Sashe 49
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
*Tun* bayan da Fateema ta koma d'akin babu wanda yace wa wani komai tsakanin ta da Hafsah, kowa na sak'awa yana kwancewa Hafsah zantukan mama da ta d`auke su marasa yuwuwa ke mata yawo, Fateema ma, su d'inne dai. _"Mene zai sa ace Hafsah ta cigaba da kulashi."?_
Shirun ya d`auke su lokaci mai tsaho, kafin Hafsah ta nemi guri ta kwanta don gani takeyi gwara ta k'irk'iro bacci, da zaman juya kalaman mama arai, masu tada hankali.
Da safe, ta tashi sakayau, babu wani _tension._ don ta sama wa kanta mafita, kawai gwara tayi watsi da abubuwan da mama ta fad'a mata ta manta kawai da ta fad'a mata su ta maida hankali akan dawo da Yusuf cikin rayuwarta, la-allah ko mama ta gane, abinda take fad'an zai faru ba faruwar zaiyi ba.
"Hafsah ta sawa ranta yiwa yusuf uzuri cikin abinda ya faru, da tasirin tuno maganganun shi.. _"Dama na fada miki duk abinda ya faru ke kika jawo.!!_
_Banyi miki cin amanar rabuwa da ke ba.!!_
To in dai kuwa hakane, ashe ita ce ta nisanta kanta dashi kenan,? Tana son dawo dashi cikin rayuwarta ba don ta biye mishi akan abinda yake so ba, sai dai da nufin, nusar dashi ya gane abinda yake nufin suyi, ba shine abinyi yanzu ba a wajenta. Abin mamaki kuma sai take yiwa kanta fatan samin nasara mai kama da yak'ini. Ta manta da cewa wanda yayi nisa baya jin kira, kuma mutum baya sauyawa lokacin d'aya, sannan Yusuf kallon da yake yiwa rayuwa da banbanci da irin nata kallon.
_Akwai aiki a gabana."_
Ta fada a zuciyarta tuno cewa bata san ma ta yaya zata fara jawo yusuf d'inba su dawo ma kamar da. Kafin azo ga batun chanja mishi ra,ayi.
Duk wata hanya an toshe, bata da damar kulashi, an hanata fita, gashi bata da waya, sannan tana kunyar ta k'ara aron wayar Fateema. Amma kuma gefen zuciyarta na bata kwarin gwiwa.
_"Hafsah kunyar Fateema ne zata sa kiyi sakacin da zaki rasa farin ciki."? Baki da isashshen lokaci fah"_
Ta ke taji cewa a zuciyarta, zata iya tambayar Fateema waya, tunda tana da yak'inin ba zata iya hanata ba, toh amma kuma idan ta sanarwa mama fah."?
_"Ki rok'eta akan ta rufa miki asiri.!_
wata zuciyar ta raya mata.
Wannan tunanin shine ya dinga yawo a zuciyarta har tsahon kwana biyu.
Abinda Hafsah bata sani ba shine, Basma har text messages, ta turo a layin Fateema, da taji shuru Hafsah bata zo inda tace su had'u ba.
_"Hmm, dama nasan bazaki iya ba, hmm ke kin isa dama ki ja da Basma Yunus."?_
Sai da _text_ d`in yayi wajen kwana uku, sannan Fateema taga ya dace tayi mata _reply_ ba tare da ta sanarwa da Hafsa zancen _sms_ d`in ba don gani take yin hakan ma kamar iza wuta ne, amma kuma yarinyar bata chanchanci ayi mata shuru ba, don kada ta zaci ana tsoron ta ne.
Saboda haka da zuciya cike da kishi irin na 'yan uwantaka, Fateema ta rubuta _reply_ a zuwan Hafsah ce.
_"Ai idan kika ga mutum na tsintar abinda ke k`asa, to ya rasa mai zai ci ne, daga ke har shi kunyi min kad'an in zauna ina bibiyar k'azamar rayuwarku, ke dai da bakya ramin kanki sai kije kiji ta cusa kai da zubar da mutunci, ni nafi k'arfi d'aga murya akan abinda kika kula, don bansaki a layin mutane ba bare na zauna damuwa da abinda kika damu dashi, ai ke duk abinda zai burge ki to expired neh..masu hankali bazasu shinshina ba.. To kije ku qaraci k'azamar rayuwarku ni na wuce ajin kulaku dukanku._
Kalaman sunyi matuk'ar zafi a zuciyar Basma, ita da taso suyi ta jan zaren, tayi ta k'onawa Hafsah rai, amma ta sakar mata, anya kuwa ba karfin hali H. Hamid tayi ba.. Ya zaayi, ma tace Yusuf ya zama _useless_ a wajenta, bayan basma tafi kowa sanin irin son da Hafsah keyi wa yusuf d`in.
_"Kai k'arya kike kawai kinji ba zaki iya yakin bane saboda anfi karfinki. Dole ki rungumi sorry_
Abinda Basma ta aiko dashi kenan, zuciyar ta cike da zafin kalaman da aka aiko mata, _bansaki a layin mutane ba."_
Wato ana nufin ita dabba ce kenan.
" _Haha..ni fa na fad`amiki yusuf bola ce wacce nayar kika d`auka banda hakanw bazaki tab`a iya winning d`in heart dinshi ba yanzu ma da kike kurin, koda ace tabbas kwatuwa yayi daga wajena, ki tuna da yadda kika kwace shi mana, siya kikayi da mutuncin ki, kika maida kanki qaramar karuwa ko kin manta..."? Kuma n fad'a miki ki jira randa abinda kika tsinta zai tsere miki.!!_
Fateema ce tayi reply da haka. Kan Basma ya kulle, anya kuwa H. Hamid ce zata iya turo wad`annan kalaman, yarinyar da tasan ta da tsoro, wata zuciyar tace, zata iya fin haka ma, tunda kinfi kowa sanin me kikayi mata, kuma ai dama shiru-shuru ce, irinsu kuwa babu mai sanin zurfin cikinsu.
Kalmomin sun mata zafi ta rasa martanin mayarwa, sai kawai tahau turo da zage-zage Fateema ta ga asarar ta barta don haka ta tura mata reply d`in qarshe da nufin tayi block d`inta.
_Kanki ake ji..kuma nasan rashin abinyi ne yasa kike ta zagi haka, kedai kiji da asarar da kikayi, zagi kuma kanki kika zaga, kar ki k'ara turo min da text don bani da wata alaqa dake if not kuma...Hmm._
Tana kokarin yin block kira na shigowa ta katse kiran tare da yin block na number.
Fateema ta lura da yawan kallonta da Hafsah keyi da alama akwai magana a bakinta.
"Meya faru ne Hafsah."
Tayi ajiyar zuciya sannan ta fara 'yan soshe-soshe.. "Um Fateema da.. dama don Allah waya zaki ara min in..kira."
Tayi ta rarraba zancen kamar me tsoron tambaya.
"Wa zaki kira."
Fateema ta tambayeta kai tsaye.
"Don Allah ki ara min so nake na tabbatar da wani abu."
Me zaki tabbatar."?
Nidai ki fad'amin wanda zaki kira."
Cikin matsuwa take, don haka ta muskuta.. "Don Allah kada ki fada wa mama na ari waya."
"A,a ni nace ki fadamin wanda zaki kira mana."?
"Nidai kiyi alk'awari bazaki fada mata ba.
"Hmm, to meye idan ta sani, nidai ki fada kawai."
Hafsah ta k'ara cewa "Don Allah, kinji."
"To naji, ki fad`amin wanene."?
:Da gaske ba zaki fad'awa mama ba."
Hafsah ta tambaya tana murmushi so take ta k'ara tabbatar wa don gudun matsala.
"Kaii wai so kike na rantse neh, Allah bazan fada mata ba, Shikenan?."
Hafsah ta rungumeta "Thank you sister.!!
A kunyace tayi k'asa da murya tace, "Shi zan kira."
"Hmm", inji Fateema.
Don ta yarda Hafsah ta shiga koro jawabin kariya.
"Kinga dai nice ban neme shi ba shiyasa, gashi bashi da hanyar nema na."
"Hmm, gaskiya.!!"
Cewar Fateema kuma da yake itama tana son a kira d`in don taga k'arshen _game_ d`in sai ta bada wayar.
"Ungo, amma with one condition."
Hafsah ta amsa cikin zumudi tana zaro ido. Mene."?
"Zaki sa wayar a hands-free naji."
Ita dai Hafsah _buk'atar maje hajji sallah_ don haka tayi saurin jinjina kai alamar yarda.
Shirun ya d`auke su lokaci mai tsaho, kafin Hafsah ta nemi guri ta kwanta don gani takeyi gwara ta k'irk'iro bacci, da zaman juya kalaman mama arai, masu tada hankali.
Da safe, ta tashi sakayau, babu wani _tension._ don ta sama wa kanta mafita, kawai gwara tayi watsi da abubuwan da mama ta fad'a mata ta manta kawai da ta fad'a mata su ta maida hankali akan dawo da Yusuf cikin rayuwarta, la-allah ko mama ta gane, abinda take fad'an zai faru ba faruwar zaiyi ba.
"Hafsah ta sawa ranta yiwa yusuf uzuri cikin abinda ya faru, da tasirin tuno maganganun shi.. _"Dama na fada miki duk abinda ya faru ke kika jawo.!!_
_Banyi miki cin amanar rabuwa da ke ba.!!_
To in dai kuwa hakane, ashe ita ce ta nisanta kanta dashi kenan,? Tana son dawo dashi cikin rayuwarta ba don ta biye mishi akan abinda yake so ba, sai dai da nufin, nusar dashi ya gane abinda yake nufin suyi, ba shine abinyi yanzu ba a wajenta. Abin mamaki kuma sai take yiwa kanta fatan samin nasara mai kama da yak'ini. Ta manta da cewa wanda yayi nisa baya jin kira, kuma mutum baya sauyawa lokacin d'aya, sannan Yusuf kallon da yake yiwa rayuwa da banbanci da irin nata kallon.
_Akwai aiki a gabana."_
Ta fada a zuciyarta tuno cewa bata san ma ta yaya zata fara jawo yusuf d'inba su dawo ma kamar da. Kafin azo ga batun chanja mishi ra,ayi.
Duk wata hanya an toshe, bata da damar kulashi, an hanata fita, gashi bata da waya, sannan tana kunyar ta k'ara aron wayar Fateema. Amma kuma gefen zuciyarta na bata kwarin gwiwa.
_"Hafsah kunyar Fateema ne zata sa kiyi sakacin da zaki rasa farin ciki."? Baki da isashshen lokaci fah"_
Ta ke taji cewa a zuciyarta, zata iya tambayar Fateema waya, tunda tana da yak'inin ba zata iya hanata ba, toh amma kuma idan ta sanarwa mama fah."?
_"Ki rok'eta akan ta rufa miki asiri.!_
wata zuciyar ta raya mata.
Wannan tunanin shine ya dinga yawo a zuciyarta har tsahon kwana biyu.
Abinda Hafsah bata sani ba shine, Basma har text messages, ta turo a layin Fateema, da taji shuru Hafsah bata zo inda tace su had'u ba.
_"Hmm, dama nasan bazaki iya ba, hmm ke kin isa dama ki ja da Basma Yunus."?_
Sai da _text_ d`in yayi wajen kwana uku, sannan Fateema taga ya dace tayi mata _reply_ ba tare da ta sanarwa da Hafsa zancen _sms_ d`in ba don gani take yin hakan ma kamar iza wuta ne, amma kuma yarinyar bata chanchanci ayi mata shuru ba, don kada ta zaci ana tsoron ta ne.
Saboda haka da zuciya cike da kishi irin na 'yan uwantaka, Fateema ta rubuta _reply_ a zuwan Hafsah ce.
_"Ai idan kika ga mutum na tsintar abinda ke k`asa, to ya rasa mai zai ci ne, daga ke har shi kunyi min kad'an in zauna ina bibiyar k'azamar rayuwarku, ke dai da bakya ramin kanki sai kije kiji ta cusa kai da zubar da mutunci, ni nafi k'arfi d'aga murya akan abinda kika kula, don bansaki a layin mutane ba bare na zauna damuwa da abinda kika damu dashi, ai ke duk abinda zai burge ki to expired neh..masu hankali bazasu shinshina ba.. To kije ku qaraci k'azamar rayuwarku ni na wuce ajin kulaku dukanku._
Kalaman sunyi matuk'ar zafi a zuciyar Basma, ita da taso suyi ta jan zaren, tayi ta k'onawa Hafsah rai, amma ta sakar mata, anya kuwa ba karfin hali H. Hamid tayi ba.. Ya zaayi, ma tace Yusuf ya zama _useless_ a wajenta, bayan basma tafi kowa sanin irin son da Hafsah keyi wa yusuf d`in.
_"Kai k'arya kike kawai kinji ba zaki iya yakin bane saboda anfi karfinki. Dole ki rungumi sorry_
Abinda Basma ta aiko dashi kenan, zuciyar ta cike da zafin kalaman da aka aiko mata, _bansaki a layin mutane ba."_
Wato ana nufin ita dabba ce kenan.
" _Haha..ni fa na fad`amiki yusuf bola ce wacce nayar kika d`auka banda hakanw bazaki tab`a iya winning d`in heart dinshi ba yanzu ma da kike kurin, koda ace tabbas kwatuwa yayi daga wajena, ki tuna da yadda kika kwace shi mana, siya kikayi da mutuncin ki, kika maida kanki qaramar karuwa ko kin manta..."? Kuma n fad'a miki ki jira randa abinda kika tsinta zai tsere miki.!!_
Fateema ce tayi reply da haka. Kan Basma ya kulle, anya kuwa H. Hamid ce zata iya turo wad`annan kalaman, yarinyar da tasan ta da tsoro, wata zuciyar tace, zata iya fin haka ma, tunda kinfi kowa sanin me kikayi mata, kuma ai dama shiru-shuru ce, irinsu kuwa babu mai sanin zurfin cikinsu.
Kalmomin sun mata zafi ta rasa martanin mayarwa, sai kawai tahau turo da zage-zage Fateema ta ga asarar ta barta don haka ta tura mata reply d`in qarshe da nufin tayi block d`inta.
_Kanki ake ji..kuma nasan rashin abinyi ne yasa kike ta zagi haka, kedai kiji da asarar da kikayi, zagi kuma kanki kika zaga, kar ki k'ara turo min da text don bani da wata alaqa dake if not kuma...Hmm._
Tana kokarin yin block kira na shigowa ta katse kiran tare da yin block na number.
Fateema ta lura da yawan kallonta da Hafsah keyi da alama akwai magana a bakinta.
"Meya faru ne Hafsah."
Tayi ajiyar zuciya sannan ta fara 'yan soshe-soshe.. "Um Fateema da.. dama don Allah waya zaki ara min in..kira."
Tayi ta rarraba zancen kamar me tsoron tambaya.
"Wa zaki kira."
Fateema ta tambayeta kai tsaye.
"Don Allah ki ara min so nake na tabbatar da wani abu."
Me zaki tabbatar."?
Nidai ki fad'amin wanda zaki kira."
Cikin matsuwa take, don haka ta muskuta.. "Don Allah kada ki fada wa mama na ari waya."
"A,a ni nace ki fadamin wanda zaki kira mana."?
"Nidai kiyi alk'awari bazaki fada mata ba.
"Hmm, to meye idan ta sani, nidai ki fada kawai."
Hafsah ta k'ara cewa "Don Allah, kinji."
"To naji, ki fad`amin wanene."?
:Da gaske ba zaki fad'awa mama ba."
Hafsah ta tambaya tana murmushi so take ta k'ara tabbatar wa don gudun matsala.
"Kaii wai so kike na rantse neh, Allah bazan fada mata ba, Shikenan?."
Hafsah ta rungumeta "Thank you sister.!!
A kunyace tayi k'asa da murya tace, "Shi zan kira."
"Hmm", inji Fateema.
Don ta yarda Hafsah ta shiga koro jawabin kariya.
"Kinga dai nice ban neme shi ba shiyasa, gashi bashi da hanyar nema na."
"Hmm, gaskiya.!!"
Cewar Fateema kuma da yake itama tana son a kira d`in don taga k'arshen _game_ d`in sai ta bada wayar.
"Ungo, amma with one condition."
Hafsah ta amsa cikin zumudi tana zaro ido. Mene."?
"Zaki sa wayar a hands-free naji."
Ita dai Hafsah _buk'atar maje hajji sallah_ don haka tayi saurin jinjina kai alamar yarda.