Sashe 86
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shine tafiyar da na sanar miki zanyi rakiya. sai dai kash mun shirya komai amma Allah bai nufa ba aunty ta rasu bisa wani hats ari da tayi a motar ta bayan ta fita babu jimawa na samu labari kamar a mafarki.
Jamila ta rushe da wani irin kuka mara misaltuwa. Sai da tayi mai isarta kafin tayi shuru wanda har Hafsah itama sai da ta share hawaye.
Hafsah a lokacin na rasa mutane biyu uwar dakina da kawata Samha wacce akace wata iriyar cuta ce ta kashe ta. Duk da ina ganin kamar nayiwa Samha butulci amma ita ta Nemo ni har take nuna min ko in kula kan gudar ta da nayi sai dai tace min. "Ai Jamila ko ina kika shiga sai na gano ki." Wato kin gama gadin gidan magajiyar shine kika dawo nan."?
Karaf a kunnen aunty ranar kuwa ta mata tatas ni kaina tun lokacin nake shakkar aunty domin ban dade gidanta ba hakan ta faru..
Hafsah rayuwata ta shiga garari yanxu haka babana yana kwance rai a hannun Allah dawowa ta gida ta kara kwantar dashi duk da yayi ikrarin cewa ya yafemin domin korata bai mishi amfani ba. Nima don da karar tsanata da aka dasa mishi a zuciyarsa ne. Domin bayan ni yayyena wanda muke uba daya har shegu biyu suka ajiye mishi acikin gidanshi kuma babu yadda ya iya dasu dole duka suna gidan.
Hafsah nayi mamaki dana ganki ba kiyi aure ba kema kuma banyi murna da hakan ba ina Yusuf din."?
Da sauri Hafsah ta mata nuni kan tayi shuru don bata son ko jin sunan Yusuf.
Jamila ta girgiza kai ta d'ora.
Hafsah wallahi aure nake so shine kawai burina.. saboda sam ban amfani rayuwata ba na rasa yadda akayi rayuwata ta zama haka bane cika koda daya da yaga cikin burikana ba..
Hafsah nayi asara dayawa a rayuwa ta..aure kawai nake son yi shine zan san na ribaci kuruciya ta sai dai ina tunanin ko za'a barni nayi Auren."? Duk da bani da wani tsayayye da zance yana sona da aure.
Hafsah ta numfasa. Ki yi hakuri ki daina kallon ayuwarki a baya kowa da irin yadda aka tsara mishi rayuwa Allah yana sane dake ki gode masa domin kinfi wasu."
Jamila cikin hawaye tace Allah Hafsah banyi irin k'azamar rayuwar da mutane ke zargi na ba imma hakan ne a farkon bari na gida ne amma kada ki so kiga yadda mutane suke kallo na."!
Hafsah tayi shuru Allah yaso bata zargi Jamila ba ita dai tasan bata gidansu kuma koda ta bawa Ukhasha labarin ta ce mishi tayi "tabar garin ne zuwa wajen dangin mahaifiyarta.
Bata soma fada mishi cewa Jamila garari ta dinga yi ba ko dan k'are nata mutuncin.. Domin maza akwai zargi.
Sunyi jugum Hafsah na bawa Jamila baki kan ta tsananta da addu'a. Bayan nan Jamila ta dame ta da zancen Yusuf ta damu ta bata labarin rabuwar su.
Da kyar Hafsah ta mata a takaice kawai ta nuna mata Abbanta ne ya rabasu saboda karatu kinsan dama lokacin bana kula kowa.
Jamila ta girgiza kai Allah sarki kuma yayi aure koh."?
Hafsah ta girgiza kai bansani ba gaskiya bani da alaqa dashi yanxu.
Jamila ta fahimci Hafsah bata son zancen don haka tabar zancen sukayi shuru. Inda Hafsah taga dacewar ta je ta duba baban Jamila don ko ba komai uba uba ne don haka tace. In sha Allah gobe zanzo duba Baban.
Jamila ta nuna jin dadin ta.
Hafsah tasan sai tayi magiya Sannan mama zata barta don haka tace sai gobe.
Tana son sanarwa Jamila batun bikinta amma kuma tana jin nauyi don haka fa bari sai abu ya matso sosai..
Ita ta raka jamila har waje sannan ta dawo jiki a sanyaye tana tararrabin yadda rayuwar Jamila ta kasance kuma tana k'ara gode wa Allah..
🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚
Kwanci tashi babu wuya a wajen Allah yau bikin Hafsah da Ukhasha ya rage saura wata daya da sati biyu.
Sun sha gaisawa da Hajiyarshi a waya haka
Wata rana idan zai zo yakan zo mata da "Najwa" Tayi ta sa Hafsah dariya tayi ta bata labarin su ya Fadwa da yadda suke tsokanar Ukhashatu.
Mama ta d'auke ta takanas ta maida ta gidan Hajiya Nafisa wato maman ya Nazeer.
Komai da ya dace maman tayi mata sosai Hafsah sai taji rayuwar da tayi agidan da gwagwarmayar da mama ta sha da ita ya dawo mata sabo kamar yanzu. Ita da kanta sai tayi ta dariya ita kadai tana qara gode wa Allah.
Takan yi wani tunani wato 'komai dai da lokacin shi.' Idan taga yadda ya'yan Nazeer su biyu suke cika gidan da hayaniya. Da tuni fa yaranta ne. Sai tayi saurin kwab'ar kanta "Kada ki zama mara godiyar Allah Hafsah kowa da wanda Allah ya rubuta zai aura a rayuwa.
Amma tana tuno Ukhashatunta da yadda yake sai taji wani farinciki mara misaltuwa har ta _kirashi da daya tamkar da dubu!!_
Tanajin kunyar mama yadda take zaunar da ita tana koya mata abubuwa babu wata shakka.
Ya zame mata dabi'a kullum kafin su fara gyaran jiki sai tayi mata nasiha da nusar da ita yadda rayuwar aure take.
Takan fada mata ko yaushe.
_Rayuwar aure wata iriyar rayuwa ce wacce ba zaki taba gane ya take ba har sai kinyi ta. Tana da matuk'ar dadi sannan akwai wahala da kalubale acikin ta amma idan har kika saka hak'uri komai zaki same shi da sauki._ Ita zaman ibada ne dole ki hadu da abubuwa masu dadi da kuma akasinsa. Amma matuk'ar kika sa aranki ibada kike to zaki sami komai da sauk'i.
_Kuskure da yanmata kuke yi shine kunfi fifita soyayya akan komai cikin rayuwar aure._
_Duk da tabbas itace ginshiki amma kuma hak'uri da biyayya sune makaman yaki da kowacce irin fitina._
Ina son ki rike abubuwan nan da zan fada miki.
Ki rike tsafta da kamshi
Sai kuma ki zama mai ka mun kai da biyayya kada ki zama mai girman kai ga mijinki.
Hafsah ta koyi abubuwa cikin sati hud'un da tayi tun daga girke girke data k'ara gogewa dasu sai kuma dabarun zama da miji da zamantakewar rayuwa ita kanta. Adduoi kuwa kullum cikin yin su take babu dare babu rana.
Bata iya sanarwa da Ukhashatu cewa bata gida ba saboda nauyinshi da take ji sai dai idan ya nuna yana son ganinta ta bashi uzuri. Ya k'osa sosai har yake fad'a mata.
"Don Allah ayi hakuri amarya adaina jamin rai ina son ganinka Allah."
Babu abinda take mishi sai dariya wanda da ya gaji sai ya sami lokaci yaje gidan.
Mufida ce ta fada mishi tana Kabuga.
Ya dawo gida asanyaye.
Yana dawowar kuwa ya kirata.
Tana dagawa taji yanayin shi kamar ba shi ba.
"Kin kyauta nagode."
Take tasha jinin jikanta.
Cike da fargaba tace hubby me ya faru kuma."?
"Hmm baki sani ba."?
Um."
Tace dashi.
Okey ya wuce nagode kawai.!!
Tayi shuru tana tunani me tayi toh."?
Sai ta marairaice.
Please Dear meya faru ne."?
"Hmm nace miki babu komai fah."
Please ta sake cewa.
Wai da gaske kike baki ce san me kikayi ba."
Murya cike da rauni tace.
Allah bansani ba I'm sorry plz tell me."
Ya danja dogon numfashi sannan yace.
"Meyasa zaki je unguwa baki sanar min ba."?
Take annurin fuskar ta ya dawo tace cikin shagwaba.
"Dear mama ne fa ta aikani sati na daya ma tace sai biki saura sati biyu na dawo."?
"What.. ina kika je haka ya fada a tsorace."
Abin ya bata dariya har tayi ta afili sannan tace "ina Kabuga gidan Yayar Mum dinmu.
"Hmm baki fad'a mini ba koh."?
I'm sorryy luv."
Ban hak'ura ba.
Tace plzzz"!!
Ya d'anyi shuru kafin yace.
To fad'amin me kikaje yi haka da har zaki dade kuma baki fad'a min ba."?
Hafsah ta bude baki sannan ta rufe kafin ta lalubi abincewa don bata son tayi b'aran b'arama.
Dear sallama naje mata fa.
"Hmm kuma har 1month koh."?
"Oh my God!! ta fada a zuciyarta. Yau na gamu da dan Jarida.
Dearrrh!!
Ta ja sunan kamar ta k'osa.
Shima yace uhum."?
Na zauna gidan fa da so mum bazata bari na yi kwanaki kadan ba.
"Okeyy shima yace.
Yaushe zan ganki toh plzzz kada ki hanani ganinki nayi missing dinki so bad dear plzzz"
Tayi mishi yar dariya.
"Really fah kike min dariya dama ke baki damu ba koh."?
ta shagwabe tace "Noo Dear.!!
"Umm bawani nan..in zo gobe ba don hali na ba."?
Tomorrow!!?
Yess"
Yace.
"Ka bari sai day after goben."
"Ok" yace mata sannan yayi dif.
Tasan fushi yayi don haka ta mishi dariya itama.
"I'm joking Dear kaxo goben kaji nima inason ganinka.
Ukhashatu ya lumshe ido saboda jin dadi.
"Thank you WiFi.
"U wlcm Data.!!
Tace mishi.
Suka sheke da dariya "Hmm ke koh..??
"Me kike so in taho miki dashi.
Ta girgiza kai kamar yana ganinta. "Nothing Dear.
"Ban yarda ba."
Tayi murmushi "Okey You You and You.!!
Yayi murmurshin jin dad'i "Amarya me wayo.!!
"Come with you alone." Ta sake fad'a.
Ya kara darawa "Nak'i din."
"Idan kukazo ba yanda nace ba zaku koma.!! tace.
Lokacin kuma tajiyo mama na kiranta sai lokacin ta tuna girki take duk da dama su aiki amma Mama sata take don ta saba sosai.
"Mum na kirana byee.
"Ok dear kije ki gaida mum."
__________________________
Biki saura sati biyu Basheer ya dira. Duk wasu shirye shirye sun tsara shi babu tsawwalawa saboda amaryar da angon basu san bid'a. Duk wani wanda ya dace yasan da bikin zuwa lokacin ya sani. Hafsah ta tura katinan gayyata ga contact d'inta.
Kowa na mata fatan alkhairi. Musamman Aysha Daheer dake da 'yaya biyu a lokacin. Su Nasreen sune organisers na komai.
Za'ayi kamu ne had'i da kauye Day sai Dinner sai kuma mother's eve. Ranar asabar k/ amarya.
Banda murnar Abbah data fi ta mama fitowa fili ita saboda kunya. Babu wanda za'ace yafi kowa farinciki da bikin kamar Basheer.
Har siyayya yayo wa Yayarshi da kudin shi shima a tashi bidi'ar ya kirkiro da wani event Arabian night."
Dole aka saka shi a manhaja.
Jamila ta rushe da wani irin kuka mara misaltuwa. Sai da tayi mai isarta kafin tayi shuru wanda har Hafsah itama sai da ta share hawaye.
Hafsah a lokacin na rasa mutane biyu uwar dakina da kawata Samha wacce akace wata iriyar cuta ce ta kashe ta. Duk da ina ganin kamar nayiwa Samha butulci amma ita ta Nemo ni har take nuna min ko in kula kan gudar ta da nayi sai dai tace min. "Ai Jamila ko ina kika shiga sai na gano ki." Wato kin gama gadin gidan magajiyar shine kika dawo nan."?
Karaf a kunnen aunty ranar kuwa ta mata tatas ni kaina tun lokacin nake shakkar aunty domin ban dade gidanta ba hakan ta faru..
Hafsah rayuwata ta shiga garari yanxu haka babana yana kwance rai a hannun Allah dawowa ta gida ta kara kwantar dashi duk da yayi ikrarin cewa ya yafemin domin korata bai mishi amfani ba. Nima don da karar tsanata da aka dasa mishi a zuciyarsa ne. Domin bayan ni yayyena wanda muke uba daya har shegu biyu suka ajiye mishi acikin gidanshi kuma babu yadda ya iya dasu dole duka suna gidan.
Hafsah nayi mamaki dana ganki ba kiyi aure ba kema kuma banyi murna da hakan ba ina Yusuf din."?
Da sauri Hafsah ta mata nuni kan tayi shuru don bata son ko jin sunan Yusuf.
Jamila ta girgiza kai ta d'ora.
Hafsah wallahi aure nake so shine kawai burina.. saboda sam ban amfani rayuwata ba na rasa yadda akayi rayuwata ta zama haka bane cika koda daya da yaga cikin burikana ba..
Hafsah nayi asara dayawa a rayuwa ta..aure kawai nake son yi shine zan san na ribaci kuruciya ta sai dai ina tunanin ko za'a barni nayi Auren."? Duk da bani da wani tsayayye da zance yana sona da aure.
Hafsah ta numfasa. Ki yi hakuri ki daina kallon ayuwarki a baya kowa da irin yadda aka tsara mishi rayuwa Allah yana sane dake ki gode masa domin kinfi wasu."
Jamila cikin hawaye tace Allah Hafsah banyi irin k'azamar rayuwar da mutane ke zargi na ba imma hakan ne a farkon bari na gida ne amma kada ki so kiga yadda mutane suke kallo na."!
Hafsah tayi shuru Allah yaso bata zargi Jamila ba ita dai tasan bata gidansu kuma koda ta bawa Ukhasha labarin ta ce mishi tayi "tabar garin ne zuwa wajen dangin mahaifiyarta.
Bata soma fada mishi cewa Jamila garari ta dinga yi ba ko dan k'are nata mutuncin.. Domin maza akwai zargi.
Sunyi jugum Hafsah na bawa Jamila baki kan ta tsananta da addu'a. Bayan nan Jamila ta dame ta da zancen Yusuf ta damu ta bata labarin rabuwar su.
Da kyar Hafsah ta mata a takaice kawai ta nuna mata Abbanta ne ya rabasu saboda karatu kinsan dama lokacin bana kula kowa.
Jamila ta girgiza kai Allah sarki kuma yayi aure koh."?
Hafsah ta girgiza kai bansani ba gaskiya bani da alaqa dashi yanxu.
Jamila ta fahimci Hafsah bata son zancen don haka tabar zancen sukayi shuru. Inda Hafsah taga dacewar ta je ta duba baban Jamila don ko ba komai uba uba ne don haka tace. In sha Allah gobe zanzo duba Baban.
Jamila ta nuna jin dadin ta.
Hafsah tasan sai tayi magiya Sannan mama zata barta don haka tace sai gobe.
Tana son sanarwa Jamila batun bikinta amma kuma tana jin nauyi don haka fa bari sai abu ya matso sosai..
Ita ta raka jamila har waje sannan ta dawo jiki a sanyaye tana tararrabin yadda rayuwar Jamila ta kasance kuma tana k'ara gode wa Allah..
🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚🔚
Kwanci tashi babu wuya a wajen Allah yau bikin Hafsah da Ukhasha ya rage saura wata daya da sati biyu.
Sun sha gaisawa da Hajiyarshi a waya haka
Wata rana idan zai zo yakan zo mata da "Najwa" Tayi ta sa Hafsah dariya tayi ta bata labarin su ya Fadwa da yadda suke tsokanar Ukhashatu.
Mama ta d'auke ta takanas ta maida ta gidan Hajiya Nafisa wato maman ya Nazeer.
Komai da ya dace maman tayi mata sosai Hafsah sai taji rayuwar da tayi agidan da gwagwarmayar da mama ta sha da ita ya dawo mata sabo kamar yanzu. Ita da kanta sai tayi ta dariya ita kadai tana qara gode wa Allah.
Takan yi wani tunani wato 'komai dai da lokacin shi.' Idan taga yadda ya'yan Nazeer su biyu suke cika gidan da hayaniya. Da tuni fa yaranta ne. Sai tayi saurin kwab'ar kanta "Kada ki zama mara godiyar Allah Hafsah kowa da wanda Allah ya rubuta zai aura a rayuwa.
Amma tana tuno Ukhashatunta da yadda yake sai taji wani farinciki mara misaltuwa har ta _kirashi da daya tamkar da dubu!!_
Tanajin kunyar mama yadda take zaunar da ita tana koya mata abubuwa babu wata shakka.
Ya zame mata dabi'a kullum kafin su fara gyaran jiki sai tayi mata nasiha da nusar da ita yadda rayuwar aure take.
Takan fada mata ko yaushe.
_Rayuwar aure wata iriyar rayuwa ce wacce ba zaki taba gane ya take ba har sai kinyi ta. Tana da matuk'ar dadi sannan akwai wahala da kalubale acikin ta amma idan har kika saka hak'uri komai zaki same shi da sauki._ Ita zaman ibada ne dole ki hadu da abubuwa masu dadi da kuma akasinsa. Amma matuk'ar kika sa aranki ibada kike to zaki sami komai da sauk'i.
_Kuskure da yanmata kuke yi shine kunfi fifita soyayya akan komai cikin rayuwar aure._
_Duk da tabbas itace ginshiki amma kuma hak'uri da biyayya sune makaman yaki da kowacce irin fitina._
Ina son ki rike abubuwan nan da zan fada miki.
Ki rike tsafta da kamshi
Sai kuma ki zama mai ka mun kai da biyayya kada ki zama mai girman kai ga mijinki.
Hafsah ta koyi abubuwa cikin sati hud'un da tayi tun daga girke girke data k'ara gogewa dasu sai kuma dabarun zama da miji da zamantakewar rayuwa ita kanta. Adduoi kuwa kullum cikin yin su take babu dare babu rana.
Bata iya sanarwa da Ukhashatu cewa bata gida ba saboda nauyinshi da take ji sai dai idan ya nuna yana son ganinta ta bashi uzuri. Ya k'osa sosai har yake fad'a mata.
"Don Allah ayi hakuri amarya adaina jamin rai ina son ganinka Allah."
Babu abinda take mishi sai dariya wanda da ya gaji sai ya sami lokaci yaje gidan.
Mufida ce ta fada mishi tana Kabuga.
Ya dawo gida asanyaye.
Yana dawowar kuwa ya kirata.
Tana dagawa taji yanayin shi kamar ba shi ba.
"Kin kyauta nagode."
Take tasha jinin jikanta.
Cike da fargaba tace hubby me ya faru kuma."?
"Hmm baki sani ba."?
Um."
Tace dashi.
Okey ya wuce nagode kawai.!!
Tayi shuru tana tunani me tayi toh."?
Sai ta marairaice.
Please Dear meya faru ne."?
"Hmm nace miki babu komai fah."
Please ta sake cewa.
Wai da gaske kike baki ce san me kikayi ba."
Murya cike da rauni tace.
Allah bansani ba I'm sorry plz tell me."
Ya danja dogon numfashi sannan yace.
"Meyasa zaki je unguwa baki sanar min ba."?
Take annurin fuskar ta ya dawo tace cikin shagwaba.
"Dear mama ne fa ta aikani sati na daya ma tace sai biki saura sati biyu na dawo."?
"What.. ina kika je haka ya fada a tsorace."
Abin ya bata dariya har tayi ta afili sannan tace "ina Kabuga gidan Yayar Mum dinmu.
"Hmm baki fad'a mini ba koh."?
I'm sorryy luv."
Ban hak'ura ba.
Tace plzzz"!!
Ya d'anyi shuru kafin yace.
To fad'amin me kikaje yi haka da har zaki dade kuma baki fad'a min ba."?
Hafsah ta bude baki sannan ta rufe kafin ta lalubi abincewa don bata son tayi b'aran b'arama.
Dear sallama naje mata fa.
"Hmm kuma har 1month koh."?
"Oh my God!! ta fada a zuciyarta. Yau na gamu da dan Jarida.
Dearrrh!!
Ta ja sunan kamar ta k'osa.
Shima yace uhum."?
Na zauna gidan fa da so mum bazata bari na yi kwanaki kadan ba.
"Okeyy shima yace.
Yaushe zan ganki toh plzzz kada ki hanani ganinki nayi missing dinki so bad dear plzzz"
Tayi mishi yar dariya.
"Really fah kike min dariya dama ke baki damu ba koh."?
ta shagwabe tace "Noo Dear.!!
"Umm bawani nan..in zo gobe ba don hali na ba."?
Tomorrow!!?
Yess"
Yace.
"Ka bari sai day after goben."
"Ok" yace mata sannan yayi dif.
Tasan fushi yayi don haka ta mishi dariya itama.
"I'm joking Dear kaxo goben kaji nima inason ganinka.
Ukhashatu ya lumshe ido saboda jin dadi.
"Thank you WiFi.
"U wlcm Data.!!
Tace mishi.
Suka sheke da dariya "Hmm ke koh..??
"Me kike so in taho miki dashi.
Ta girgiza kai kamar yana ganinta. "Nothing Dear.
"Ban yarda ba."
Tayi murmushi "Okey You You and You.!!
Yayi murmurshin jin dad'i "Amarya me wayo.!!
"Come with you alone." Ta sake fad'a.
Ya kara darawa "Nak'i din."
"Idan kukazo ba yanda nace ba zaku koma.!! tace.
Lokacin kuma tajiyo mama na kiranta sai lokacin ta tuna girki take duk da dama su aiki amma Mama sata take don ta saba sosai.
"Mum na kirana byee.
"Ok dear kije ki gaida mum."
__________________________
Biki saura sati biyu Basheer ya dira. Duk wasu shirye shirye sun tsara shi babu tsawwalawa saboda amaryar da angon basu san bid'a. Duk wani wanda ya dace yasan da bikin zuwa lokacin ya sani. Hafsah ta tura katinan gayyata ga contact d'inta.
Kowa na mata fatan alkhairi. Musamman Aysha Daheer dake da 'yaya biyu a lokacin. Su Nasreen sune organisers na komai.
Za'ayi kamu ne had'i da kauye Day sai Dinner sai kuma mother's eve. Ranar asabar k/ amarya.
Banda murnar Abbah data fi ta mama fitowa fili ita saboda kunya. Babu wanda za'ace yafi kowa farinciki da bikin kamar Basheer.
Har siyayya yayo wa Yayarshi da kudin shi shima a tashi bidi'ar ya kirkiro da wani event Arabian night."
Dole aka saka shi a manhaja.