Sashe 30
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
*Kafin* su Hafsah, su isa gidan, yusuf da Basma, sun kai wani d'an mataki a shagala..'
( To dama abu ne da kowa ke buk'ata, sai kuma suka keb'e, sannan ga taimakon tattaunawar da sukayi ta tsawon wajen mintuna ashirin, wacce yawancinta Yusuf ne ya bayyana wa Basma cikinsa kaf, da duk wani sirri nashi, sanan ya b'ige da bata labarin rayuwarshi har da nuna mata photonan nan shi da yan matanshi na can wad'anda suka d'auka a yanayi daban daban.
Yusuf ya k'arasa hure mata kunnenta, sannan ya b'ige ga neman taimakonta bisa halin da yake ciki.')
Komai yayi tasiri a zuciyarta kuma sai yau ta k'ara yabawa dashi sosai, don haka, ta cire tsoron komai, bisa bin umarnin zuciyarta na ganin yanzu ne ya dace itama taji dad'in rayuwarta.'..
🤔
Suna dira daga 'Napep' yar tafiya kad'an sukayi sai ga gidan da Aysha ta tabbatar shine, ta kuma duba address d'in dake cikin wayarta.'
'Suka tura gate suka shiga, mai gadin wanda bazaifi shekara 37 ba, cikin shiga sosai kamar ba mai gadi ba, kana ganinshi kasan gidan 'yan boko yake aiki, yasa earpiece a kunne sai kad'a kai yake yi.'
Aysha ta mishi magana "Am kai yusuf na nan koh'?
Yace "Yes tare da kad'a kai.'
'Kaimu part enshi Kai tsaye tayi maganar'.
Dam gaban Hafsah yayi wata mummunar fad'uwar gaba banda wacce take ciki, tun d'azu.' ta ware idanunta ta kalli Aysha, kallon tuhuma dama gidan su Yusuf ta kawo ta.'??
Mai gadi, ya dakatar da tunaninta da cewa.' "Am sorry gaskiya oga baicemin zaku zo ba, so ku kirashi idan yace ku shiga sa..
Kai Malam bama son iskancin banza kasan matsayin mu kuwa..?
Wuce muje ka nuna mana idan yaso ka tsaya kaga mu su waye a wajen 'Yusuf"??
'Aysha ta fad'a cikin fad'a-fad'a, cikin son yi mishi baraza.'
Baiyi magana ba ya wuce gaba suka bishi, yana tunanin wanne irin bak'in mata yau 'Oga Yusuf' yakeyi haka.'?
Har cikin part d'in ya kaisu sai da suka je dai dai k'ofar falonshi mai gadin ya tsaya, yana shirin yin 'Knocking' Aysha ta d'aga mishi hannu ta dakatar da shi.'
"No jeka thank you."
Batayi wani tunani ba ta tura k'ofar ta fad'a ciki Hafsah ma taga bata da zab'i illa ta bita, dukkansu wara idanu suke, kafin idanunsu su gama wayewa a cikin daki'n idon Hafsah ya hango mata su shi da wata da bata gama tantance wacece ba.'
'Zuciyarta ta buga da wani mugun k'arfi, ta yi saurin mutstsike idonta, ta k'ara dora shi kansu'
Nan ta hau waige waige kuma, idanunta yakai kan kofin Glass dake kan d'an table d'innan ta rarumo shi ta d'aga Kenan,..
Jikinsu ya basu akwai mai kallon su, babu shiri suka rabo, tare da juyowa sosai cikin muguwar fargaba.'
'Tsoro ne sosai ya shigi Yusuf yadda yaga Hafsa babu tsammani.'
'Ita kuma Basma ta hau soshe-soshen k'arya.'
'Zuciyar Hafsah ta tsaya cak cikin rashin sanin abin yi'
'Ko kwakwkwaran motsi ta kasa.'
Sai wani jiri jiri ma da taji yana kwasarta.'
'Me idonta ke nuna mata shigen al,mara,? Basma k'awarta? da Yusuf mijin da take fata.'
Ta d'an rufe idonta ta bud'e don tabbatarwa.'
'Aysha ce tayi k'arfin halin tafa hannayenta tare da cewa, dubunku ta cika munafukai, 'yan iska.. ' shed'anu.. Maciya amana, ta nuna Yusuf, lallai ka cika d'an iskan gaske..'
'Tana k'arasa fad'ar hakan Yusuf ya mik'e a zafafe ya wanke fuskar ta da mari.' tayi saurin rik'e kuncin, tana masa kallon k'askanci, shikuma sai huci yake yi.'
'Sai lokacin bakin Hafsa ya bud'e daga kullewar da yayi, ta mik'e cikin zafin nama tayi kan Yusuf.'
'Taci kwalar shi cikin rashin hayyaci, ta fara magana cikin kuka, da huci,
"k'arya kake Yusuf, yaushe ka zama munafikin mata..? Yaushe ka kware a yaudara..? Yaushe ka zama d'an iska??.. Yusuf ka cuceni.."
"Yanzu koh zaka aikata haka,.. karasa dawa zakuci amanata sai Basma..??
"Wayyo Allah, Yusuf ka cuceni wallahi, bazan yafe maka ba..'
'Tana k'arasa fad'in haka, ta sakeshi tare da hankad'ashi da duk k'arfinta.'
'Tun da tayi masa rik'on ya gaza aiwatar da komai banda kallonta da yake, sai tunani da dama cikin zuciyarshi.'
'Yasan dai bai kyauta mata ba, amma to ya zaiyi da rayuwarshi.'?
'Tana hankad'a shin yai saurin zama a kujera domin ya kusa fad'uwa, ya dafe kai cikin rashin sanin mafita.'
'Kamin yayi wani yunkuri yaji saukar wani bahagon mari a kuncinsa, asukwane ya d'ago don ganin wanne mai tsautsayin ne ya mare shi.'
'Aysha ya gani tsaye akansa tana huci, azuciye yakai hannu da nufin yi mata wani wawan duka, amma sai yaji an rik'e hannunshi, ya juyo rai a b'ace don ganin waye ya katse mishi hanzarin sa.'?
'Hafsah ya gani ta dakatar da shi cikin rawar murya mai rauni tace tana hawaye, "Yusuf dukanta zakayi, don ta rama abinda ka mata."
"Yusuf ka koya min darasi kuma na koya..' me nayi maka da ka saka min da wannan mummunar sakayyar.? Yusuf ka yiwa rayuwata illah, sai da na gama yarda da kai sannan kaci amanata..'
'Ta durkushe a gurin tana kuka mai tsuma rai.'
Shima a sanyaye ya durk'usa gabanta.'
"Hafsah believe me, banci amanarki ba, bakya tausayina koh, kiss and even hug baki rab'a yimin ba as my girlfriend, amma, Basma fa ita ta..''
"Ya isa! Ya isheka!! Ta fad'a cikin wani fad'a da wata murya mai k'ara gami da kuka, da haka basma ta fini a gurinka koh Yusuf, ta fad'a tana nuno, Basma data sab'a jakarta a kafad'a, tana gyara mayafi don shirin rantawa a na kare kafin hankalin Hafsa ya dawo ta juyo kanta.'
Nibance ta fiki wajena ba, idan ta bani abinda kika hanani kinga kowa matsayinshi daban',..
"Kai wanne iri ne Yusuf mai yasa baka ji ne, ehe, Meyasa ba zaka d'auka hakan laifi bane ko a addini.."
'Maganganun datake yi mishi kenan.'..
"Ta juya ga Basma, kin bani mamaki,kin ci amanata in sha Allah Allah sai saka min.."
'Ta finciko Aysha suka fita, inda Yusuf da Basma suka tsaya kallon kallo a junansu.'..
*Yours*
*Khareemerh T Mansur*👌🏼
[1/12, 1:56 PM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken heart story*
💔💔
( To dama abu ne da kowa ke buk'ata, sai kuma suka keb'e, sannan ga taimakon tattaunawar da sukayi ta tsawon wajen mintuna ashirin, wacce yawancinta Yusuf ne ya bayyana wa Basma cikinsa kaf, da duk wani sirri nashi, sanan ya b'ige da bata labarin rayuwarshi har da nuna mata photonan nan shi da yan matanshi na can wad'anda suka d'auka a yanayi daban daban.
Yusuf ya k'arasa hure mata kunnenta, sannan ya b'ige ga neman taimakonta bisa halin da yake ciki.')
Komai yayi tasiri a zuciyarta kuma sai yau ta k'ara yabawa dashi sosai, don haka, ta cire tsoron komai, bisa bin umarnin zuciyarta na ganin yanzu ne ya dace itama taji dad'in rayuwarta.'..
🤔
Suna dira daga 'Napep' yar tafiya kad'an sukayi sai ga gidan da Aysha ta tabbatar shine, ta kuma duba address d'in dake cikin wayarta.'
'Suka tura gate suka shiga, mai gadin wanda bazaifi shekara 37 ba, cikin shiga sosai kamar ba mai gadi ba, kana ganinshi kasan gidan 'yan boko yake aiki, yasa earpiece a kunne sai kad'a kai yake yi.'
Aysha ta mishi magana "Am kai yusuf na nan koh'?
Yace "Yes tare da kad'a kai.'
'Kaimu part enshi Kai tsaye tayi maganar'.
Dam gaban Hafsah yayi wata mummunar fad'uwar gaba banda wacce take ciki, tun d'azu.' ta ware idanunta ta kalli Aysha, kallon tuhuma dama gidan su Yusuf ta kawo ta.'??
Mai gadi, ya dakatar da tunaninta da cewa.' "Am sorry gaskiya oga baicemin zaku zo ba, so ku kirashi idan yace ku shiga sa..
Kai Malam bama son iskancin banza kasan matsayin mu kuwa..?
Wuce muje ka nuna mana idan yaso ka tsaya kaga mu su waye a wajen 'Yusuf"??
'Aysha ta fad'a cikin fad'a-fad'a, cikin son yi mishi baraza.'
Baiyi magana ba ya wuce gaba suka bishi, yana tunanin wanne irin bak'in mata yau 'Oga Yusuf' yakeyi haka.'?
Har cikin part d'in ya kaisu sai da suka je dai dai k'ofar falonshi mai gadin ya tsaya, yana shirin yin 'Knocking' Aysha ta d'aga mishi hannu ta dakatar da shi.'
"No jeka thank you."
Batayi wani tunani ba ta tura k'ofar ta fad'a ciki Hafsah ma taga bata da zab'i illa ta bita, dukkansu wara idanu suke, kafin idanunsu su gama wayewa a cikin daki'n idon Hafsah ya hango mata su shi da wata da bata gama tantance wacece ba.'
'Zuciyarta ta buga da wani mugun k'arfi, ta yi saurin mutstsike idonta, ta k'ara dora shi kansu'
Nan ta hau waige waige kuma, idanunta yakai kan kofin Glass dake kan d'an table d'innan ta rarumo shi ta d'aga Kenan,..
Jikinsu ya basu akwai mai kallon su, babu shiri suka rabo, tare da juyowa sosai cikin muguwar fargaba.'
'Tsoro ne sosai ya shigi Yusuf yadda yaga Hafsa babu tsammani.'
'Ita kuma Basma ta hau soshe-soshen k'arya.'
'Zuciyar Hafsah ta tsaya cak cikin rashin sanin abin yi'
'Ko kwakwkwaran motsi ta kasa.'
Sai wani jiri jiri ma da taji yana kwasarta.'
'Me idonta ke nuna mata shigen al,mara,? Basma k'awarta? da Yusuf mijin da take fata.'
Ta d'an rufe idonta ta bud'e don tabbatarwa.'
'Aysha ce tayi k'arfin halin tafa hannayenta tare da cewa, dubunku ta cika munafukai, 'yan iska.. ' shed'anu.. Maciya amana, ta nuna Yusuf, lallai ka cika d'an iskan gaske..'
'Tana k'arasa fad'ar hakan Yusuf ya mik'e a zafafe ya wanke fuskar ta da mari.' tayi saurin rik'e kuncin, tana masa kallon k'askanci, shikuma sai huci yake yi.'
'Sai lokacin bakin Hafsa ya bud'e daga kullewar da yayi, ta mik'e cikin zafin nama tayi kan Yusuf.'
'Taci kwalar shi cikin rashin hayyaci, ta fara magana cikin kuka, da huci,
"k'arya kake Yusuf, yaushe ka zama munafikin mata..? Yaushe ka kware a yaudara..? Yaushe ka zama d'an iska??.. Yusuf ka cuceni.."
"Yanzu koh zaka aikata haka,.. karasa dawa zakuci amanata sai Basma..??
"Wayyo Allah, Yusuf ka cuceni wallahi, bazan yafe maka ba..'
'Tana k'arasa fad'in haka, ta sakeshi tare da hankad'ashi da duk k'arfinta.'
'Tun da tayi masa rik'on ya gaza aiwatar da komai banda kallonta da yake, sai tunani da dama cikin zuciyarshi.'
'Yasan dai bai kyauta mata ba, amma to ya zaiyi da rayuwarshi.'?
'Tana hankad'a shin yai saurin zama a kujera domin ya kusa fad'uwa, ya dafe kai cikin rashin sanin mafita.'
'Kamin yayi wani yunkuri yaji saukar wani bahagon mari a kuncinsa, asukwane ya d'ago don ganin wanne mai tsautsayin ne ya mare shi.'
'Aysha ya gani tsaye akansa tana huci, azuciye yakai hannu da nufin yi mata wani wawan duka, amma sai yaji an rik'e hannunshi, ya juyo rai a b'ace don ganin waye ya katse mishi hanzarin sa.'?
'Hafsah ya gani ta dakatar da shi cikin rawar murya mai rauni tace tana hawaye, "Yusuf dukanta zakayi, don ta rama abinda ka mata."
"Yusuf ka koya min darasi kuma na koya..' me nayi maka da ka saka min da wannan mummunar sakayyar.? Yusuf ka yiwa rayuwata illah, sai da na gama yarda da kai sannan kaci amanata..'
'Ta durkushe a gurin tana kuka mai tsuma rai.'
Shima a sanyaye ya durk'usa gabanta.'
"Hafsah believe me, banci amanarki ba, bakya tausayina koh, kiss and even hug baki rab'a yimin ba as my girlfriend, amma, Basma fa ita ta..''
"Ya isa! Ya isheka!! Ta fad'a cikin wani fad'a da wata murya mai k'ara gami da kuka, da haka basma ta fini a gurinka koh Yusuf, ta fad'a tana nuno, Basma data sab'a jakarta a kafad'a, tana gyara mayafi don shirin rantawa a na kare kafin hankalin Hafsa ya dawo ta juyo kanta.'
Nibance ta fiki wajena ba, idan ta bani abinda kika hanani kinga kowa matsayinshi daban',..
"Kai wanne iri ne Yusuf mai yasa baka ji ne, ehe, Meyasa ba zaka d'auka hakan laifi bane ko a addini.."
'Maganganun datake yi mishi kenan.'..
"Ta juya ga Basma, kin bani mamaki,kin ci amanata in sha Allah Allah sai saka min.."
'Ta finciko Aysha suka fita, inda Yusuf da Basma suka tsaya kallon kallo a junansu.'..
*Yours*
*Khareemerh T Mansur*👌🏼
[1/12, 1:56 PM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken heart story*
💔💔