← Book details Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 88

Sashe 22

Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*Sai* da safen mama tashigo tace mata, 'ta shirya zuwa makaranta. K'arfe 9:00am ne, exam d'in, don haka, da 'Nura' yazo, Abba cewa yayi ya kaisu bashir, ita idan lokacin yayi ya dawo ya kaita.
'Tunda ta jita a mota taji wani farinciki ya ziyarceta, tana son tajita cikin k'awayenta, sannan tana son ganin Basma.'
Sanda taje ana daf da shiga, saboda haka bata sami ganin Basma, ba. Kuma cikin rashin sa,a ajin da suke exam daban ne.
Suna fitowa daga 'Papper', Aysha D'ahir ta nufo ta.
Suka cafe hannu.
"H Hamid ya jiki..? Wallahi har kin rame!"
"Hafsah dai tace Da sauk'i kawai"
Ke wallahi mutuminki ya dameni, kullum sai yacemin in had'aku
a waya idan nazo school,..So na fad'a mishi baki da lafiya, ne but ya damu fa sosai"
Hafsah taji dad'in hakan har da lumshe ido,
"Oh Allah sarki My Yusuf, nima nayi missing nashi wallahi"..
"Please ki had'amu"
"Am sorry to say "Na baro wayar a gida because naga exam za,a fara, kada ayimin seizing, but don't worry in sha Allah tomorrow zan Had'aku".
Hafsah ta rungume ta "Thank you my friend!!"
Muryar Nura (Drivern su) taji, yana cewa, "Hafsah, kiyi sauri don Allah"
Ta rik'e hannun Aysha, "See you tomorrow bye"
sai taji zuciyarta ta d'an k'untata 'Ashefa yanzu ba da bane'.. (Wato abba ya bawa Nura umarnin idan tana da paper biyu, matuk'ar bazata wuce awa 4 biyar a exam ba, Nura ya jira ta tagama sanan ya dak'k'ota, wannan doka ce akanta, idan kuma ta haura lokacin gama exam yace mishi laifinshi ne'
'Haka tanaji, ta shiga mota bata sami ganin Basma, ba.'
Wasa-wasa har sunyi rabin exam d'in, amma bata sami had'uwa da Basma, sun zauna ba. Suna had'uwa a duk lokacin da ta zo su gaisa. Watarana suna d'an fara hira, ake shiga 'Exam'..
Sanan hirace irin ta group, bata samun keb'ewa da Basman, kuma mafi yawanci tana riga su basma fitowa, kuma, da Nura ya k'yalla ido, ya ganta zai ce suyi gida..'
Haka Aysha ta bata hak'urin, rashin had'ata da Yusuf, saboda ta daina zuwa da waya. Agabanta, aka k'wace ta wata... Hafsa amma kiyi ha'kuri in sha Allah gobe ki shigo da wuri zan had'aku."
Haka kuwa, akayi dama exam d'in ta karfe tara ce, kuma Abba ma yana da copy na timetable d'in, tun daga dare take shirya irin k'aryar da zatayi, abarta yau ta bi su bashir'.
Taje ta sami Abba, afalo. Saboda ita yanzu da wuya ki ganta a falo, ko yasa yaushe tana 'Bed room'.
"Abba"
"Na,am,
Ta d'an yi shiru..
"Ya akayi".
Inji Abban'
"Um, dama ance gobe mu shiga da wuri saboda, jibi, zamuyi 'Catering' ne, to wai akwai abinda malamar zata koya mana.
Ta k'arashe maganar tana kallon Abban don taga ya k'aryar tata ta karbu'?..
Abba ya kalleta sosai, ya nazarci yanayinta, sannan yace ,
"To ki shirya ku tafi da su bashir".
Tayi murmushi "Nagode, Abbah"
Har takai bakin k'ofar d'akinta yace mata,
"ki dinga yin addu,ar neman nasarar Exam d'in dai."
"To Abba"
'Ta shige d'aki'
'Cike take da farinciki, da tunanin gobe ya zata kasance da Yusuf, d'inta a waya.' Hakan ya bata damar yin ishashshen bacci mai cike da ni'imar mafarkin Yusuf, d'inta a cikinsa.'
Washe garin ranar, ta zame mata mai sa,a, wato Basma, tazo sannan ga Hafsah, cikin zumud'i ta nufi Basma ta rungume ta. "Basma Yunus!!
Basma ta d'anyi murmushi H Hamid kin b'uya,"
Wallahi, bari naje wajen Aysha Taheer, na dawo.
"Ok, Basma ta fad'a tana bin bayanta da rakiyar wani kallo'..
*"Kuyi Hak'uri please wallahi bacci nke ji"*

*Hajeeyah Kareemerh*
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔

Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to: Unique In Love Heart Members*

📄 *26*

*Tana* isa wajen Aysha suka tafa, taja hannun Aysha sukayi cikin class. Baifi mutum uku suka gani ciki ba, kasancewar, yawanci basu zo ba.
'Suka nemi wuri can baya suka zauna.
Aysha ta na danna waya take cewa,
"H. Hamid, wallahi guy enki na sonki fa, ya damu yaji muryarki, you're lucky wallahi"
'Suka tafa.'
Ta mik'a wa Hafsah wayar, "yawwa ya d'aga"
'Hafsah ta mik'e ta koma wani desk en.
'Hello'
"I miss you my baby!..
'Da kalmar daya tareta kennan.
Hafsah, taji ta cikin wata duniya mai cike da farinciki.
"Me too dear nah!"
"Baki nemana ai hafsah"
Taji dad'in kiran sunan nata da yayi har cikin zuciyarta.
Ta jingina jikin 'abin jingina' dake jikin desk d'in, babu abinda take sai murmushi.
"Am sorry dear, it's not my fault wallahi, Abbanmu ne ya hanani"..
"Hmm"
Tacigaba,
Please ka daure ka zo wajen Abba, shine zai bamu damar kasancewa tare, please I beg you" 'Ta k'arashe maganar cikin murya mai rauni.'
"Hum" Yai ajiyar zuciya. "Okey" in sha Allah but ki bari kiyi candy koh, since 10days, remained.
"OK thank youu, dear'
"Hmm, dear friend enki asked me to attend her birthday nd graduation party,..and she asked me to come with you"..
"Hum, Hafsah tayi ajiyar zuciya.' Lokaci d'aya taji ba'kin ciki da kishi sun rufe ta, wai wanne irin rainin hankali basma ke mata ne"? "What did she mean?
"Baby, kinyi shiru"
"Hmm, dear please wai mene ya sa kamin haka?
"What do I did?
"Hmm, me yasa kake yin waya da Basma, ban sani ba"?
'Ya kwantar da murya " Am sorry mai baby, I told you I just respect her.. Please zaki je party en koh"
"Noo bazani ba"
'Ta fad'a da fad'a.'
"Hmm, yai murmushi, yayi k'asa da murya "Am sorry, please kije zanzo muje dake, don Allah kinga basma is our friend"..
Ta maimaita cikin murya mai bayyana mamaki'
"Our friends,?' Hmm, let me tell you, basma is no longer my friend ehe"
"Hahh, your friend is my friend so, please calm down stop feeling jealousy, she's just a friend"
'Yayi maganar cikin dariyar da ta d'anso tafiya da ita, 'tana son dariyarshi.'
'Ta d'an share kawai ta binne kishin a k'asan zuciyarta, bata son ta b'arar musu d'an farincikin da suke ciki bayan sun dad'e cikin kewar juna'.
'Cikin shagwabar daya saba, yace, "Baby what about yours ina za,ayi namu party en"
Ta d'an hadi'ye takaicinta, da dane ai Abba abinda zai mata yana da yawa, amma yanzu bata tunanin za,ayi mata wani abu"..
"Kinyi shiru"
Yace da ita,
"Nothing, bana son party"
"Oh my baby, why?.. Mene yasa ke komai baki so?
"Hmm, babu komai, ka share kawai."
Yai ajiyar zuciya "Ok, but I will prepare something special for you"
Tayi saurin cewa thank you, but please ka barshi kawai"
"Baaby,?
"Uhum"
"Kina fushi da nine koh?
"No, ni bana fushi da kai Allah" tayi saurin fad'ar hakan'
"So meyasa kike rejecting abinda nake so"..? "Babu komai wallahi dear", ni bana son party ne "
"Ok, ya wuce'
"Yanzu yaushe zanzo ganinki?
'Tab'.. Ta fad'a a zuciyarta.
Shi ana ga-yak'i yana ga-k'ura'!!😅😅

"Hmm, sai bayan kazo kaga Abba."
"Hm okey", yace mata kawai, don ta rufe mishi baki'
"I love you" ya fad'a mata babu tsammani, taji dad'i sosai,
Me too dear"!
"Ok, sai anjima, koh, take care of yourself "
'Sai taji babu dad'i fiye da koyaushe idan suna waya yai mata sallama, da k'yar tace mishi,
"Bye bye,"
'Yai mata kiss, a wayar'
'Ta gaza cire wayar
daga kunnenta, har wata k'walla ce ta cika mata ido, sai yaushe abba zai yarda da Yusuf?
Tayi zumbur ta mik'e da ta tuna aika aikatar da Basma, tayi mata, ta mik'awa Aysha wayar, tare da cewa "Thank you sister," ta fita da sauri, tana huci, kishin Basma ya rufe ta...
'Tana zaune tana cin cake, Hafsah ta zauna gefenta tana d'an huci,
"Am Basma ina son magana dake".
Basma na ganin yanayinta itama ta d'an daure fuska, "Uhum go ahead"
'Ta fad'a batare da ta bawa zancen Hafsan muhimmanci ba.
"Me yasa kike kiran yusuf a waya? Sannan mene zaki wani gayyaceshi partynki"
Basma ta d'an gyara zama, "Am H. Hamid dama shine kike wani huci?"
"So maida wuk'ar" ta fad'a tana kaucewa hafsan hanci. Hafsah ta m
do ke hannunta,
"Kinga ki fad'a min dalili".
'Basma tayi dariya, "Nothing fa I just take him as my brother, so kuma nasan idan na gayyaceki partyn bazaki je ba, shine na fad'amishi, becouse partynma na dare ne"
"Hmm, waye ya ce miki bazani ba, kuma da kika fad'amishi shi zai sani naje,?..kinga please, kada ki k'ara kiranshi, kiyi ma delete contact enshi, Bana son irin haka ni"
Basma ta d'anji ta kaici, amma sai ta share, saboda har yanzu, ba,a zo inda take so azoba."
"Haha H. Hamid' kenan"
"Yanzu dai please kuzo partynnan ke da shi"
"Bazan zo ba" shi tunda kin gayyaceshi sai yazo ai"
"Hmm, H. Hamid, kenan, ai nasan yusuf zai zo"
"Mts, Hafsah taja tsaki sannan ta bar mata gurin.'
Basma tayi murmushi "Hmm yarinya ai dama baso nake ki zo ba yarinya"
'Yau Hafsah cikin nishad'i ta yini a gida, har da taya mama aiki. Mama taji, dad'in hakan har tana mata nasiha'..
"_Hafsah dama babu, wanda ya sauya miki a cikin gidannan amma duk kinbi kin damu kanki kin daina shiga cikin 'yan uwanki,.. ??_ _Mufa iyayenki ne, idan bamu miki fad'a ba wane zai miki, Don Allah ki gyara rayuwarki, ki daina abinda kike yi kinji"._
Chapter 22 · 0% Book details