Sashe 11
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Basma ta d'auki wani salo na yawan zuwa gidan su Hafsa, suyi ta hirar su. Dama ita ba wasu k'awayene da ita ba, Jamila ce kawai..
Kwanaki sun shud'e, har su Hafsah sun koma makaranta, Yanzu tana Aji na k'arshe a secondary wato SS 3.
Wanda tun ranar da suka had'u da Yusuf, agidan su Basma basu k'ara had'uwa ba. Sai dai waya ce koyaushe suna yinta duk dare da kuma sanyin safiya..
Hafsah sosai takan tsaya tayi tunani akan soyayyarsu da Yusuf..
Dole ne ta kirashi da 'First Love' d'inta (Saurayinta na farko) ita dai tasan ko ada bata da saurayi, irin soyyayyar nan ta makaranta da akeyi da class mate duk batayi kwata-kwata.
Shiyasa take jin wani abu na musammaman game da Yusuf.
Misali aduk randa bai kirata ba sai ta tsinci kanta cikin kewa da damuwa, sai taji kamar ma bata da lafiya.
Ko tunashi tayi sai
taji wani nishadi a tattare da ita.. Sau da dama Mama tasha kamata tana murmushi ita kad'ai, idan ta tambayeta "Ke lafiyarki?
Sai ta ce mata "Hmm Mama babu komai."
Mama ta kance "Allah ya shirya"
Hafsah na ayyanawa ('imagine') kanta irin rayuwar da zasuyi da Yusuf idan sunyi aure..
Ko da a makarantar boko idan ana hira, irin ta aure kamar yadda 'yan matan yanzu kanyi, (musamman yara 'yan secondary)
Takan nuna ra,ayinta akan Miji mai kula da matarshi ('Caring husband') a ra,ayinta bata son Namiji mai nuna halin 'ko-'in-kula' (I don't care attitude).
Lokacin suna tare da Jamila.
Wata rana Jamilar ta tab'a d'aukar Diary (Na Hafsah). Da yake Jamila akwaita da son bincike da kuma neman sanin duk abinda bata sani ba musammaman akan harkar 'Gayu'.
Hafsah wai me kike rubutawa anan ne??
(dake lokacin a yarinta ne) kuma ba wani abu ne cikin Diary d'inba banda shirme irin na yarinta. Hafsah ce mata tayi
"Ki bud'e ki karanta mana"
Jamila ta hau bud'e Diary d'in page by page.. Abubuwa take gani kala-kala aciki kamar:
*"My first-day at school*
To day is the first day of my secondary school..
Wani shafi (page) daya burge jamila shine Wanda taga an rubuta..
*I WANT MY FEATURE HUSBAND TO BE...*
Beautiful, Tall, and Mid obese.
'Colour of dressing: English wears..'
Behavior: I want him to be: Humble, caring, sociable, Cool-temfered and Good- hearted,
That would scriface everything to me!
*And then "Wanda baxai zai min kishiya ba!*😅
And I want to him to always say 'I love you'!
Jamila tayi dariya
Hahh Hafsah kenan Allah ya baki"
"Amin Jamila.
"Ni fa kafin ma in aure ka sai na tantanceka"
Jamila ta kalleta "Koh?
Na tsani 'Mugun Miji'
Wallahi biki ga aunty na yadda mijinta ke mata wulak'anci ba!
"Allah ya bamu nagari" inji Jamila.
"Amiin. Aini kullum nayi sallah sai na rok'i Allah ya bani Miji na gari." inji Hafsah.
(Yana da kyau ga kowacce budurwa ma rok'i Miji na gari wajen Allah SWT) # khareemerh.
Hmm Hafsah ki bani wannan littafin mana. Tana nufin Diary d'ina.
Kai Jamila ai nawane sai dai in munje store da abbanmu zan d'akko miki in sha Allah..
"Au d'akko wa ake"?
"Kiji ki, I mean I will bought it for you"
"Au nagode sosai Hafsah.
Aminci sosai Basma da Hafsah sukeyi yanzu, wanda kowa acikin ajin yake mamakinsu.
Wata ranar Asabar Mama tasa Hafsah ta shirya taje gidan 'Hajiyah' wato kakarsu ta wajen uba. Ta dad'e bata je gidan ba.
Kwana d'aya zatayi ta dawo.
A unguwar ja,en gidan yake ta shirya tun wajen 11:00am.
Hajeeyah Amina dattijuwa ce 'yar kimanin shekara 70. Tana da halin dattako, Shiyasa da wuya ka ganta gidan d'anta (Abbansu Hafsa) tana da kawaici bata saka baki a cikin al,amransu. Sai dai hakan bai hana idan taga b'arna ta nuna musu hanyar gyara ba.
Fara ce ita, kyakyauwa da 'yar furfura akanta. Tana da tsafta, kuma ita kad'aice a gidan nata, sai wata yarinya me mata aiki sai kuma autanta dake shirin yin aure nan da wasu watanni wato k'anin abbansu Hafsah 'Auncle Abdallah'
Hafsah tayi sallama cikin falon da Hajiya ke zaune.
'Wa alaikumussalam da Hafsah na"
Hafsah ta shiga cikin falon ta ajye Jakarta a gefe.
Ta zauna a k'asa Hajiya na kan kujera.
"Hajiya ina kwana"
Lpia lau Hafsat.
"Kece yau a gidan kenan?
"Gaskiya kin rabu da zuwa kwana biyu"
"Saboda school shi yasa"
"Eh hakane kuma"
"Ya Mamantaku da sauran k'annen naki?
"Suna nan lpia lau suna gaisheki."
"To madallah"
"Ki shiga ciki ki ajye jakar taki mana"inji Hajiyah.
Hafsah ta mik'e ta d'auki jakarta ta shiga wani d'aki dake falon.
Katiface shinfid'e a daki'n kawai.
Ta ajye sanna ta cire mayafinta ta fito.
Hira suka d'an farayi da Hajiyar.
"Nace ko kuna dai yin k'okari a makaranta Koh?
Hafsah ta d'anyi dariya
"Sosai ma Hajiya"
"To Allah ya taimaka"
"Ni nafi son ma kiyi karatun likita."
"Hah ai Hajiya ni ba a science class nake ba, sai dai bashir, shine ma yake son ya zama Doctor"
"Hajiya ta kalleta to ke me zakiyi?
"Law zan karanta"
Menene kuma haka?
"To lawyer zan zama!
Hajiya ta harareta "Ke dahalla bana son shirmen banza mak'aryaci ya kike so ki zama ?
Hafsah ta Shek'e da dariya.
Hajiya lawyer fa ba mak'aryaci bane"
"Ke rufe min baki."
Shi Habibun (Tana nufin Abba) ne yake so ki karanta wannan karatun k'aryar ko me?
"A,a ni nakeso dai Hajiya..
"To kwa idan na isa bazakiyi ba.."
Hafsah ta k'unshe dariyar ta. (Wannan rigima ta Granny ta fad'a a zuciyarta)
Ni ko sanda Hamidu (kakan su Hafsah) ya fito zai aure ni, dama ya gama sakandara (Secondary), da yace min karatun 'Loya' (Lawyer) zai cewa nayi indai yayi na fasa aurenshi.. Shine fa ya fasa ya koma Malamin makaranta..
"Hahh,Gaskiya Hajiya kice kin ja mishi class"😅
"Ke ja,ira fad'i da Hausa muji"
Cewa nayi
"Ashe tun da ma 'yan mata suna juya saurayi?
Gidanku kin d'auka muma Irinku ne.. Saiki ga yarinya ta na bin saurayi unguwa don rashin kamun kai.. Mu ada ba sai yazo nak'i fitowa ba ma, kuma dole ya aikomin da kud'in zance!!.. Ku ko yanzu da ko kwandala basa baku??😒
Hafsah tayi dariya
Hajiya ai yanzu ba da bane..
"Kyaji da shi dai ni dai ki kawon shi murmushi gaisa.."
Hafsah an tab'o mata inda ke mata k'aik'ayi '.
Ai Hajiya yau ma zai zo gidannan.
"Au haba"?
"Yayi kyau ai"
Tashi kije kitchen akwai farfesu ki d'akko ki ci.
"To Hajiya."
Da daddare Hafsah tayi kwalliya sosai saboda zuwa da yusuf zai yi..
Hajiya ce harda bata turare ta fesa..
"Ku dinga sa turare sosai, saboda maza nason k'amshi."
"Kin ganki yanzu kin yi kyau sosai, shiyasa kike burgeni bakya yin kwalliyar nan ta aljanu da kuke"
Hafsah tayi dariya "Gayu ne fa hajiya"
"Ke ina wani gayu?
Ungo saka kwalli sai ku dinga barin ido fari fat"
Hafsah ta karb'a tasa.
Lokacin kuma wayarta tayi k'ara alamar Yusuf ya iso kenan..
INA FATAN KUNA JIN DAD'IN WANNAN LITTAFI *ZAZZAFAN SO*
DOMIN COMMENTS KO GYARA KO NEMAN K'ARIN BAYANI 09072802875
*HAJEEYAH KAREEMERH CE DAI*👌🏼
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to:*
*Unique In Your Love Heart Members.*
*MUCH OF LOVE TO YOU MY AUNTY Maryam Adam Gid'ad'o. (MAMAN ASLAM) ALLAH YA RAYA SWEETIE*👏🏼😘😘
📄 *15*
Kwanaki sun shud'e, har su Hafsah sun koma makaranta, Yanzu tana Aji na k'arshe a secondary wato SS 3.
Wanda tun ranar da suka had'u da Yusuf, agidan su Basma basu k'ara had'uwa ba. Sai dai waya ce koyaushe suna yinta duk dare da kuma sanyin safiya..
Hafsah sosai takan tsaya tayi tunani akan soyayyarsu da Yusuf..
Dole ne ta kirashi da 'First Love' d'inta (Saurayinta na farko) ita dai tasan ko ada bata da saurayi, irin soyyayyar nan ta makaranta da akeyi da class mate duk batayi kwata-kwata.
Shiyasa take jin wani abu na musammaman game da Yusuf.
Misali aduk randa bai kirata ba sai ta tsinci kanta cikin kewa da damuwa, sai taji kamar ma bata da lafiya.
Ko tunashi tayi sai
taji wani nishadi a tattare da ita.. Sau da dama Mama tasha kamata tana murmushi ita kad'ai, idan ta tambayeta "Ke lafiyarki?
Sai ta ce mata "Hmm Mama babu komai."
Mama ta kance "Allah ya shirya"
Hafsah na ayyanawa ('imagine') kanta irin rayuwar da zasuyi da Yusuf idan sunyi aure..
Ko da a makarantar boko idan ana hira, irin ta aure kamar yadda 'yan matan yanzu kanyi, (musamman yara 'yan secondary)
Takan nuna ra,ayinta akan Miji mai kula da matarshi ('Caring husband') a ra,ayinta bata son Namiji mai nuna halin 'ko-'in-kula' (I don't care attitude).
Lokacin suna tare da Jamila.
Wata rana Jamilar ta tab'a d'aukar Diary (Na Hafsah). Da yake Jamila akwaita da son bincike da kuma neman sanin duk abinda bata sani ba musammaman akan harkar 'Gayu'.
Hafsah wai me kike rubutawa anan ne??
(dake lokacin a yarinta ne) kuma ba wani abu ne cikin Diary d'inba banda shirme irin na yarinta. Hafsah ce mata tayi
"Ki bud'e ki karanta mana"
Jamila ta hau bud'e Diary d'in page by page.. Abubuwa take gani kala-kala aciki kamar:
*"My first-day at school*
To day is the first day of my secondary school..
Wani shafi (page) daya burge jamila shine Wanda taga an rubuta..
*I WANT MY FEATURE HUSBAND TO BE...*
Beautiful, Tall, and Mid obese.
'Colour of dressing: English wears..'
Behavior: I want him to be: Humble, caring, sociable, Cool-temfered and Good- hearted,
That would scriface everything to me!
*And then "Wanda baxai zai min kishiya ba!*😅
And I want to him to always say 'I love you'!
Jamila tayi dariya
Hahh Hafsah kenan Allah ya baki"
"Amin Jamila.
"Ni fa kafin ma in aure ka sai na tantanceka"
Jamila ta kalleta "Koh?
Na tsani 'Mugun Miji'
Wallahi biki ga aunty na yadda mijinta ke mata wulak'anci ba!
"Allah ya bamu nagari" inji Jamila.
"Amiin. Aini kullum nayi sallah sai na rok'i Allah ya bani Miji na gari." inji Hafsah.
(Yana da kyau ga kowacce budurwa ma rok'i Miji na gari wajen Allah SWT) # khareemerh.
Hmm Hafsah ki bani wannan littafin mana. Tana nufin Diary d'ina.
Kai Jamila ai nawane sai dai in munje store da abbanmu zan d'akko miki in sha Allah..
"Au d'akko wa ake"?
"Kiji ki, I mean I will bought it for you"
"Au nagode sosai Hafsah.
Aminci sosai Basma da Hafsah sukeyi yanzu, wanda kowa acikin ajin yake mamakinsu.
Wata ranar Asabar Mama tasa Hafsah ta shirya taje gidan 'Hajiyah' wato kakarsu ta wajen uba. Ta dad'e bata je gidan ba.
Kwana d'aya zatayi ta dawo.
A unguwar ja,en gidan yake ta shirya tun wajen 11:00am.
Hajeeyah Amina dattijuwa ce 'yar kimanin shekara 70. Tana da halin dattako, Shiyasa da wuya ka ganta gidan d'anta (Abbansu Hafsa) tana da kawaici bata saka baki a cikin al,amransu. Sai dai hakan bai hana idan taga b'arna ta nuna musu hanyar gyara ba.
Fara ce ita, kyakyauwa da 'yar furfura akanta. Tana da tsafta, kuma ita kad'aice a gidan nata, sai wata yarinya me mata aiki sai kuma autanta dake shirin yin aure nan da wasu watanni wato k'anin abbansu Hafsah 'Auncle Abdallah'
Hafsah tayi sallama cikin falon da Hajiya ke zaune.
'Wa alaikumussalam da Hafsah na"
Hafsah ta shiga cikin falon ta ajye Jakarta a gefe.
Ta zauna a k'asa Hajiya na kan kujera.
"Hajiya ina kwana"
Lpia lau Hafsat.
"Kece yau a gidan kenan?
"Gaskiya kin rabu da zuwa kwana biyu"
"Saboda school shi yasa"
"Eh hakane kuma"
"Ya Mamantaku da sauran k'annen naki?
"Suna nan lpia lau suna gaisheki."
"To madallah"
"Ki shiga ciki ki ajye jakar taki mana"inji Hajiyah.
Hafsah ta mik'e ta d'auki jakarta ta shiga wani d'aki dake falon.
Katiface shinfid'e a daki'n kawai.
Ta ajye sanna ta cire mayafinta ta fito.
Hira suka d'an farayi da Hajiyar.
"Nace ko kuna dai yin k'okari a makaranta Koh?
Hafsah ta d'anyi dariya
"Sosai ma Hajiya"
"To Allah ya taimaka"
"Ni nafi son ma kiyi karatun likita."
"Hah ai Hajiya ni ba a science class nake ba, sai dai bashir, shine ma yake son ya zama Doctor"
"Hajiya ta kalleta to ke me zakiyi?
"Law zan karanta"
Menene kuma haka?
"To lawyer zan zama!
Hajiya ta harareta "Ke dahalla bana son shirmen banza mak'aryaci ya kike so ki zama ?
Hafsah ta Shek'e da dariya.
Hajiya lawyer fa ba mak'aryaci bane"
"Ke rufe min baki."
Shi Habibun (Tana nufin Abba) ne yake so ki karanta wannan karatun k'aryar ko me?
"A,a ni nakeso dai Hajiya..
"To kwa idan na isa bazakiyi ba.."
Hafsah ta k'unshe dariyar ta. (Wannan rigima ta Granny ta fad'a a zuciyarta)
Ni ko sanda Hamidu (kakan su Hafsah) ya fito zai aure ni, dama ya gama sakandara (Secondary), da yace min karatun 'Loya' (Lawyer) zai cewa nayi indai yayi na fasa aurenshi.. Shine fa ya fasa ya koma Malamin makaranta..
"Hahh,Gaskiya Hajiya kice kin ja mishi class"😅
"Ke ja,ira fad'i da Hausa muji"
Cewa nayi
"Ashe tun da ma 'yan mata suna juya saurayi?
Gidanku kin d'auka muma Irinku ne.. Saiki ga yarinya ta na bin saurayi unguwa don rashin kamun kai.. Mu ada ba sai yazo nak'i fitowa ba ma, kuma dole ya aikomin da kud'in zance!!.. Ku ko yanzu da ko kwandala basa baku??😒
Hafsah tayi dariya
Hajiya ai yanzu ba da bane..
"Kyaji da shi dai ni dai ki kawon shi murmushi gaisa.."
Hafsah an tab'o mata inda ke mata k'aik'ayi '.
Ai Hajiya yau ma zai zo gidannan.
"Au haba"?
"Yayi kyau ai"
Tashi kije kitchen akwai farfesu ki d'akko ki ci.
"To Hajiya."
Da daddare Hafsah tayi kwalliya sosai saboda zuwa da yusuf zai yi..
Hajiya ce harda bata turare ta fesa..
"Ku dinga sa turare sosai, saboda maza nason k'amshi."
"Kin ganki yanzu kin yi kyau sosai, shiyasa kike burgeni bakya yin kwalliyar nan ta aljanu da kuke"
Hafsah tayi dariya "Gayu ne fa hajiya"
"Ke ina wani gayu?
Ungo saka kwalli sai ku dinga barin ido fari fat"
Hafsah ta karb'a tasa.
Lokacin kuma wayarta tayi k'ara alamar Yusuf ya iso kenan..
INA FATAN KUNA JIN DAD'IN WANNAN LITTAFI *ZAZZAFAN SO*
DOMIN COMMENTS KO GYARA KO NEMAN K'ARIN BAYANI 09072802875
*HAJEEYAH KAREEMERH CE DAI*👌🏼
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to:*
*Unique In Your Love Heart Members.*
*MUCH OF LOVE TO YOU MY AUNTY Maryam Adam Gid'ad'o. (MAMAN ASLAM) ALLAH YA RAYA SWEETIE*👏🏼😘😘
📄 *15*