← Book details Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 88

Sashe 8

Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ta zame hannunta a Hankali ta sannan ta miqe tana rungume, hannu a qirji, amma kirjinta sai bugawa yake da sauri da sauri don tsoro.
"Dear lemme go kada nayi late."
Ya kura mata ido, baiyi magana ba dai.
Ya miqa mata qaramar wayar hannun shi.
Okay take this."
"Noo dear."
Please ki karba mana, da me zanna contacting dinki."
Mama zata bani wayata.
Ta fara tafiya don ta fara tsorata da makarar da tayi.
Ya bita suka jera.
"Plz mana baby."
"Am sorry dear, zan amso nawa nace maka."
Ya karanci tsoro a idonta don haka ya kyaleta.
"OK ki dinga kirani a wayan friend dinki.
"Okay."
Sai da ya kusa rakata makaranta sannan suka rabu, ya miqa mata wata Leda dake hannunshi.
Da zata k'i amsa, ya
had'e ranshi sosai.
Dole ta karb'a saboda bata son su tsaya ja'inja, taqara bata lokaci, sannan tana tsoro kada idon-sani ya ganta."
"Thank you dear."
"I love you." Yace mata.
"Me too dear."
"Bye see you later."
Ya fad'a yana kallo ta.
Suna ta waiwayen juna, cike da farin ciki Hafsah take, gaskiya ya had'u bata tab'a zaton samun saurayi kamar wannan ba.

Gefe guda, tana fargabar riqe hannunta da yayi, Allah yasa dai ba haka yake ba.
sai kuma fargabar makarar data tafka, don ma ansan bata makara...

.[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔

Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to:*
*Unique In Your Love Heart Members.*

📄 *12*

*Ko* da Hafsah taje islamiyya acan ta rabar da abinda yusuf ya kawo mata..
Ice cream ne sai tarkacen kayan ciye -ciye..
Bayan ta dawo gida ne tana d'akinta mama ta kira ta ta dawo falo.
Tun daga rannan mama bata barin ta ta keb'e ita d'aya a d'aki idan ba lokacin bacci ne yayi ba..
Da safe suna isa makaranta layinsu Basma ta nufa, sai dai cikin rashin sa,a ranar gaba d'aya Basman bata zo makaranta ba.
Haka hafsah tayi zaman makarantar babu wata walwala.
Fatima ce ke fad'amata "Hafsah wallahi kwana biyu kin chanja, ko son zaman cikin class bakya yi.."
"Hmm, ruk'ayya wani abu ne ke damuna wallahi..
"Kuma kike rasa dawa zakiyi shawara sai Basma Yunus koh?"
Hafsah ta d'an sha jinin jikinta sai kawai ta kawo mata wani zance.
"Fatima ba wani abu bane kinsan k'awata jamila da nake fad'a miki?
"Eh"
Nan hafsah ta shiga labarta mata abinda ya sami Jamilar..
"To yanzu neman yadda zaku nemota kuke ko me??"
Hafasah bata da amsar bata don haka tace bazaki gane ba Fatima"
"To Allah ya taimka"
"Amin" inji Hafsah.
A ganin Fatima Basma ba k'awar da za,a zauna shawara da ita bace.. Ina ma taga hankalin da zata hango abinda Hafsah bata gano ba,?.. Ita damuwarta ma wai me suke tattaunawa ne??
Don bata yarda da abinda Hafsan ta fad'a mata ba.
A saninta Basma ba wata k'awar hafsah bace, hasalima abokiyar takararta ce don idan hafsah tayi sakaci wani lokacin Basma ke k'wace mata 1st position d'inta.
Basma akwai shishshigi da bani na iya.. Tana son shiga al,amran da babu ruwanta..
Tatasone agaban mahaifiyarta don tun tana shekara 5 suka rabu da mahaifinta. Sanadin haka yasa yake sakarwa maman tata kud'i har 'albashi' yake biyanta wai ladan d'awainiyar da take da 'yarshi duk wata dubu d'ari..
Mahaifiyar Basma business takeyi, kuma tana yawan yin tafiye tafiye sai tayi fiye da sati bata gari ko kuma ma k'asar gaba d'aya.
Don haka koyaushe basma na gidan k'awayen mamanta (Can take kaita idan tayi tafiya).

Don bata da kowa a kano duk danginta na kaduna, amma tunda tayi aure take zaune a kano, ita kad'ai sai 'yan aiki sai abokan hul'arta mazaa da mata da kullum suke zarya a gidan..
Idon Basma a bud'e yake sosai, domin idan mama tayi tafiya, haka manya- manyan samari ('ya'yan k'awayen mama) suke d'aukarta zuwa yawo, sune club, sune park, sune party.
Duk da haka mamanta na sata tayi karatu dole. (kuma don ma tana da kwakwalwar karatun ne.)
"Kiyi karatu basma ki dogara da kanki, kinfi k'arfin raini..
"ki daina la,akari da babanki yana da kud'i.."
Ahakan kuma take hanata kula samari, amma duk da haka bata hanata zuwa wajen wani party ko wani taro idan ya kama...
To,Hafsah bata samu damar tattaunawa da basma ba sai washe gari lokacin, malaminsu na lissafi zai shigo ajin suna hango shi suka fice, Basma na cewa "Mts yanzu zai damemu da wani revision."
SS 1a suka shige suka nemi guri suka zauna acan baya..
"ya kukayi H Hamid?
"Um,Basma yazo na fad'a mishi. Amma ba shine matsalar ba."
Ta fad'a cikin damuwa.
"To Mene matsalar?
Tayi k'asa da murya sannan tace
" Yusuf yana son rayuwar turawa, yana k'aunar ya tab'ani.. Wai haka yace min na mishi kiss"😳
"Mtsss"
Basma ta ja wani dogon tsaki.
"To sai me? Ke da irin local soyyaya zaki nuna mishi, wallahi kin bada ni"
Ni duk kinsa ma raina ya b'aci."
Hafsah dai tayi shiru ita yaushe zata fara wannan watsewar??
tab' Allah ya tsareta.
Amma dake kamar tana tsoron basma ne sai tace
"Basma yanzu an fasa kiran nashi kenan?
"Hmm ai kece, ta mik'a mata wayar tana cewa ungo saka number d'in..
(Al,adar Basma ce zuwa da waya makaranta.)
Ringing biyu aka d'aga.
"Hello" yace
Hafsah ta kalli Basma, bata san me zata ce ba.
Basma ta harareta.
Sai ta dawo kan doka da oda.
"Am, dear iam Hafsat"
"Oh my gosh!
Ya fad'a cikin wata k'ara my baby I miss u alot"
Ta daure tace "Me too"
"ya kake?
"Fine but thinking of you, wai when ur mama zata baki wayarki ne?
"Um very soon in sha Allah."
"Um um ni dai ban yarda ba kawai mu had'u anjima na baki wani"
"No, ka barshi yau zan karbi wayar"
"OK thank you my baby, yaushe ne zanzo my eyes want to see u kinji.?
Dam gabanta ya fad'i ashefa bata fad'a mishi an hanata kula shi ba..
"Um, am.. Ka bari mama ta bani wayar,
"Nooo ni dai I can't wait, pls baby nah"!
OK ina school kaga yanzu ka bari zamuyi waya, but pls kada kazo sai mun kuma yin waya."
"OK, bye bye i love u" 😍
"Thank you"
Gama wayarsu kenan, Geography teacher ya danno ajin, kuma shine form master d'in su Hafsah (shine ma ya gansu ran nan)
Suna ganinshi suka mik'e ya kallesu kawai..
"Again?
Ya fad'a yana rik'e haba..
"Yunus and Hamid What are you doing here??
"Am.. im Nothing sir"
"Ok, very good".
Ya fad'a yana kad'a kai.
Suna fita Basma ta Shek'e da wata shashashar dariya..
Tana wani abu da fuskarta kamar ta ga wani abin tsoro, look at your reaction H. Hamid, when Teacher catched us,...😱😨🤥 uhum kamar kinga zaki" hahh 😂😂
A gida kuma mama tunani takeyi akan, Kodai ta bawa Hafsah wayarta ne, a tunaninta, hafsah 'ya macece wacce Yanzu shekarunta sun kai 17, bai dace a matsa mata ba, don takai munzalin tsayawa da saurayi. Don ma abin ya zo da zamani da dane ai da tuni tana d'akin mijinta..
"Ai kuma ya dace ki nuna mata kuskurenta"
Wata zuciyar ta fad'a mata...
'Zan bari zuwa suyi hutu'
Haka mama ta kudurce a ranta..
To kusan kullum a makaranta sai Hafsah sunyi waya da Yusuf, kuma kullum zancen shi d'aya yaushe zai zo?
"Ka bari dear, ka bani two weeks"
Haka ta fad'a mishi wata rana, lokacin sun fara jarabawa.
"What? Mene kina cewa??
"Ok bakya sona ne I realized, ok I will leave you kawai"
Ya fad'a, kawai ya kashe wayar.
"Na shiga uku Basma kinji wani abu kuma"??
"To ya zan miki an baki shawara kink'i karb'a, ba saiki bari ya kub'ce miki ba."
Ta fad'a cikin rashin nuna damuwa da zancen.
"To aini basma tsoro nakeji..
"To ai shikenan"
Ta kuma kiran number ba,a d'aga ba.
"Oh my God! dama haka yake da fushi?.
So bata kuma samu sunyi waya ba sai ana gobe hutu (Bayan malaminsu ya kirata ya mata fad'a akan karatu )
Da k'yer ta samu ya hak'ura, amma yace mata dole ne su had'u cikin wani satin.
Aranar da aka musu hutu, ranar ne kuma bayan ta dawo, mama ta kira ta suka zauna a falon maman..
"Hafsah kinga kin girma, ki nutsu kisan abinda kike yi, zan baki wayarki..
Ta d'ago cike da murmushi,
"Nagode, Mama.
Ba wannan ba, kada ki bari abbanku ya ga wayar nan, sannan kiyi taka tsan -tsan da samari, bance ki kula kowa ba, tunda abbanki baya so,.. Kuma kada ki k'ara karb'ar abu makamancin wannan a hannun wani."
"Nagode Mama, in sha Allah zan kiyaye."
Ta mik'a mata wayar,
"ungo ki b'oye, k'awayenki kawai na yarda ki kira"
Cikin zumud'i ta karb'a..
Baki 'nunamin result d'in naki ba."
Tsoro ya cikata, babu yadda zatayi haka ta dakko ta bata.
"Kaii, ya akayi haka Hafsah??
Bari abbannaki ya dawo, wato don an hanaki kula samari shine zaki k'i maida hankali kan karatunki koh?
(A tunanin Mama kenan)
"Kiyi ha'kuri Mama wallahi ba haka bane."
"Yayi kyau"
Tashi kije kya had'u dashi ai"
Tana zuwa daki'n ta tura mishi text zuciyarta cike da farin ciki.
"My phone is with me.. But don't call me now, let's have phone by night..
I love you!!
*To shine fa wayar da tayi yau, bayan ta dawo daga wajen abban ya mata fad'an karatu, shine kuma wayar da mama ta kamata tanayi a darenna..(Page 1 to 3 )*👏🏼👏🏼

*Muje zuwa muji wannan soyyaya ya zata kaya..*😇

*Hajeeyah Kareemerh ce dai*👌🏼
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔

Story and writing by:

*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*

*Dedicated to:*
*Unique In Your Love Heart Members.*
😘😘😘👍🏻👍🏻👍🏻
*Jinjina gareku ZAZZAFAN SO NOVEL GROUP*
🍒 *Farida (Farisam*)
🍒 *Gimbiya Bilkisu*
🍒 *Basma A adam*
*فا طم*
🍒 *Ummi M shehu*
🍒 *Amina Yusha,u*
🍒 *Umman Aryan*
🍒 *Maman husna*
🍒 *Mufy expensive*
🍒 *Mummy khali*
👏🏼 *Ina yinku 💯 kamar yadda kuke yin novel d'ina*😘

📄 *13*
Chapter 8 · 0% Book details