← Book details Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 88

Sashe 7

Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da SIM card akan wayar sai dai babu chaji kara d'aya ne kawai.
Ta saka wayar a vibrations sannan ta d'auki chajar wayar ta jona ta achaji ta koma ta kwanta tana jiran taji ankira wayar..amma shiru har lokacin sallar magariba.Ta mik'e ta nufi toilet don yin alwala...
Bayan isha'i ne mama tazo ta kirata. Allah yaso lek'owa tayi bata shigo ba.
"Ki zo ki raka abbanku shopping keda bashir."
Ta saki k'ofar data rike ta juya.
Ajiyar xuciya Hafsah tayi sannan ta mik'e ta d'ora after dress akan kayan jikinta tayi rolling da mayafi sannan ta d'auki wayar ta maidata kwalinta sannan ta mayar inda ta bo'ye ta da farko.
Jin muryar mama tayi a bayanta tana "kiyi sauri fa"
Ta tsorata sosai.Mama ma taga hakan sai dai bata ce komai ba.
Al,adar abbannasu ce zuwa dasu shopping musammaman ita da bashir idan k'annensu suna buk'atar wani abin suna fad'a musu idan xa,a shopping a tawo musu dashi.
Yana jan hafsah ajiki sosai duk da ita ba namiji bace..amma yana hira da ita ya bata labarin Yarintar shi da yadda sukai karatu a boarding school (makarantar kwana) yana nuna mata al,amran rayuwa sosai, niyyar shi shine ta sami kyakykyawan tarbiyya da kwaxo ta zamewa k'annenta kamar uwa.
Abba nason Hafsah sosai ya kan fad'a mata ma wani lokacin "Hafsah ina son ki" (idan tayi wani abu ya burgeshi) yana nuna mata ita wata ce kuma tana da girma Shiyasa yakan kirata da "Yaya." (wasu lokutan idan zai kira ta) yakan ce mata idan k'annenta sun mata laifi ko bashir ya kawo mata raini wani lokacin "Haba yaya aikece babba kiyi hak'uri mana, duk abinshi kin dai girmeshi. Kokuma "Ke fa babba ce, kiyi ha'kuri dole babba sai yayi ha'kuri kinga kece zaki zame musu abin koyi, ki kula da rayuwarki Hafsah kada ki dinga shashanci da shirme"..
Wannan ne irin kalaman abba yawanci a gareta, wanda suna tasiri matuk'a azuciyarta har suka sa mata nutsuwa da girma fiye da shekarunta, don baka tab'a ganin ta tana abu na shashashanci ko rawar kai irin na 'yan matan yanxu, musamman wad'anda iyayensu ke da sukuni irinta..
Komai takeyi cikin nutsuwa take yinsa, bata gaggawa, shi yasa ake ganin kamar tana da 'yanga'.
Ki dinga nutsuwa Hafsah mace da nutsuwa aka santa ki daina gaggawa a al,amra domin gaggawa aikin shed'ance"..
Wannan ne kalaman abbanta ko da Yaushe.
Tsaye ta tarar da abban a falo yai murmushi "To mu tafi koh"?
Sunzo fita daga layinsu kenan taga motarshi zata shigo. gabanta ya fad'i, ta dafe k'irji
"ya salam"
To sunje sunyi siyayya sosai, mama kuma ta bata sautu don tace yau basai taje ba.
Sai wajen 9:00pm suka dawo.
Yaran sai murna suke dama abban baizo da tsaraba ba.
Dariya kawai take so take ita dai ta wuce d'aki ta duba wayarta.
Abba ya kalleta.
"Ko kin gaji ne yaya?
Ta kad'a kai
To maza je ki kwanta ta mik'e ta nufi bedroom d'inta.
Sai da ta d'an watsa ruwa sannan tasa kayan bacci. Ta dakko wayar ta kashe fitila ta kwanta.
5 missed calls ta gani akan wayar.
Sannan da text akan wayar tana cikin dubawa, sai ga wani kiran..
Ta d'aga ta kara a kunne "Hello."
Muryarshi mai sanyi da dad'i ta daki kunnenta. Ta d'an muskuta, kafin tayi magana yace cikin shagwabar nan tashi.
"Haba baby nayi miki laifi ko na kiraki kink'i picking then nazo kuma kika cemin bakya nan, pls mena miki ne..??
Ta bude baki xatayi magana kenan, taga haske ya baibaye d'akin tayi saurin juyowa mama ta gani idonta akan wayar hannunta.. 😳
Shigowa tayi ta tambayeta waye yazo nemanta d'azu? sai ta fara kunna fitila so take suyi magana kan kada ta soma kula wani tunda tasan abbanta baiso..
To kuma tana kunna fitila taga abinda da bata tab'a zato ba... Hafsah da waya to waye ya bata?? dawa ma take wayar??
Ku biyo ni..😇

*Hajeeyarku ce*👌🏼
*Pls idan kunga typing error ko kuskure kuyi hak'uri ni sabuwa a harkar. Wanna ne first novel di'na..👏🏼*
*Ina Godiya fans ☺*
*Pls I need your comments to encourage me!*👏🏼
[1/11, 1:33 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔

Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Karemerh)*
*Dedicated to:*
*Unique in your love heart group members.*

📄 *11*

*Tsawa* Maman ta daka mata tare da kai mata duka, wanda yaja tsoro yasa wayar fad`uwa a kan gadon.
Caraf mama tasa hannu ta d`auka abin yana bata mad`aukakin mamaki bata tab`a zata ba.

Uban wa ya baki wayar nan."?

Iya rudewa Hafsah tayi ta har ta kasa bada amsa.
"Tashi zaune."
Ta qara daka mata wata tsawar.

Ta miqe cike da fargaba yayin da maman ta zauna gefe gadon.

Ta kafe ta da ido sannan tace, "Ki fad`a mini wanda ya baki wayar nan tun muna mu biyu, idane ba haka ba zan hadaki da abban ku. "
Zufa ta ketowa Hafsah, ya zata yi idan wannan zancen yaje wajen Abba, ai ta ka d'e

Gwara ta fad`i gaskiya tun suna su biyu da maman tunda an kama ta dumu-dumu ai bata da wata mafita.

Cikin Hawaye ta labartawa maman yadda wayar tazo hannunta, Sannan ta qare mata ta kalaman kare kai.

"Wallahi Mama ajye min yayi ya tafi shiyasa na karb`a, kuma Allah ranar na fara ganinshi."

Tana gama zancen, taji mama ta kama kunnenta kamar zata tsinka.
"Ki kiyaye ni Hafsah, wallahi duk ranar da na kuma ganin makamancin haka sai ranki yayi mummunan b'aci, shashasha, kuma yanzu ma zan iya fadawa abbanki matuqar na qara ganin abin me kama da wannan. Kuma wayar na kwace bazaki qara ganinta ba. Kuma duk ranar da kika sake naji labarin kin k'ara kula yaron nan to ki tabbatar kamar abbanku ya sani ne."

"Bazan qara ba mama kiyi hak'uri."
Binta mama tayi da kallo kawai, sannan ta fice cike da mamaki.

Ta boye wayar sannan ta saita nutsuwar ta kada Abban Hafsah ya gane, sam bata son tada mishi hankali da irin wannan zancen ba.

Da alhinin k'wace wayar Hafsah ta kwana har ta kasa yin isashshen bacci. Allah Allah take safiya tayi taje makaranta ta sanar da Basma.

"Na shiga uku Basma, mama ta kwace wayar nan fah."

"Basma ta d`aka mata duka ke garin yaya, banza."

Tsautsayi Basma, waya nake tazo ta tadda ni, Allah ya rufamin asiri ba Abba bane ya ganni da na shiga uku.!!"

"Hmm, gaskiya ke doluwa ce, idan nice wallah bazan bayar da wayar ba."

Hafsah ta zaro ido. Kaii Basma tafa riga ta gani.
"Hmm, kedai tunda kinyi sakaci ai shikenan.
Please Basma, help me Mama tace kada ta sake ganin yazo na fita, wallah ina sonshi Basma, ya zanyi in dinga ganinshi gashi babu waya."?
"Please help me.!!
Dariya Basma tayi me isarta sannan ta kamo Hafsah tayi mata rad'a a kunne.
_"Ke dallah can appointment zaki dinga hada muku."_
Hafsah ta zaro ido, kamar a ina kenan nifa bana fita kinsani.
"Nonsense ki zo gidanmu mana."
"Kaii Chab Mama bazata barni ba."
"Hmm, kina da abin haushi H Hamid."
"Ba kina zuwa islamiyya ba."?
Eh ina zuwa."
"Why not kuna had'uwa idan kin fita.
Hafsah tayi shuru tana tunani, can kuma ta tuna tabbas babu mafita idan ba hakan ba don haka ta rungume Basma tana godiya.

Sanin da Hafsah tayi basma na zuwa da waya yasa tace,
"Please ki bani wayarki, na tura test Allah yaso n riqe number d`in.

"Hmm, ungo badon halinki ba. Ta ciro wayar daga aljihun uniform ta ba ta.

"Dear it's Hafsah, Mama na ta kwacen waya, ina son mu hadu, yau a bayan layin mu by 2:00pm plz kada kazo Gidan mu.

Minti kad'an ya kira, ta d'aga.
Baby me kike fad`amin, mamanki ta kwace waya.
Eh okay, mun had`u na baki wani.
"Noo dear thank you."
Aa zan taho miki dashi..
Ta katse wayar saboda tsoron kada a kama su da waya.
murna take sosai babu sauran damuwa.

Hakan ne ya faru kuwa, bayan Hafsah ta koma gida tayi ta nuk'u nuk'u har qannenta suka gaji da jiranta, mama tace suyi tafiyar su.
Dama haka take so don haka Basma ta tsara mata.

katon hijab ne har qwauri sai doguwar riga, sune uniform d`in. Ta sab'a Jakarta ta cewa mama ta tafi.

Yana ta kai kawo a layin, tun qarfe 1:30pm yake wajen har ya fidda ran ganinta.

Ya saki ajiyar zuciya sanda ya hango ta, ya nufi motar shi da nufin ya kunna su shiga ciki amma ta mishi alamar daya bari.
Ta gabanshi tazo ta wuce, sannan ta mishi inkiya (signer) da ya biyo ta.
Ahankali suke tafiya, har zuwa _lokon su Jamila, dake lokon_ babu Mutane sosai, kuma dama suna bin hanya biyu ko su bi tanan ko subi titi street.

A Wani dakali suka yada zango.
Ya kura mata ido yana murmushi, ya mata kyau sosai, taji ta a wata sabuwar duniya, _Lallai babu abinda ya kai soyayya sanya nishad`i._
"Baby I miss you."
Ya fad'a a hankali.
murmushi tayi itama.
Really"?
Yes ya fad'a yana jinjina kai.
"Me too my dear.
Itama ta fad`a.
Ya sakar mata murmushin daya sa ta shagala da kallon shi.
Bata ankara ba taji ya kamo hannunta, dole ta farga, tana kokarin kwacewa ta tuno basma.
_"Saura kuma ki nuna mishi qauyanci!._
Bata fahimce ta ba a lokacin amma Idan hakane dole tayi kyauyanci kuwa, yaushe zata bari haka na faruwa.
Chapter 7 · 0% Book details