHAIRI.*
*KARIMA NAJI DAKU😇*
*ZAZZAFAN So NOVEL GROUP:*
🌹 ummu al,amen, Adam's Fudiyya, Maman affan, Ramcy, Hajara ayuba, Sarauniya Bilkisu.👏🏼👏🏼👏🏼
*UNIQUE IN YOUR LOVE HEART GROUP:*
🌹 Zeena Khalid, pure baby and the whole members👏🏼
*JIDDA TIJJANI NOVEL GROUP:*
🌹Deejah, Lawisa tanaskha, Binta musa salisu (Mamana), Maman Hanan, Nana Hauwa,u, juwaira lukman. And also Aysha Tukur (Maman Teemah and Ahmad)👏🏼👏🏼
*RAYUWAR SUMAYYA NOVEL GROUP:*
🌹 ummu muhd, bintu muhd, Habiba abdul k'adir.
*SIRRIN MU:*
🌹 Ummu hibban 'yar baba, zaujatu muhibbuha, Mrs naseer.👏🏼
*NOVEL ZAFAFA:*
🌹Mr Otu, sumyhala2017.👏🏼
*MATAN AURE NOVELS:*
🌹SUA, Zeenah Khalid, pure baybee. 👏🏼
*NIDA K'AWATA FANS:*
🌹 Nadiya sadou, S ubanduma, maman umar, Aisha ya,u.👏🏼
*KUNDIN NOVEL GROUP:*
🌹Zulaihart, Maman Hafsah, Khadeejah.👏🏼
*TAURARUWAR MACE GROUP :*
🌹Sumayya hadi and Mami boy.👏🏼
💘💘💘💘💘💖💖💖💖💖
*Am totally in love with you.. Kun gane ai*😊👏🏼👏🏼👏🏼
📄 *19*
*Kafin* yayi magana ta riga shi,
"Haba, Abban Hafsah, don Allah d'auki al,amran nan da sauk'i."
Ya kalleta da kyau.
Ta karyar da kai.
"Don Allah"
Yayi shiru sannan ya dawo ya zauna.
Ya Kalli Maman.
Kinsan da zaman wayar?
"Nasani" a ta fad'a a tausashe.
Yaji zafin hakan sosai, don me zata dinga b'oye mishi, abinda ya shafi rayuwar 'yarshi. Yaso rufeta da fad'a sai ya tuna da 'yarsu a wajen..
Ya danne axuciyarshi. Sai fushin ya koma kan Hafsah da dama Itace mai alhakin laifin."
Afusace ya kalleta Yaushe ya baki wayar,? meya sa ma kika kaishi gidan Hajiya?...Wato ni ban isa ki kawo min shi ba koh? Hafsah har kin isa ki yi abu irin wannan bada izinina ba koh?
Hawaye suka biyo kuncinanta.
Meya sameta? tabbas tasan batayi wa kanta adalci ba.
"Abba Don Allah kuyi hak'uri wallahi bazan sake ba."
"Hum, hak'uri kike bani Hafsah?? Dama shi yasa kike sakaci da karatunki koh? Kika sa wasa a zuciyarki, saboda kina yin wani shirme can koh?..
'Tashi ki d'akkomin wayar stupid!!
Ya fad'a cikin wata tsawa.
Ta mik'e a hanzarce gudun kada ya daketa ta nufi d'aki ta dakko wayar.. Har yanzu hawaye bai daina zarya a kan fuskarta ba.
Ta durk'usa ta mik'a mishi da hannu biyu, ya karb'a ya ajye a gefenshi.
Mama dai tayi shiru, don babu damar yin magana.
"Kun dad'e dashi dama ban sani ba?
Abba ya jefo mata tambayar.
Hafsah ta girgiza kai.
"Magana zaki min,"
Ya fad'a cikin tsawa.
Cikin rawar murya tace, "A,a.
Abba ya kalleta sosai,
"Kice masa yazo ina son ganinshi"
Ba Hafsah ba har Mama sai da gabanta ya fad'i. Takai kallonta ga abban, yayin da shi kuma ya k'ara tamke fuska.
Sai ma ya kalli sashin da Hafsah take.
"Tashi ki bani guri"
Ta mik'e sum sum sum ta fita.
Shiru ya mamaye d'akin sai zuciyar kowa da ke sak'e-sak'e. Shi Abba jiran cewar Mama yake yayin da itama take jiran ya sauk'le fushin akanta. Sai kuma tunanin yau yasa taji kunya a gaban 'yarta, don basu tab'a haka ba agaban 'ya'yansu.
Can taji yayi ajiyar zuciya, had'e da juyo da kallonshi b'arin da take, itama lokacin ta kalloshi sai suka had'a ido.
Ya tsaya ya kalleta sosai, kallon daya k'ara raunana zuciyarta cike yake da tuhuma da kuma mamakin abinda tayi mishi, duk ta karanta wannan a idanunshi.
Ahankali tayi k'asa da idanunta, ta dafe kanta da hannu biyu.
Yace, Cikin k'aramin sauti,
"Amina!
Taji amma ta gaza amsawa.
Shikuma yayi shiru, tasan jiran amsawarta yake.
"Amina"
Ya fad'a a karo na biyu.
Muryarta a disashe tace. "Na,am"
Bai damu da rashin d'agowarta ba, ya fara magana.
"Kin san hali na, kuma kinsani idan nace 'eh' bana cewa 'a,a."
Ya d'an yi shiru sannan ya cigaba.
"Kinsan tsari na, kuma dake mukayi magana, ban fad'a miki kada ki bari hafsah ta kula wani yaro ba?? bance miki sai tayi candy ba?
Ahankali tace
"ka Fad'a"
To meyasa kika k'i bin abinda nace?.. Ko dan bake Allah zai tuhuma ba idan ta lalace koh??
Ta girgiza kai.
"Amina me kuke so wanda bazan yi muku shi ba?"
Ya d'anyi k'asa da murya.
"Idan kina son ta rik'e waya me yasa bazaki fad'amin ba.. Sai ki goyi bayan ta k'arbi abin hannun samari koh?
"To Allah ya gani dai ban hanaku komai ba!!..
Maganar daya fad'a ta k'arshe tayi wa mama zafi, sannan ta sa ta taji 'tabbas batayi dai dai ba..
Yau mijinta ne da kanshi yake fad'a mata wai ya fita hak'k'insu??
Kwallah ta cika idanunta.
Shiko bai k'ara kallonta ba ya mik'e ya shige toilet enshi ya murza key.
Bai sake mata magana ba tun da ya fito, kuma yak'i bata damar yi mishi magana ko hak'uri ne ta bashi.
Tana son ta fita ta duba 'ya'yanta tana tsoron kada ta fita ya kulle k'ofarshi, don tasa a ranta dole anan zata kwana.
Shine ma ya mik'e ya fita, dakunan yaran yasasu yin fitsari, sannan ya dawo falo yayi zamanshi.
Shiru Mama na zuba idon dawowarshi.
Sai can wajen d'aya 1:00am sannan ya tashi ya koma d'akin.
To Kwanan ranar dai haka sukayi shi babu d'adi dai...
B'angaren Hafsah kuwa kuka take yi gurshek`e..
Abubuwa ne da yawa suka had'ar mata, na farko nadamar zama silar samun sab'anin iyayenta, domin tasan da wayonta bata tab'a ganin hakan ba gabanta, sannan bataji dad'i Abba ya kamata da laifi irin wannan ba.
Na biyu kuma jimamin k'wace wayar ta da Abban yayi.
Sai kuma babban wato tunkarar yusuf da maganar abba.
Tunani dai shiya cinye rabin darenta.
♥♥♥♥ ♥♥♥♥
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to:*
*Unique In Your Love Heart Members.*
📄 *18*
Ahankali yayi sallama, mama ta amsa tana shirin mik'ewa ta karb'i jakar shi, taga ya nufi hanyar d'akin shi, tayi mamakin hakan.
Baya shiga d'akin shi daga dawowarshi, sai dai idan suna fushi da juna..
Ta Kalli yaran hankalinsu na kan kallo. Ta mik'e a sanyaye ta bishi.
Da sallama ta shiga, yana zaune akan gadonshi ya zubawa carpet d'in d'akin ido.
Ahankali ta nemi guri kusa da shi ta zauna.
"Sannu da zuwa"
Bai mata magana ba kuma bai d'ago ba.
Ta d'an sha jinin jikinta.
Ta d'an yi shiru, Mintuna kamar biyu sai tayi tunanin ta kawo masa ruwa.
Ta mik'e kenan ta fara tafiya taji ya kirata a hankali.
"Amina!!
Ta juyo ta dawo ta zauna wajen da take da.
"Me yasa kakai min haka?
Mamaki ne ya cika ta har yasa ta bud'a baki tace
"Menayi abban..
Ya tare ta cikin b'acin rai.
"Ok me kikayi kike tambayata koh? To
zaki fahimta idan na d'auki mummunan mataki akanku!!
😳
Subhaanallah ta fad'a a hankali.
Sannan ta kwantar da murya,
Haba Abban Hafsah, don Allah kayi hak'uri, Allah ya wuci zuciyarka."
"Hmm dole ki ce haka mana, amma fa kin bani mamaki wallahi.."
"Please kayi hak'uri don Allah, ka fad'amin Meyake faruwa?
"Hum"
Kawai yace.
Sai kuma yayi wani tunani.
'Ya lura ta kasa sanin meye laifinta, shi kuma ba shi da lokacin b'atawa wajen zaman fad'amata'
Don haka yace:
"Sai ki kirata tunda ai da sanin ki takeyin komai."
Ba zata ce bata fahimci da wa yake ba don tasan da 'Hafsah yake'
Ta mik'e cikin azama ta nufi d'akin Hafsah, abinda ya so firgita ta,
'waya ta ganta tana yi.
Ta Kai mata duka, ta sami wayar ta fad'i ak'asa.
Hafsah ta juyo a razane,
Maman ta watsa mata harara sannan tace,
"Sai ki taso abbanku na nemanki"
Hafsah ta razana da jin kiran.
Tuni ita maman ta fice.
Ko hijab bata sa ba itama ta nufi d'akin Abban.
Tayi sallama ta zauna.
Bata ga fuskar gaida shi ba.
"Ke waye ya baki waya??
Tambayar taso ta ruguza kanta kamar saukar aradu haka taji tambayar.
"Da ke nake"
Abban ya fad'a yana nuna ta da yatsanshi.
Hawaye ne ya fara biyo kankuncinta.
Shikenan yau ta kad'e. wacce k'addara ce ke neman afka mata Ayau.
"Zaki yi min magana ko kuwa sai nayi ball da ke a wajen nan."
Abban ya fad'a lokacin da yake kawo mata wani bahagon duka da hannunshi.
Mama tayi azamar tare hannun nashi. Abinda ya hana dukan sauka akan fuskar Hafsah kenan. Don la shakka daya sauka da babu abinda zai hana hak'oranta zubewa.😳😂
Abba ya juyo a fusace, yana huci b'acin ranshi ya nunku, ya kalleta fuskarshi cike da b'acin rai..
👏🏼👏🏼👏🏼
*Am sorry kuyi haquri da wannan*
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to :Unique In Your Love Heart Members.*
😘😘😘😘😘😘
*Kai jama,a, ni mai zance da masoya wannan novel ne??*🤔🤔
*Sai dai in gode muku kawai*👌🏻
*INA GODIYA DA ALFAHARI DAKU INA MUKU FATAN ALKHAIRI.*
*KARIMA NAJI DAKU😇*
*ZAZZAFAN So NOVEL GROUP:*
🌹 ummu al,amen, Adam's Fudiyya, Maman affan, Ramcy, Hajara ayuba, Sarauniya Bilkisu.👏🏼👏🏼👏🏼
*UNIQUE IN YOUR LOVE HEART GROUP:*
🌹 Zeena Khalid, pure baby and the whole members👏🏼
*JIDDA TIJJANI NOVEL GROUP:*
🌹Deejah, Lawisa tanaskha, Binta musa salisu (Mamana), Maman Hanan, Nana Hauwa,u, juwaira lukman. And also Aysha Tukur (Maman Teemah and Ahmad)👏🏼👏🏼
*RAYUWAR SUMAYYA NOVEL GROUP:*
🌹 ummu muhd, bintu muhd, Habiba abdul k'adir.
*SIRRIN MU:*
🌹 Ummu hibban 'yar baba, zaujatu muhibbuha, Mrs naseer.👏🏼
*NOVEL ZAFAFA:*
🌹Mr Otu, sumyhala2017.👏🏼
*MATAN AURE NOVELS:*
🌹SUA, Zeenah Khalid, pure baybee. 👏🏼
*NIDA K'AWATA FANS:*
🌹 Nadiya sadou, S ubanduma, maman umar, Aisha ya,u.👏🏼
*KUNDIN NOVEL GROUP:*
🌹Zulaihart, Maman Hafsah, Khadeejah.👏🏼
*TAURARUWAR MACE GROUP :*
🌹Sumayya hadi and Mami boy.👏🏼
💘💘💘💘💘💖💖💖💖💖
*Am totally in love with you.. Kun gane ai*😊👏🏼👏🏼👏🏼
📄 *19*
*Kafin* yayi magana ta riga shi,
"Haba, Abban Hafsah, don Allah d'auki al,amran nan da sauk'i."
Ya kalleta da kyau.
Ta karyar da kai.
"Don Allah"
Yayi shiru sannan ya dawo ya zauna.
Ya Kalli Maman.
Kinsan da zaman wayar?
"Nasani" a ta fad'a a tausashe.
Yaji zafin hakan sosai, don me zata dinga b'oye mishi, abinda ya shafi rayuwar 'yarshi. Yaso rufeta da fad'a sai ya tuna da 'yarsu a wajen..
Ya danne axuciyarshi. Sai fushin ya koma kan Hafsah da dama Itace mai alhakin laifin."
Afusace ya kalleta Yaushe ya baki wayar,? meya sa ma kika kaishi gidan Hajiya?...Wato ni ban isa ki kawo min shi ba koh? Hafsah har kin isa ki yi abu irin wannan bada izinina ba koh?
Hawaye suka biyo kuncinanta.
Meya sameta? tabbas tasan batayi wa kanta adalci ba.
"Abba Don Allah kuyi hak'uri wallahi bazan sake ba."
"Hum, hak'uri kike bani Hafsah?? Dama shi yasa kike sakaci da karatunki koh? Kika sa wasa a zuciyarki, saboda kina yin wani shirme can koh?..
'Tashi ki d'akkomin wayar stupid!!
Ya fad'a cikin wata tsawa.
Ta mik'e a hanzarce gudun kada ya daketa ta nufi d'aki ta dakko wayar.. Har yanzu hawaye bai daina zarya a kan fuskarta ba.
Ta durk'usa ta mik'a mishi da hannu biyu, ya karb'a ya ajye a gefenshi.
Mama dai tayi shiru, don babu damar yin magana.
"Kun dad'e dashi dama ban sani ba?
Abba ya jefo mata tambayar.
Hafsah ta girgiza kai.
"Magana zaki min,"
Ya fad'a cikin tsawa.
Cikin rawar murya tace, "A,a.
Abba ya kalleta sosai,
"Kice masa yazo ina son ganinshi"
Ba Hafsah ba har Mama sai da gabanta ya fad'i. Takai kallonta ga abban, yayin da shi kuma ya k'ara tamke fuska.
Sai ma ya kalli sashin da Hafsah take.
"Tashi ki bani guri"
Ta mik'e sum sum sum ta fita.
Shiru ya mamaye d'akin sai zuciyar kowa da ke sak'e-sak'e. Shi Abba jiran cewar Mama yake yayin da itama take jiran ya sauk'le fushin akanta. Sai kuma tunanin yau yasa taji kunya a gaban 'yarta, don basu tab'a haka ba agaban 'ya'yansu.
Can taji yayi ajiyar zuciya, had'e da juyo da kallonshi b'arin da take, itama lokacin ta kalloshi sai suka had'a ido.
Ya tsaya ya kalleta sosai, kallon daya k'ara raunana zuciyarta cike yake da tuhuma da kuma mamakin abinda tayi mishi, duk ta karanta wannan a idanunshi.
Ahankali tayi k'asa da idanunta, ta dafe kanta da hannu biyu.
Yace, Cikin k'aramin sauti,
"Amina!
Taji amma ta gaza amsawa.
Shikuma yayi shiru, tasan jiran amsawarta yake.
"Amina"
Ya fad'a a karo na biyu.
Muryarta a disashe tace. "Na,am"
Bai damu da rashin d'agowarta ba, ya fara magana.
"Kin san hali na, kuma kinsani idan nace 'eh' bana cewa 'a,a."
Ya d'an yi shiru sannan ya cigaba.
"Kinsan tsari na, kuma dake mukayi magana, ban fad'a miki kada ki bari hafsah ta kula wani yaro ba?? bance miki sai tayi candy ba?
Ahankali tace
"ka Fad'a"
To meyasa kika k'i bin abinda nace?.. Ko dan bake Allah zai tuhuma ba idan ta lalace koh??
Ta girgiza kai.
"Amina me kuke so wanda bazan yi muku shi ba?"
Ya d'anyi k'asa da murya.
"Idan kina son ta rik'e waya me yasa bazaki fad'amin ba.. Sai ki goyi bayan ta k'arbi abin hannun samari koh?
"To Allah ya gani dai ban hanaku komai ba!!..
Maganar daya fad'a ta k'arshe tayi wa mama zafi, sannan ta sa ta taji 'tabbas batayi dai dai ba..
Yau mijinta ne da kanshi yake fad'a mata wai ya fita hak'k'insu??
Kwallah ta cika idanunta.
Shiko bai k'ara kallonta ba ya mik'e ya shige toilet enshi ya murza key.
Bai sake mata magana ba tun da ya fito, kuma yak'i bata damar yi mishi magana ko hak'uri ne ta bashi.
Tana son ta fita ta duba 'ya'yanta tana tsoron kada ta fita ya kulle k'ofarshi, don tasa a ranta dole anan zata kwana.
Shine ma ya mik'e ya fita, dakunan yaran yasasu yin fitsari, sannan ya dawo falo yayi zamanshi.
Shiru Mama na zuba idon dawowarshi.
Sai can wajen d'aya 1:00am sannan ya tashi ya koma d'akin.
To Kwanan ranar dai haka sukayi shi babu d'adi dai...
B'angaren Hafsah kuwa kuka take yi gurshek`e..
Abubuwa ne da yawa suka had'ar mata, na farko nadamar zama silar samun sab'anin iyayenta, domin tasan da wayonta bata tab'a ganin hakan ba gabanta, sannan bataji dad'i Abba ya kamata da laifi irin wannan ba.
Na biyu kuma jimamin k'wace wayar ta da Abban yayi.
Sai kuma babban wato tunkarar yusuf da maganar abba.
Tunani dai shiya cinye rabin darenta.
♥♥♥♥ ♥♥♥♥