Sashe 68
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wayar da ke kunnenta ta shiga k'arar da tasa ta dawo daga tunanin ta take ta kullawa a zuciyar ta.
Tayi saurin zare wayar, sunan Jamila ta gani.
Ta saki ajiyar zuciya, ta daga kiran.
Hello."
Jamila tace.
Itama ta amsa da Hello
Jamila kina lafiya.
Cikin muryar ta da dama ta dad'e da chanjawa, tace, "I'm fine. "Ya mutanen gidan ya mum."?
Hafsah taji dad`in hakan..
Lafiya lau." tace tana dan murmushi tace, "Bayan kince zaki zo baki zo d`in ba."?
Wallah babu time ne, ina ta son inzo, but zaki ganni, savoda zanje Dubai nan da two weeks so zan shigo unguwar kafin na tafi."
Gaban Hafsah ya fad'i. "Dubai kuma."?
"Kada dai Jamila tayi shaharar zama _International."_
Don haka taga asarar barin Jamila batare da ta nemi k'arin bayani ba. Da sauri tace.
Dubai me zaki je yi Dubai."?
"Zanyi rakiya ne."!! Jamila tayi magana tana wata 'yar siririyar dariya.
Kan Hafsah yayi wata iriyar sarawa.
Tana son ta k'ara tambayar Jamila, _Wa zata raka haka."?_
Amma kuma bata son Jamilar taga kamar tana binciken ta ne. Don haka tayi shuru kawai.
Sai ta juyo Jamila na cewa. "Thank you, ki gaida mama, bari na d'aga wani kira.
"Okay thank you bye bye.
Hafsah tace...
📝
*HAJEEEYAH KHAREEMERH*
[17/03, 2:46 p.m.] UMAIMA BASHEER: ♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so (Guba ne)*
💔💔
*By*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Khareemerh)*
*Dedicated to unique in your love heart*
📄 *56*
_NAILA group 1 ina godia da Soyayyar ku... Espclly #ummita_😊😊
_Sayyada_ kema Inayinki. (NAILA group 2)
*Team Ukhasha
*Team Hafsah.
Inajin dad`in comment d'inku.💃🏼💃🏼💃🏼
*Ranar* da ta biyo baya, bai kirata ba sam tun daga safiya har wata wayewar garin.
Hafsah ta sanya kanta cikin tsarguwa. Amma kuma tanajin ba zata iya kiranshi ba.
___________________
Yau gaba d'aya busy yake, abubuwa sun mishi yawa, bayan dawowar shi daga office, yayanshi Dr. Sunusi yace ya same shi a gida, zasu tattauna.
Yana dawowa abinci kawai yaci, yayi wanka sannan yayiwa Hajiya sallama ya wuce.
Bayan hira da sukayi ta zumunci, Dr. Sunusi ya bujurowa da Ukhasha maganar da yasa ya kirashi.
"Ukhasha."!!
Ukhashatu ya amsa.
"Naam Yaya.!!
Dama wata _share_ ce zan maka talla ko zaka sa kud'inka kaima aciki..
Ukhashatu ya bada gaba d'ayan hankalinshi ga yayan nashi.
Dr. Sunusi ya cigaba da magana.
Wani d'an k'aramin company ne, na had`in guiwa mukeso mu bude ni da abokai na mu shidda, to kuma mun duba munga muna da buk'atar k'arin kud'i shine muke bukatar k'arin mutum d'aya.
Ukhasha ya gyara zama. Okey Yaya, kamar nawa ake buk'atar kowa ya saka."?
Ba wai bukata ake kowa sai yasaka daidai da na kowa ba. Zaka iya saka ko nawa kake dashi kawai, tunda za,a dinga raba ribar ne, daidai da yadda kudin mutum yake aciki.
Ukhashatu ya jinjina kai, Okey na gane Yaya, amma kamar nawa kake ganin ni zansa."?
Um..To." Inji Doctor. Sannan ya kalli ukhashatu.
Zaka iya saka 4million, ko da rabi ma.!!
Ukhasha yayi murmushin gefen kunci.
"Doctor, ansan nauyin aljihun fah.
Na sani.!
Inji Dr Sunusi yana murmushi shima.
"Ka saka 4million d`in dai."
Ukhasha yayi ajiyar zuciya a hankali, Dr. ya kalle shi da alamar tambaya. Ukhasha yace, "da inada wani lissafi da nakeyi ne."
Dr. Sunusi yayi murmushi, wanne tunani kuma."?
Ukhashatu ya sunkuyar da kai, yana shiga matsa k'afar shi, dama a kasa suke dukan su a zaune.
Dariya ya bawa, Dr. ma sai da ya gama dariyar sannan yayi magana.
Aure zakayi."? Bai barshi ya bada amsa ba ya d'ora.
Ka gaji da zaman gwaurontakar kenan...
Ukhasha yayi wani dan murmushi. "A,a fa Yaya."
To mene tunanin naka idan ba shi ba.
Yayi shuru, don bashi da amsa.
Hmm, yanzu dai ka nemo, 4m. kawai kaidai, zamuji dad`in abin fa idan ya kankama.
Okey in sha Allah."
Inji Ukhasha.
Zuwa Yaushe za,a karbi kud'in.
Nan da wata d'aya muke son mu fara shirya komai, amma muna yin meeting akan yadda abin zai kankama, gobe ma muna dashi, da daddare sai ka shigo muje.!!
Okey, in sha Allah.
Am naji Hajiya na cewa zatayi retire koh."?
"Eh haka tace, nan da wata d'aya ne."
Gud, ai gwara ta huta.!! Inji Dr. Sannan ya shiga wata maganar.
"Yaushe ma Abba yace zamuje gidan gonar nan don na manta.
Nan da sati d'aya ne." Cewar ukhasha.
Ai abin ne da yawa abubuwan sunyi yawa.
"Ana kokari ai."
Inji ukhashatu, Naji yace yana so ne, ya k'ara fad'ad'a wajen."
"Yayi kyau hakan ai, kaga ya dad'e bai je duba gurin ba fah.
Ukhasha ya jinjina kai, "Eh amma
"yana tura ni akai-akai ai, kuma naga babu laifi ma,aikatan suna kula da wajen yadda ya dace.!!
So ko zamu bude namu d'an k'aramine haka koda iya kaji ne, da kifi sai mu saka. Cewar Doctor yana dariya.
Ukhasha ya taya shi dariyar shima. "Hmm Doctor kenan.!!
Cikin nutsuwa yake jawo hakalin Ukhashatu kan abin da cewa, "Ina da wani tunanine, kuma dana bujurowa da Abba shi naga ya nuna jin dad'inshi har ya sanyawa abin albarka ma."
Ukhashatu ya kalle shi irin kallon neman k'arin bayani.
Cikin nutsuwa doctor yace, inaso mu bude wani kasuwanci dukanmu har matan ma, kai hatta mahseem sai ansa mata nata kason aciki.!
Ukhashatu ya waro ido.
Doctor ya jinjina kai, Yes, wannan zai kara kawo had`inkai, sannan kuma gaba ake ji ba baya ba."
Ukhashatu ya jinjina kai. "Hakane..abun yayi kyau.
Baka ga yadda Abba ya d`auki abin ba, daga yi mishi zancen ni na zaci ma yayi maka zancen.
Ukhashatu ya girgiza kai.
"A,a" Amma waye zai sawa su yaran tunda kace har Mahseem."?
Doctor yace yana dariya. "Abba ne.!! Kuma ai ba wani abu mai yawa zai maka musu ba, tunda kasuwanci ne irin na kayan amfani irin na kasuwa da kadan zamu fara, kuma za,a saka equal ne babu mace babu namiji kowa _one hundred thousand._ Yayi kyau Yaya Allah ya bar zumunci ya taimake mu, Allah ya taimaki Abban."
"Amiin ya Allah. Inji Dr. Sannan ya kuma kallon Ukhashatu.
A ina ka sami yarinyar ne."?
Ukhasha yayi saurin bude baki, "Am ai bamu gama daidaitawa da ita bama."
"Hmm, koh.."? Baka sanarwa da su Abba ba kenan."?
Ukhashatu ya daga kai alamar, "Eh."
Cikin nutsuwa doctor yake nusar dashi. "Kayi kokari dai, kayi abinda zai farantawa su Abba."
Ukhashatu ya gyada kai, In sha Allah, bamu dad'e da sanin juna bane shiyasa."
Okey, nagane Allah ya tabbatar da alkhairi.!
"Amin Yaya. Sannan ya duba agogon hannunshi, "Bari na tafi dare yayi yaya.
Okey, ba zaka shiga cikin ku gaisa ba."?
To bari na shiga naga 'yar rigima.
Sukayi dariya sannan suka mik'e a tare.
Suka shiga da sallama. Fadeel na jin muryar auncle ya taho da gudu yana murna "uncle!! uncle!! Ukhashatu ya d`auke shi, ya daga shi sama suna dariya.
"Kaii Kaii Kaii." kai fa ka girma yanzu, kayi nauyi "Ya Fadeel zan daina d'aukarka kai da "Ãrif. Na'eemah kawai zan dinga d'auka.!! Ukhashatu ya fad'a sanda yake sauke shi.
Suka zauna a Kujera yaron ya zauna kusa da shi."
"Uncle su sunyi bacci."
"Kai meyasa bakayi bacci ba toh."?
"Assignment nake yi, nima yanzu zanyi bacci, aunty dinmu tace ina da k'ok'ari!!
Allah, ai na sani dama _my boy is a gifted.!!_
Suka tafa shida Fadeel d`in suna dariya.
"Au uncle ina yini."?
Inji Fadeel harda d'an rank'wafawa. Doctor da Ukhashatu suka sheke da dariya, doctor yace, "Au sai yanzu aka tuna da gaisuwar."?
"Mantawa nayi Abba.!! Inji Fadeel.
To Lafiya lau, Fadeel d`ina kana lafiya."? Inji ukhashatu.
Lafiya lau uncle.
Suna cikin haka, maman yaran ta fito daga d'aki.
Au Engr. Sai yanzu kenan ka shigo koh."?
Afwan auntie ina yini."?
Lafiya lau, yasu Hajiya da Abba."?
Lafiya lau suke."?
Ta dan sami guri ta zauna.
"To yasu Fadwa M aryam, kwana biyu basu lek'oni ba."
"Suna nan kalau, bari na wuce ma kada dare yayi min."
Daga shigowa kuma."? Inji aunty Jamila.
"Dare ne zaiyi min shiyasa"
Eh, kuma kazo kawar taka na bacci koh."?
Eh fa, ai gobe ma zan dawo in sha Allah."
"Tom sai kazo d`in.
Ya mik'e Fadeel ma ya mik'e ya rik'e hannunshi.
Ya kalli, yayanshi. Sai da safe yaya."
Tom ka gaida gida ukhashatu sai goben, ka gaida su Abba da hajiya.
Zasuji, yace, sannan ya juya ga aunty Jamila, Tom aunty sai da safe, Allah ya tashe mu lafiya, agaida Hajiya da mama."
"Zasuji sosai, yace.
Ta kamo hannun Fadeel, oh baby zo kaje ka kwanta kaji.
Ya noke k'afada "A,a ni uncle zan bi."
Ukhashatu yayi dariya, Aa aboki ka bari gobe zan dawo sai muje gidan Abba amma yanzu kaga dare yayi koh."
Ya daga kai, a sanyaye da alama bai so ba."
Ukhashatu ya sake shi, sannan ya laluba aljihun shi babu, ya zaro 500. "Ungo Aboki."
Ya damk'awa yaron.
Asai chocolate yau na manta ban taho dashi ba.
Yaron yasa hannu biyu ya k'arba yana murna.
Thank you auncle, ka gaida gida.
Aunty Jamila tace, Allah dama ukhasha shiyasa yaran nan suke makale maka, ka daina basu kudi don Allah idan babu alawa a hak'ura.
Yayi murmushi kawai, yana dagawa yaron hannu "Bye bye.
Shima yaron ya daga mishi "Bye bye uncle gud night.!!
Ukhasha ya fita yana murmushi.
__________________
Daya koma gida, 11 na dare ta wuce, kafin yayi wasu al,adu da ya saba kafin kwanciya bacci har sha biyu tayi. Dole ya hakura da kiranta da yayi niyya. Gashi ya gaji likis, yana kwanciya babu jimawa bacci ya d`auke shi mai cike da mafarkanta..
_________________
Tana ta sak'awa da kwancewa akan neman dalilin rashin jin shi gaba-d`aya yau, amma tunanin ta yafi fad'awa kan cewa ya gaji ne, ya yanke hukunci. Hankalinta ya dugunzuma, meyasa bata mishi koda SMS bane bayan wayar da sukayi. Ta shiga yiwa kanta fad'a, tabbatas da gaskiya r shi, su fa ba yara bane 'yan secondary da zata dinga yi mishi abubuwa irin haka.
Dole ne, ta sami hanyoyin fahimtar dashi abinda take ji game dashi.
Ta lalubi wayarta, akan wayar taga dare yayi har k'arfe 11:30pm, taji kamar ta mishi text da _I love you.!_ har ta shiga wajen yin typing message, sai kuma taja dan siririn tsaki, ta fasa.
Tayi saurin zare wayar, sunan Jamila ta gani.
Ta saki ajiyar zuciya, ta daga kiran.
Hello."
Jamila tace.
Itama ta amsa da Hello
Jamila kina lafiya.
Cikin muryar ta da dama ta dad'e da chanjawa, tace, "I'm fine. "Ya mutanen gidan ya mum."?
Hafsah taji dad`in hakan..
Lafiya lau." tace tana dan murmushi tace, "Bayan kince zaki zo baki zo d`in ba."?
Wallah babu time ne, ina ta son inzo, but zaki ganni, savoda zanje Dubai nan da two weeks so zan shigo unguwar kafin na tafi."
Gaban Hafsah ya fad'i. "Dubai kuma."?
"Kada dai Jamila tayi shaharar zama _International."_
Don haka taga asarar barin Jamila batare da ta nemi k'arin bayani ba. Da sauri tace.
Dubai me zaki je yi Dubai."?
"Zanyi rakiya ne."!! Jamila tayi magana tana wata 'yar siririyar dariya.
Kan Hafsah yayi wata iriyar sarawa.
Tana son ta k'ara tambayar Jamila, _Wa zata raka haka."?_
Amma kuma bata son Jamilar taga kamar tana binciken ta ne. Don haka tayi shuru kawai.
Sai ta juyo Jamila na cewa. "Thank you, ki gaida mama, bari na d'aga wani kira.
"Okay thank you bye bye.
Hafsah tace...
📝
*HAJEEEYAH KHAREEMERH*
[17/03, 2:46 p.m.] UMAIMA BASHEER: ♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so (Guba ne)*
💔💔
*By*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Khareemerh)*
*Dedicated to unique in your love heart*
📄 *56*
_NAILA group 1 ina godia da Soyayyar ku... Espclly #ummita_😊😊
_Sayyada_ kema Inayinki. (NAILA group 2)
*Team Ukhasha
*Team Hafsah.
Inajin dad`in comment d'inku.💃🏼💃🏼💃🏼
*Ranar* da ta biyo baya, bai kirata ba sam tun daga safiya har wata wayewar garin.
Hafsah ta sanya kanta cikin tsarguwa. Amma kuma tanajin ba zata iya kiranshi ba.
___________________
Yau gaba d'aya busy yake, abubuwa sun mishi yawa, bayan dawowar shi daga office, yayanshi Dr. Sunusi yace ya same shi a gida, zasu tattauna.
Yana dawowa abinci kawai yaci, yayi wanka sannan yayiwa Hajiya sallama ya wuce.
Bayan hira da sukayi ta zumunci, Dr. Sunusi ya bujurowa da Ukhasha maganar da yasa ya kirashi.
"Ukhasha."!!
Ukhashatu ya amsa.
"Naam Yaya.!!
Dama wata _share_ ce zan maka talla ko zaka sa kud'inka kaima aciki..
Ukhashatu ya bada gaba d'ayan hankalinshi ga yayan nashi.
Dr. Sunusi ya cigaba da magana.
Wani d'an k'aramin company ne, na had`in guiwa mukeso mu bude ni da abokai na mu shidda, to kuma mun duba munga muna da buk'atar k'arin kud'i shine muke bukatar k'arin mutum d'aya.
Ukhasha ya gyara zama. Okey Yaya, kamar nawa ake buk'atar kowa ya saka."?
Ba wai bukata ake kowa sai yasaka daidai da na kowa ba. Zaka iya saka ko nawa kake dashi kawai, tunda za,a dinga raba ribar ne, daidai da yadda kudin mutum yake aciki.
Ukhashatu ya jinjina kai, Okey na gane Yaya, amma kamar nawa kake ganin ni zansa."?
Um..To." Inji Doctor. Sannan ya kalli ukhashatu.
Zaka iya saka 4million, ko da rabi ma.!!
Ukhasha yayi murmushin gefen kunci.
"Doctor, ansan nauyin aljihun fah.
Na sani.!
Inji Dr Sunusi yana murmushi shima.
"Ka saka 4million d`in dai."
Ukhasha yayi ajiyar zuciya a hankali, Dr. ya kalle shi da alamar tambaya. Ukhasha yace, "da inada wani lissafi da nakeyi ne."
Dr. Sunusi yayi murmushi, wanne tunani kuma."?
Ukhashatu ya sunkuyar da kai, yana shiga matsa k'afar shi, dama a kasa suke dukan su a zaune.
Dariya ya bawa, Dr. ma sai da ya gama dariyar sannan yayi magana.
Aure zakayi."? Bai barshi ya bada amsa ba ya d'ora.
Ka gaji da zaman gwaurontakar kenan...
Ukhasha yayi wani dan murmushi. "A,a fa Yaya."
To mene tunanin naka idan ba shi ba.
Yayi shuru, don bashi da amsa.
Hmm, yanzu dai ka nemo, 4m. kawai kaidai, zamuji dad`in abin fa idan ya kankama.
Okey in sha Allah."
Inji Ukhasha.
Zuwa Yaushe za,a karbi kud'in.
Nan da wata d'aya muke son mu fara shirya komai, amma muna yin meeting akan yadda abin zai kankama, gobe ma muna dashi, da daddare sai ka shigo muje.!!
Okey, in sha Allah.
Am naji Hajiya na cewa zatayi retire koh."?
"Eh haka tace, nan da wata d'aya ne."
Gud, ai gwara ta huta.!! Inji Dr. Sannan ya shiga wata maganar.
"Yaushe ma Abba yace zamuje gidan gonar nan don na manta.
Nan da sati d'aya ne." Cewar ukhasha.
Ai abin ne da yawa abubuwan sunyi yawa.
"Ana kokari ai."
Inji ukhashatu, Naji yace yana so ne, ya k'ara fad'ad'a wajen."
"Yayi kyau hakan ai, kaga ya dad'e bai je duba gurin ba fah.
Ukhasha ya jinjina kai, "Eh amma
"yana tura ni akai-akai ai, kuma naga babu laifi ma,aikatan suna kula da wajen yadda ya dace.!!
So ko zamu bude namu d'an k'aramine haka koda iya kaji ne, da kifi sai mu saka. Cewar Doctor yana dariya.
Ukhasha ya taya shi dariyar shima. "Hmm Doctor kenan.!!
Cikin nutsuwa yake jawo hakalin Ukhashatu kan abin da cewa, "Ina da wani tunanine, kuma dana bujurowa da Abba shi naga ya nuna jin dad'inshi har ya sanyawa abin albarka ma."
Ukhashatu ya kalle shi irin kallon neman k'arin bayani.
Cikin nutsuwa doctor yace, inaso mu bude wani kasuwanci dukanmu har matan ma, kai hatta mahseem sai ansa mata nata kason aciki.!
Ukhashatu ya waro ido.
Doctor ya jinjina kai, Yes, wannan zai kara kawo had`inkai, sannan kuma gaba ake ji ba baya ba."
Ukhashatu ya jinjina kai. "Hakane..abun yayi kyau.
Baka ga yadda Abba ya d`auki abin ba, daga yi mishi zancen ni na zaci ma yayi maka zancen.
Ukhashatu ya girgiza kai.
"A,a" Amma waye zai sawa su yaran tunda kace har Mahseem."?
Doctor yace yana dariya. "Abba ne.!! Kuma ai ba wani abu mai yawa zai maka musu ba, tunda kasuwanci ne irin na kayan amfani irin na kasuwa da kadan zamu fara, kuma za,a saka equal ne babu mace babu namiji kowa _one hundred thousand._ Yayi kyau Yaya Allah ya bar zumunci ya taimake mu, Allah ya taimaki Abban."
"Amiin ya Allah. Inji Dr. Sannan ya kuma kallon Ukhashatu.
A ina ka sami yarinyar ne."?
Ukhasha yayi saurin bude baki, "Am ai bamu gama daidaitawa da ita bama."
"Hmm, koh.."? Baka sanarwa da su Abba ba kenan."?
Ukhashatu ya daga kai alamar, "Eh."
Cikin nutsuwa doctor yake nusar dashi. "Kayi kokari dai, kayi abinda zai farantawa su Abba."
Ukhashatu ya gyada kai, In sha Allah, bamu dad'e da sanin juna bane shiyasa."
Okey, nagane Allah ya tabbatar da alkhairi.!
"Amin Yaya. Sannan ya duba agogon hannunshi, "Bari na tafi dare yayi yaya.
Okey, ba zaka shiga cikin ku gaisa ba."?
To bari na shiga naga 'yar rigima.
Sukayi dariya sannan suka mik'e a tare.
Suka shiga da sallama. Fadeel na jin muryar auncle ya taho da gudu yana murna "uncle!! uncle!! Ukhashatu ya d`auke shi, ya daga shi sama suna dariya.
"Kaii Kaii Kaii." kai fa ka girma yanzu, kayi nauyi "Ya Fadeel zan daina d'aukarka kai da "Ãrif. Na'eemah kawai zan dinga d'auka.!! Ukhashatu ya fad'a sanda yake sauke shi.
Suka zauna a Kujera yaron ya zauna kusa da shi."
"Uncle su sunyi bacci."
"Kai meyasa bakayi bacci ba toh."?
"Assignment nake yi, nima yanzu zanyi bacci, aunty dinmu tace ina da k'ok'ari!!
Allah, ai na sani dama _my boy is a gifted.!!_
Suka tafa shida Fadeel d`in suna dariya.
"Au uncle ina yini."?
Inji Fadeel harda d'an rank'wafawa. Doctor da Ukhashatu suka sheke da dariya, doctor yace, "Au sai yanzu aka tuna da gaisuwar."?
"Mantawa nayi Abba.!! Inji Fadeel.
To Lafiya lau, Fadeel d`ina kana lafiya."? Inji ukhashatu.
Lafiya lau uncle.
Suna cikin haka, maman yaran ta fito daga d'aki.
Au Engr. Sai yanzu kenan ka shigo koh."?
Afwan auntie ina yini."?
Lafiya lau, yasu Hajiya da Abba."?
Lafiya lau suke."?
Ta dan sami guri ta zauna.
"To yasu Fadwa M aryam, kwana biyu basu lek'oni ba."
"Suna nan kalau, bari na wuce ma kada dare yayi min."
Daga shigowa kuma."? Inji aunty Jamila.
"Dare ne zaiyi min shiyasa"
Eh, kuma kazo kawar taka na bacci koh."?
Eh fa, ai gobe ma zan dawo in sha Allah."
"Tom sai kazo d`in.
Ya mik'e Fadeel ma ya mik'e ya rik'e hannunshi.
Ya kalli, yayanshi. Sai da safe yaya."
Tom ka gaida gida ukhashatu sai goben, ka gaida su Abba da hajiya.
Zasuji, yace, sannan ya juya ga aunty Jamila, Tom aunty sai da safe, Allah ya tashe mu lafiya, agaida Hajiya da mama."
"Zasuji sosai, yace.
Ta kamo hannun Fadeel, oh baby zo kaje ka kwanta kaji.
Ya noke k'afada "A,a ni uncle zan bi."
Ukhashatu yayi dariya, Aa aboki ka bari gobe zan dawo sai muje gidan Abba amma yanzu kaga dare yayi koh."
Ya daga kai, a sanyaye da alama bai so ba."
Ukhashatu ya sake shi, sannan ya laluba aljihun shi babu, ya zaro 500. "Ungo Aboki."
Ya damk'awa yaron.
Asai chocolate yau na manta ban taho dashi ba.
Yaron yasa hannu biyu ya k'arba yana murna.
Thank you auncle, ka gaida gida.
Aunty Jamila tace, Allah dama ukhasha shiyasa yaran nan suke makale maka, ka daina basu kudi don Allah idan babu alawa a hak'ura.
Yayi murmushi kawai, yana dagawa yaron hannu "Bye bye.
Shima yaron ya daga mishi "Bye bye uncle gud night.!!
Ukhasha ya fita yana murmushi.
__________________
Daya koma gida, 11 na dare ta wuce, kafin yayi wasu al,adu da ya saba kafin kwanciya bacci har sha biyu tayi. Dole ya hakura da kiranta da yayi niyya. Gashi ya gaji likis, yana kwanciya babu jimawa bacci ya d`auke shi mai cike da mafarkanta..
_________________
Tana ta sak'awa da kwancewa akan neman dalilin rashin jin shi gaba-d`aya yau, amma tunanin ta yafi fad'awa kan cewa ya gaji ne, ya yanke hukunci. Hankalinta ya dugunzuma, meyasa bata mishi koda SMS bane bayan wayar da sukayi. Ta shiga yiwa kanta fad'a, tabbatas da gaskiya r shi, su fa ba yara bane 'yan secondary da zata dinga yi mishi abubuwa irin haka.
Dole ne, ta sami hanyoyin fahimtar dashi abinda take ji game dashi.
Ta lalubi wayarta, akan wayar taga dare yayi har k'arfe 11:30pm, taji kamar ta mishi text da _I love you.!_ har ta shiga wajen yin typing message, sai kuma taja dan siririn tsaki, ta fasa.