Sashe 29
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
*A* k'ofar gidansu, aka ajye Basma, ta fito, ta tsaya gefen gidan, sannan ta d'akko wayarta, ta danna kiranshi, ringing d'aya ya d'auka. Yanzu, muryarshi ta fi d'azu yin sanyi.
"Hello,"
"Am gani a gate enku."
"Ok, ki shigo kinji"
'Ya kira mai gadi, a waya yace ya rakata har k'ofar sashinshi.'
Tana shigowa, mai gadin ya mik'e da saurinshi, "Barka da zuwa Hajiya"
'Ta kalleshi kawai.' Ya shige gaba, tana binshi a baya, yana mamakin wacce irin bak'uwa ce wannan..??
'Asanin shi dai Yusuf, yana yawon daren shi, amma bai tab'a ganin ya kawo wata, cikin gidan su ba.'
'Azuciyarshi yace 'Allah ya shirya'
Ba wai don yana zargin, Yusuf d'in da wani abu bane, amma, bai ga dalilin da idan zaku tattauna wani abu da mace ba, har sai ka kirata gida kun keb'e..
'Suna isa dai dai bakin k'ofar wajen nashi, yai mata nuni da k'ofar, "Hajiya nan ne shashin oga Yusuf, d'in."
Ta yatsina fuska, sannan ta ce "Ok."
'Ta murd'a k'ofar a hankali, ta sanya k'afarta cikin wani madaidaicin, falo.
'A kwance ta hango shi, kan kujera 'Three seater', daga shi sai singlet da gajeren wando, ta d'an so razana, amma sai ta dake.'
'Ta k'arasa cike da yanga, ta nemi kujera mai kallon tashi ta zauna.'
'Shi kuma tunda ta bud'e k'ofar ya k'ura mata ido, har ta zauna, sannan ya mik'e zaune ya fuskanto ta sosai, ita kuma ta wani lumshe ido ta bud'e.'
'Ya saki murmushin daya nuna mata yaji dad'in ganinta sosai, sannan ya bud'e baki ya fara magana cikin k'asa da murya.'
"You're welcome"!
Tayi murmushi mai sauti, "Hmm, thank you."
'Ya karkatar da kai, "Zaki, iya..
zuwa.. dama"?
Tayi fari da idonta, "Hmm why not"?.
"Yai murmushi thanks alot"
Ahankali ya mik'e ya ya isa fridge ya d'akko lemo da ruwa da d'an plate da cup, duk a ciki, sannan ya tako har kujerar da take zaune, ahankali ta dinga jin fad'uwar gaba, amma sai tayi k'arfin hali ta dake, a zuciyar ta tana kishin ka da yaga hakan ya rainata, sai ma ta dinga k'ak'alo murmushin kan leb'e tana yi.
🤔 _k'arfin hali_😅
'Bayan ya ajye su akan d'an wani table, sannan ya zauna a wajen da yaji ya mishi, wato daf da ita sosai, sannan yayi gyaran murya,
"Hmm Basma ma friends"
"Hmm, Yusuf, ya akayi ne"
'Cikin juyayyiyar hausarshi yace,
"Hmm mene ma ba,ayi bane, ke dai ki sha lemon nan kinji."
'Ya sunkuiya yana zuba mata a cup sannan ya mik'a mata, "Thank you."
'Tace dashi.'
Ta d'an sha yadda bazaice tayi k'auyancin kinsha ko kuma ta shanye ba."
'Ta dire kofin yayin da shi kuma ya ke kallonta cikin k'ura ido, tana k'ara k'awatuwa a idanunshi, wani b'angaren tana kore Hafsah, ta hanyar karanto mishi idan, itace bazata iya ba, saboda gidadancin ta, (ita Hafsan)
'Ita dai Basma jiran, cewar shi takeyi wato taji, ('Dalilin gayyato ta)
'Hum, yai wata gauruwar ajiyar zuciya sanan ya ce cikin muryar da take bayyana mata irin halin da ya ke ciki.'
"Am basma,.. Nasan kinyi mamakin inviting enki dana yi, koh,? '
'So kada ki damu, ni ina so ne mu k'ulla friendship ni da ke, yafi na da, and then ina so ki bani shawara da kuma k'arin bayani akan Hafsah."
'Ya k'arasa yana zuba mata idanunshi, ita kuma sai da ta d'anyi kokawa da tunaninta kafin ta k'arasa fahimtar inda dunkulellen zancen ya nufa.'
'Ta kuma jiyo muryarshi yana cewa, "kin dai son irin mu,amalan da Hafsah ke min, please kina ganin ya za,ayi na jure zama da ita haka,"
Basma tayi murmushi azuciyarta, amma sai ta gimtse da taji yace, "I don't mean zan rabu da ita ne, sai dai na fad'a mata zamanmu ba zai yiwu haka ba,.. saboda ita ne fa, for more than 1 year duba rabona da..".
'Sai ya katse zancen babu shiri, ita kuma ta hau ajiyar zuciya.'
"Dole ne kinga na samar wa kaina, solution koh"
'Ya fad'i hakan cikin k'aramin sauti.'..
'A gidan su Hafsa kuwa, tana kwance, a falo kan kujera, taji sallama, ta amsa tare da tashi zaune don tabbatar wa da wacce take tunani.'
"A Taheer!!
'Ta fad'a cikin k'araji suka rungume juna.
'Aisha dai ahankali take sakin murmushi kawai.'
'Hafsah ta shiga hidima da ita, ta kawo mata lemo, ruwa da snacks har abinci ma da yaji nama acikin shi.'
'Aisha ta shiga tab'awa tana jimanta yadda zata ruguzawa Hafsah d'an farin cikin da ta ganta ciki yanzu, amma sai ta sami k'warin guiwa da ta tuna babu ishashshen lokacin b'atawa.
'Tayi goron numfashi cikin rashin sanin ta ina zata fara.'
"Oh dama zaki zo gidanmu Aysha."
"Hahh gani kuwa"
Kinyi k'okarin ganewa."
"Hmm Koh."
"Sosai ma, don ma babu wuya gidan."
"Hakane kam."
"Ma manku bata nan ne"?
"Eh wllhi ba nisa tayi ba dai ta d'anje barka ne."
"Hmm, lallai kam shine ke kuma baki tafi islamiyya ba."
'Babu kowa ne a gidan, kuma kinsan munyi sauka mun ma juya bita ake tayi fa, ni hadda ma nake."
"Allah, izufin ki nawa?
"Ai na dad'e a ajin hadda tun kafin muyi sauka izufina 35"
"Kai Masha Allah, hafizai Allah ya bamu yaku."
Hafsah tayi dariya "Hmm Kinjiki."
'Sukayi shiru kad'an kowa na son jin ta bakin d'an uwanshi.'
Hafsah dai jikinta na bata akwai magana fa, da akwai abinda Aysha ke son fad'a a yadda taga yanayin ta.'
'Sai kuma, Ayshan ta daure tace "Hafsah ina Yusuf kuwa."?
'Dam' gaban Hafsah ya fad'i tare da jin wani shauk'i, tayi ajiyar zuciya sanan tace, "Aysha na rasa laifin da na mishi, ya daina nema na, ko zuwan nan na katsalandon da yake min, rabon da na ganshi yafi sati biyu tun fa ranar birthday d'in Basma.'
"Hmm, inji Aysha, lokacin da take ciro wayarta daga jaka, tayi saurin danna wajen videos ta kunna wa Hafsah ta mik'a mata. Cikin sha,awa da nishadi ta fara kallon, kafin daga bisani tayi nadamar d'ora idanunta kan wayar,
'Komai burgeta yake har zuwa lokacin da Yusuf ya bayyana cikin videon, sai kuma nishad'inta ya koma kishi, abin bai k'ara tsuma ta ba, sai da suka zo yanka cake, gashi ta kasa magana, har zuwa lokacin 'Gift, dake videon wani na k'arewa wani ke shigowa.' Aysha bata ankara ba sai k'arar Hafsah taji, tare da yin cilli da wayar gefe guda ta kifa sai wani sautin kuka mai tsuma zuciya.'
'Aysha ta san dole haka zai faru, amma yanayin sautin kukan ke tsoratata, kanaji kasan anayi ne cikin rashin sanin mafita kuma yana fitowa ne daga zuciyar data k'untata rauni ya baibaye ta matuk'a, kuma bata da mafitar hakan, kuka mai sa mai sauraro yaji kamar shima yayi kukan..
'Cikin rauni itama Ayshan, ta d'an daure ta fara magana.'
'Kiyi ha'kuri Hafsah yanzu ba lokacin kuka bane, ki k'arfafa zuciyarki don Allah, kiyi yak'i domin samarwa kanki 'yanci, in yaso daga baya kya koka, ni nasan anci amanarki, amma kiyi ha'kuri kuka mai zaiyi tasiri anan ba, don Allah ki tashi muje akwai sauran al,amarin da yafi wannan.'
Ta k'arashe maganar tana goge ragowar k'wallarta itama, sannan ta mik'a hannu tana tattaro wayarta data tarwatse, har 'Screen protector' d'inta ya fashe.'
'Hafsa tayi wata irin d'agowa cikin zafin nema, ta figo hijabinta daga kan gado batayi magana ba ta mik'e, ganin hakan yasa Aysha itama saurin mik'ewa, ta na duban fuskar Hafsah da tayi wani jajir ga kamanninta da suka d'an sauya saboda b'acin ran da take ciki. Aysha ta saka ledar kyautar Yusuf, cikin drawer Hafsah, sannan suka jera babu wanda ya kalli ma d'an uwanshi bare suyi wani zance.'
'Ita Aysha tsoron Hafsah ma, ta d'an fara ji a yadda ta ganta duk ta sauya lokaci d'aya.'
'Yayin da ita Hafsah, take jinjina irin wannan cin amana na babu zato da aka yi mata. 'Gefe guda kuma tana tunanin yanzu ina zasu je, don ita dai kawai taji tana son tabi Aysha ne zuwa ko ma ina ne.'
'Tafiya suke a hankali har suka isa get d'in gidan, hafsah tasa key ta kulle gidan, suka cigaba da tafiya, har yanzu zuciyarta na rad'adi, da tariyo mata lokacin da Basma ta rungume mata Yusuf d'inta, idanunta na zubar da zafafan, hawaye a hankali.'
Har suka tsare 'Napep' suka shiga ita dai tamkar kurma ko mutum- mutumi, zuciyarta ko fal k'una da zafi cikinta..'
*HAJEEYARKU CE DAI*👌🏼
[1/11, 1:38 PM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A Broken*
*Heart Story*
💔💔
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to: Unique In Your Love Heart Members*
📄 *32*
"Hello,"
"Am gani a gate enku."
"Ok, ki shigo kinji"
'Ya kira mai gadi, a waya yace ya rakata har k'ofar sashinshi.'
Tana shigowa, mai gadin ya mik'e da saurinshi, "Barka da zuwa Hajiya"
'Ta kalleshi kawai.' Ya shige gaba, tana binshi a baya, yana mamakin wacce irin bak'uwa ce wannan..??
'Asanin shi dai Yusuf, yana yawon daren shi, amma bai tab'a ganin ya kawo wata, cikin gidan su ba.'
'Azuciyarshi yace 'Allah ya shirya'
Ba wai don yana zargin, Yusuf d'in da wani abu bane, amma, bai ga dalilin da idan zaku tattauna wani abu da mace ba, har sai ka kirata gida kun keb'e..
'Suna isa dai dai bakin k'ofar wajen nashi, yai mata nuni da k'ofar, "Hajiya nan ne shashin oga Yusuf, d'in."
Ta yatsina fuska, sannan ta ce "Ok."
'Ta murd'a k'ofar a hankali, ta sanya k'afarta cikin wani madaidaicin, falo.
'A kwance ta hango shi, kan kujera 'Three seater', daga shi sai singlet da gajeren wando, ta d'an so razana, amma sai ta dake.'
'Ta k'arasa cike da yanga, ta nemi kujera mai kallon tashi ta zauna.'
'Shi kuma tunda ta bud'e k'ofar ya k'ura mata ido, har ta zauna, sannan ya mik'e zaune ya fuskanto ta sosai, ita kuma ta wani lumshe ido ta bud'e.'
'Ya saki murmushin daya nuna mata yaji dad'in ganinta sosai, sannan ya bud'e baki ya fara magana cikin k'asa da murya.'
"You're welcome"!
Tayi murmushi mai sauti, "Hmm, thank you."
'Ya karkatar da kai, "Zaki, iya..
zuwa.. dama"?
Tayi fari da idonta, "Hmm why not"?.
"Yai murmushi thanks alot"
Ahankali ya mik'e ya ya isa fridge ya d'akko lemo da ruwa da d'an plate da cup, duk a ciki, sannan ya tako har kujerar da take zaune, ahankali ta dinga jin fad'uwar gaba, amma sai tayi k'arfin hali ta dake, a zuciyar ta tana kishin ka da yaga hakan ya rainata, sai ma ta dinga k'ak'alo murmushin kan leb'e tana yi.
🤔 _k'arfin hali_😅
'Bayan ya ajye su akan d'an wani table, sannan ya zauna a wajen da yaji ya mishi, wato daf da ita sosai, sannan yayi gyaran murya,
"Hmm Basma ma friends"
"Hmm, Yusuf, ya akayi ne"
'Cikin juyayyiyar hausarshi yace,
"Hmm mene ma ba,ayi bane, ke dai ki sha lemon nan kinji."
'Ya sunkuiya yana zuba mata a cup sannan ya mik'a mata, "Thank you."
'Tace dashi.'
Ta d'an sha yadda bazaice tayi k'auyancin kinsha ko kuma ta shanye ba."
'Ta dire kofin yayin da shi kuma ya ke kallonta cikin k'ura ido, tana k'ara k'awatuwa a idanunshi, wani b'angaren tana kore Hafsah, ta hanyar karanto mishi idan, itace bazata iya ba, saboda gidadancin ta, (ita Hafsan)
'Ita dai Basma jiran, cewar shi takeyi wato taji, ('Dalilin gayyato ta)
'Hum, yai wata gauruwar ajiyar zuciya sanan ya ce cikin muryar da take bayyana mata irin halin da ya ke ciki.'
"Am basma,.. Nasan kinyi mamakin inviting enki dana yi, koh,? '
'So kada ki damu, ni ina so ne mu k'ulla friendship ni da ke, yafi na da, and then ina so ki bani shawara da kuma k'arin bayani akan Hafsah."
'Ya k'arasa yana zuba mata idanunshi, ita kuma sai da ta d'anyi kokawa da tunaninta kafin ta k'arasa fahimtar inda dunkulellen zancen ya nufa.'
'Ta kuma jiyo muryarshi yana cewa, "kin dai son irin mu,amalan da Hafsah ke min, please kina ganin ya za,ayi na jure zama da ita haka,"
Basma tayi murmushi azuciyarta, amma sai ta gimtse da taji yace, "I don't mean zan rabu da ita ne, sai dai na fad'a mata zamanmu ba zai yiwu haka ba,.. saboda ita ne fa, for more than 1 year duba rabona da..".
'Sai ya katse zancen babu shiri, ita kuma ta hau ajiyar zuciya.'
"Dole ne kinga na samar wa kaina, solution koh"
'Ya fad'i hakan cikin k'aramin sauti.'..
'A gidan su Hafsa kuwa, tana kwance, a falo kan kujera, taji sallama, ta amsa tare da tashi zaune don tabbatar wa da wacce take tunani.'
"A Taheer!!
'Ta fad'a cikin k'araji suka rungume juna.
'Aisha dai ahankali take sakin murmushi kawai.'
'Hafsah ta shiga hidima da ita, ta kawo mata lemo, ruwa da snacks har abinci ma da yaji nama acikin shi.'
'Aisha ta shiga tab'awa tana jimanta yadda zata ruguzawa Hafsah d'an farin cikin da ta ganta ciki yanzu, amma sai ta sami k'warin guiwa da ta tuna babu ishashshen lokacin b'atawa.
'Tayi goron numfashi cikin rashin sanin ta ina zata fara.'
"Oh dama zaki zo gidanmu Aysha."
"Hahh gani kuwa"
Kinyi k'okarin ganewa."
"Hmm Koh."
"Sosai ma, don ma babu wuya gidan."
"Hakane kam."
"Ma manku bata nan ne"?
"Eh wllhi ba nisa tayi ba dai ta d'anje barka ne."
"Hmm, lallai kam shine ke kuma baki tafi islamiyya ba."
'Babu kowa ne a gidan, kuma kinsan munyi sauka mun ma juya bita ake tayi fa, ni hadda ma nake."
"Allah, izufin ki nawa?
"Ai na dad'e a ajin hadda tun kafin muyi sauka izufina 35"
"Kai Masha Allah, hafizai Allah ya bamu yaku."
Hafsah tayi dariya "Hmm Kinjiki."
'Sukayi shiru kad'an kowa na son jin ta bakin d'an uwanshi.'
Hafsah dai jikinta na bata akwai magana fa, da akwai abinda Aysha ke son fad'a a yadda taga yanayin ta.'
'Sai kuma, Ayshan ta daure tace "Hafsah ina Yusuf kuwa."?
'Dam' gaban Hafsah ya fad'i tare da jin wani shauk'i, tayi ajiyar zuciya sanan tace, "Aysha na rasa laifin da na mishi, ya daina nema na, ko zuwan nan na katsalandon da yake min, rabon da na ganshi yafi sati biyu tun fa ranar birthday d'in Basma.'
"Hmm, inji Aysha, lokacin da take ciro wayarta daga jaka, tayi saurin danna wajen videos ta kunna wa Hafsah ta mik'a mata. Cikin sha,awa da nishadi ta fara kallon, kafin daga bisani tayi nadamar d'ora idanunta kan wayar,
'Komai burgeta yake har zuwa lokacin da Yusuf ya bayyana cikin videon, sai kuma nishad'inta ya koma kishi, abin bai k'ara tsuma ta ba, sai da suka zo yanka cake, gashi ta kasa magana, har zuwa lokacin 'Gift, dake videon wani na k'arewa wani ke shigowa.' Aysha bata ankara ba sai k'arar Hafsah taji, tare da yin cilli da wayar gefe guda ta kifa sai wani sautin kuka mai tsuma zuciya.'
'Aysha ta san dole haka zai faru, amma yanayin sautin kukan ke tsoratata, kanaji kasan anayi ne cikin rashin sanin mafita kuma yana fitowa ne daga zuciyar data k'untata rauni ya baibaye ta matuk'a, kuma bata da mafitar hakan, kuka mai sa mai sauraro yaji kamar shima yayi kukan..
'Cikin rauni itama Ayshan, ta d'an daure ta fara magana.'
'Kiyi ha'kuri Hafsah yanzu ba lokacin kuka bane, ki k'arfafa zuciyarki don Allah, kiyi yak'i domin samarwa kanki 'yanci, in yaso daga baya kya koka, ni nasan anci amanarki, amma kiyi ha'kuri kuka mai zaiyi tasiri anan ba, don Allah ki tashi muje akwai sauran al,amarin da yafi wannan.'
Ta k'arashe maganar tana goge ragowar k'wallarta itama, sannan ta mik'a hannu tana tattaro wayarta data tarwatse, har 'Screen protector' d'inta ya fashe.'
'Hafsa tayi wata irin d'agowa cikin zafin nema, ta figo hijabinta daga kan gado batayi magana ba ta mik'e, ganin hakan yasa Aysha itama saurin mik'ewa, ta na duban fuskar Hafsah da tayi wani jajir ga kamanninta da suka d'an sauya saboda b'acin ran da take ciki. Aysha ta saka ledar kyautar Yusuf, cikin drawer Hafsah, sannan suka jera babu wanda ya kalli ma d'an uwanshi bare suyi wani zance.'
'Ita Aysha tsoron Hafsah ma, ta d'an fara ji a yadda ta ganta duk ta sauya lokaci d'aya.'
'Yayin da ita Hafsah, take jinjina irin wannan cin amana na babu zato da aka yi mata. 'Gefe guda kuma tana tunanin yanzu ina zasu je, don ita dai kawai taji tana son tabi Aysha ne zuwa ko ma ina ne.'
'Tafiya suke a hankali har suka isa get d'in gidan, hafsah tasa key ta kulle gidan, suka cigaba da tafiya, har yanzu zuciyarta na rad'adi, da tariyo mata lokacin da Basma ta rungume mata Yusuf d'inta, idanunta na zubar da zafafan, hawaye a hankali.'
Har suka tsare 'Napep' suka shiga ita dai tamkar kurma ko mutum- mutumi, zuciyarta ko fal k'una da zafi cikinta..'
*HAJEEYARKU CE DAI*👌🏼
[1/11, 1:38 PM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A Broken*
*Heart Story*
💔💔
Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to: Unique In Your Love Heart Members*
📄 *32*