Sashe 59
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Cikin k'asa da murya kuma a nutse yace, "kina burgeni Hafsah.
Muryar da kiran sunanta da yayi sukayi tasiri a zuciyarta..
Ina son sunanki, sunan mamana ne dake, fah.
"Allah sarki. "Haka tace kawai.
"Bari na barki kiyi bacci kada na hanaki bacci, Allah ya bamu alkhairi."
Ya kashe ba tare daya jira tace wani abu ba.
Ta zubawa numbobin shi ido, wane ne shi.. wanne irin mutum ne Allah ya hadata dashi, ya sanyata dariya lokaci d'aya ya barta kuma."?
A take, taji ya shiga ranta, duk da wani bangaren na zuciyarta na kwab'arta akan _kada ta zak'e, daga had'uwa baki sanshi ba.!!
_Funny ukhasha._
Haka taga hannunta ya rubuta wajen saving d`in number shi.
Allah ne ya kawo mata shi, lokacin da tunanin Jamila yayi mata yawa, saboda damuwar tana kiran number bata shiga, gashi 'yar wayar da sukayi har yasa ta manta...
Ta runtse idonta, sai taji tana son ta tuno kamannin shi, Ahankali take imagine ( _ayyana shi_) d`inshi, da wani ustazun mutum, mai cikar kamala...
Kwanaki sun fara tafiya, har ta saba da kiranta da yake, su gaisa, amma yawanshi a tak'aice, sai dai ba sa waya su gama bai sata dariya ba. Sai dai wani lokacin idan ya kirata takan share, idan kuwa ta d'aga kiranshi na gaba sai ya nemi afuwar ta, "Ayi hak'uri a taimaka kada a gaji dani d'indai, in sha Allah kin kusa gane wanene ni, don nasan hakane yakesa kike doubting akaina.!!
Wannan wanene haka, ya kware wajen _reading mind d'inta._ Hakika ta matsu ta ganshi, Gashi kullum sai dai yace, mata ta kusa sanin _wane shi,_ amma har yau bai tab'a neman alfarmar zai ganta ba shi, sai ta fara zargin abubuwa da dama..
Abinda bata sani ba shine, ya matsu sosai ya ganta, amma yana shakkar tambayar ta ne kada taga zak'ewar shi..
Yau ta kuduri niyyar kiran jamila a waya, suyi magana ko na mintuna ne ta haka zata gane idan har zata ci nasara akan jamilar.
Bayan missed calls in da tayi mata har wajen guda biyar, k'arshe dai jamilar ta biyo kiran.
'Sun gaisa sosai, sai kuma Hafsah taji kamar ran Jamila a b'ace yake, saboda yadda taji muryar ta.
Gashi kuma gefe guda ta rasa ta yadda zata cigaba da hirar tasu, domin bayan gaisuwar basu ce komai ba.
Jamila ce tace, "Hafsah H Hamid, kin gama school koh."?
"Eh Jamila mun gama Service ma."
Tayi murmushi, "Gud."!
"Kina aiki kenan."
Eh Inji Hafsah, a takaice ta bata amsa saboda tambayoyin yana tuna mata baya ne, kuma sai take ga kamar tono halin da jamilar ke ciki ne a yanzu.
Can ta jiyo Jamilar ta kuma cewa, tana wani murmushi..
"Hmm Hafsah kenan ai zan kawo miki ziyara, Idan na shigo unguwar namu."
Gaban Hafsah ya fad'i jin hakan, saboda batayi tunanin Jamila zatace zata zo gidan su ba.
Amma sai itama tayi murmushi kawai tace, "Okey thanks sai na ganki."
Okey Inji Jamila, sannan tace "Bye."
Ta kashe wayar.
Hafsah tayi ajiyar zuciya kawai, tayi shiru tana tunani, anya abinda take son yi kuwa zai yiwu..?
Ance,
_"Duk wanda yai nisa baya jin kira.!_
Sai taji tana k'ara godewa Allah bisa, yadda ita rayuwarta bata tab'arbare ba..
Tasani ba dabarar ta bace ko kuma dabarar iyayenta, kawai dai shiriyar Allah ce wacce yake shiryar da wanda yaso.'
"Alhamdulillah alaa kulli haal."!
Ta fad'a ahankali tare da yiwa kanta murmushi.
___________________
Yana kwance kan gadonshi, yana kallon sama, ya dafe kanshi da Hannaye biyu, wani irin Ciwon kai yake fama dashi tun tashinshi daga bacci, azuci yake karanto addu,a sannan ya shafe kan nashi.
Ya duba agogo, karfe shida na yamma magriba ta kusa.
Don haka ya mik'e zaune, saboda yamma ce lik'is.
Koda aka kira sallah ma bai fita ba, adakinshi yayi sallah har zuwa daf da isha'i sannan Fadwa tazo tana buga k'ofarshi.
Abude kofar take Don haka ta jiyo shi yana cewa, "Abude yake k'ofar ki shigo."
Duk da bai san wanene ba, yasan bazai wuce ita bace.
Ta shigo da sallama, ya amsa ahankali, yana kwance a dandaryar k'asa, akan dadduma inda yayi sallah.
Ta sami gefe ta dan zauna sannan ta fara mishi magana.
"Sannu Yaya."
Duk da bai fad'a mata ba tasan bashi da lafiya ne.
"Yawwa."
Yace mata.
"Me yake damunka, ya nuna mata kanshi."
"Oh sannu, Hajiya tace baka ci abinci ba, yanzu me za,a dafa maka."?
"Ki dafa min koma mene."
"A,a dai Yaya ka fad'i me zaka ci."
"To ki bari kawai"
Najwa tayi shiru, abin ya bata mamaki da takaici, amma data tuna halinshi sai kawai ta mike ta fita.
Ta fahimci baya son adameshi idan har yana wannan ciwon kan, amma ita ta tambayeshi ne saboda taji irin abinda yakeso, kada tayi mishi abinda baya so.
Har ta tafi sai kuma ta dawo adan tsorace tace, "Um wai kasha magani."?
Yasan babu wanda ya sata ta tambayeshi tunda babu wanda yasan bashi da lafiyar idan ba yanzu da aka ga bai fito ba tun yamma.
"Zansha."
Yace mata kawai.
Ta juya ta fita..
Fadwa rasa abinda zata kawo mishi tayi, sai kawai ta hada mishi kayan tea, ta dafa mishi Indomie, ta kawo mishi.
Ya mike yana kallon abincin, ko nazarin me yake oho, ita ko tana gefe ta zauna.
Har kusan minti 3, sannan taga dacewar ta ta had'a mishi, nan ta hada mishi komai, sannan ta mik'e zata fita.
"Thank you."
Yace mata ahankali.
Bata juyo ba kuma bata, ce mishi komai ba ta fice, tana murmushi.
_Wato zaman da yayi jira yake tayi serving d'inshi ne, amma kuma yaki mata magana._
Muryar da kiran sunanta da yayi sukayi tasiri a zuciyarta..
Ina son sunanki, sunan mamana ne dake, fah.
"Allah sarki. "Haka tace kawai.
"Bari na barki kiyi bacci kada na hanaki bacci, Allah ya bamu alkhairi."
Ya kashe ba tare daya jira tace wani abu ba.
Ta zubawa numbobin shi ido, wane ne shi.. wanne irin mutum ne Allah ya hadata dashi, ya sanyata dariya lokaci d'aya ya barta kuma."?
A take, taji ya shiga ranta, duk da wani bangaren na zuciyarta na kwab'arta akan _kada ta zak'e, daga had'uwa baki sanshi ba.!!
_Funny ukhasha._
Haka taga hannunta ya rubuta wajen saving d`in number shi.
Allah ne ya kawo mata shi, lokacin da tunanin Jamila yayi mata yawa, saboda damuwar tana kiran number bata shiga, gashi 'yar wayar da sukayi har yasa ta manta...
Ta runtse idonta, sai taji tana son ta tuno kamannin shi, Ahankali take imagine ( _ayyana shi_) d`inshi, da wani ustazun mutum, mai cikar kamala...
Kwanaki sun fara tafiya, har ta saba da kiranta da yake, su gaisa, amma yawanshi a tak'aice, sai dai ba sa waya su gama bai sata dariya ba. Sai dai wani lokacin idan ya kirata takan share, idan kuwa ta d'aga kiranshi na gaba sai ya nemi afuwar ta, "Ayi hak'uri a taimaka kada a gaji dani d'indai, in sha Allah kin kusa gane wanene ni, don nasan hakane yakesa kike doubting akaina.!!
Wannan wanene haka, ya kware wajen _reading mind d'inta._ Hakika ta matsu ta ganshi, Gashi kullum sai dai yace, mata ta kusa sanin _wane shi,_ amma har yau bai tab'a neman alfarmar zai ganta ba shi, sai ta fara zargin abubuwa da dama..
Abinda bata sani ba shine, ya matsu sosai ya ganta, amma yana shakkar tambayar ta ne kada taga zak'ewar shi..
Yau ta kuduri niyyar kiran jamila a waya, suyi magana ko na mintuna ne ta haka zata gane idan har zata ci nasara akan jamilar.
Bayan missed calls in da tayi mata har wajen guda biyar, k'arshe dai jamilar ta biyo kiran.
'Sun gaisa sosai, sai kuma Hafsah taji kamar ran Jamila a b'ace yake, saboda yadda taji muryar ta.
Gashi kuma gefe guda ta rasa ta yadda zata cigaba da hirar tasu, domin bayan gaisuwar basu ce komai ba.
Jamila ce tace, "Hafsah H Hamid, kin gama school koh."?
"Eh Jamila mun gama Service ma."
Tayi murmushi, "Gud."!
"Kina aiki kenan."
Eh Inji Hafsah, a takaice ta bata amsa saboda tambayoyin yana tuna mata baya ne, kuma sai take ga kamar tono halin da jamilar ke ciki ne a yanzu.
Can ta jiyo Jamilar ta kuma cewa, tana wani murmushi..
"Hmm Hafsah kenan ai zan kawo miki ziyara, Idan na shigo unguwar namu."
Gaban Hafsah ya fad'i jin hakan, saboda batayi tunanin Jamila zatace zata zo gidan su ba.
Amma sai itama tayi murmushi kawai tace, "Okey thanks sai na ganki."
Okey Inji Jamila, sannan tace "Bye."
Ta kashe wayar.
Hafsah tayi ajiyar zuciya kawai, tayi shiru tana tunani, anya abinda take son yi kuwa zai yiwu..?
Ance,
_"Duk wanda yai nisa baya jin kira.!_
Sai taji tana k'ara godewa Allah bisa, yadda ita rayuwarta bata tab'arbare ba..
Tasani ba dabarar ta bace ko kuma dabarar iyayenta, kawai dai shiriyar Allah ce wacce yake shiryar da wanda yaso.'
"Alhamdulillah alaa kulli haal."!
Ta fad'a ahankali tare da yiwa kanta murmushi.
___________________
Yana kwance kan gadonshi, yana kallon sama, ya dafe kanshi da Hannaye biyu, wani irin Ciwon kai yake fama dashi tun tashinshi daga bacci, azuci yake karanto addu,a sannan ya shafe kan nashi.
Ya duba agogo, karfe shida na yamma magriba ta kusa.
Don haka ya mik'e zaune, saboda yamma ce lik'is.
Koda aka kira sallah ma bai fita ba, adakinshi yayi sallah har zuwa daf da isha'i sannan Fadwa tazo tana buga k'ofarshi.
Abude kofar take Don haka ta jiyo shi yana cewa, "Abude yake k'ofar ki shigo."
Duk da bai san wanene ba, yasan bazai wuce ita bace.
Ta shigo da sallama, ya amsa ahankali, yana kwance a dandaryar k'asa, akan dadduma inda yayi sallah.
Ta sami gefe ta dan zauna sannan ta fara mishi magana.
"Sannu Yaya."
Duk da bai fad'a mata ba tasan bashi da lafiya ne.
"Yawwa."
Yace mata.
"Me yake damunka, ya nuna mata kanshi."
"Oh sannu, Hajiya tace baka ci abinci ba, yanzu me za,a dafa maka."?
"Ki dafa min koma mene."
"A,a dai Yaya ka fad'i me zaka ci."
"To ki bari kawai"
Najwa tayi shiru, abin ya bata mamaki da takaici, amma data tuna halinshi sai kawai ta mike ta fita.
Ta fahimci baya son adameshi idan har yana wannan ciwon kan, amma ita ta tambayeshi ne saboda taji irin abinda yakeso, kada tayi mishi abinda baya so.
Har ta tafi sai kuma ta dawo adan tsorace tace, "Um wai kasha magani."?
Yasan babu wanda ya sata ta tambayeshi tunda babu wanda yasan bashi da lafiyar idan ba yanzu da aka ga bai fito ba tun yamma.
"Zansha."
Yace mata kawai.
Ta juya ta fita..
Fadwa rasa abinda zata kawo mishi tayi, sai kawai ta hada mishi kayan tea, ta dafa mishi Indomie, ta kawo mishi.
Ya mike yana kallon abincin, ko nazarin me yake oho, ita ko tana gefe ta zauna.
Har kusan minti 3, sannan taga dacewar ta ta had'a mishi, nan ta hada mishi komai, sannan ta mik'e zata fita.
"Thank you."
Yace mata ahankali.
Bata juyo ba kuma bata, ce mishi komai ba ta fice, tana murmushi.
_Wato zaman da yayi jira yake tayi serving d'inshi ne, amma kuma yaki mata magana._