Sashe 74
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A sit room suka yada zango, bayan dukkansu sun zauna a gurin da shi abba yaiwa kanshi mazauni, da kuma gurin da yayi wa ukhashatu nuni daya zauna tun f
Kafin shi Abban ya zauna, amma sai da ukhashatu ya bari Abba ya zauna sannan ya zauna a k'asan kujerar da aka mishi nuni da ita.
Abba yaji dad`in wannan ladabin. Ya fuskace shi kuma da murmushi a fuskar shi.
"Ya mutanen gidan suna lafiya."
Ukhashatu yayi murmushi, yana dan sunkwi da kai.
Lafiya lau Abba.
Abba ya d'anyi gyaran murya.
"Sai dai ban shaida fuskar ba daga ina ake."
Ukhashatu ya k'ara k'asa da kanshi.
Nassarawa."
"To Masha Allahu." yana murmushi yace, "Za,a fad'a mana sunan mai Gidan ko nafi ganewa."
Ukhashatu yayi murmushi shima, Eh, "Alhaji Abubakar Khady."
Abba ya fad'ad'a fara,arshi.
To Masha Allah, Khady dai da na sani mai sharia na majestry court"?
Ukhashatu ya jinjina kai cikin ladabi.
Abba cikin fara,a Alhamdulillah. "Ai Khady na mu ne, Allah ya k'ara mishi lafiya."
"Amin Abba."
Cewar ukhasha.
Sannan Abba ya d`an shaki numfashi kafin yace, "To wajen Basheer aka zo ne."?
( _baya son ya mishi tambayar gurin wa yazo cikin yayanshi mata kai tsaye._)
Ukhashatu ya sosa k'eya yana gyara zama cikin jin nauyin abba yace, "Eh Abba mun gaisa dashi kuma nazo wajen mun gaisa da Hafsah ma."
Abba jira kawai yake yaji alak'ar Basheer da Hafsah.
Cikin son mishi wayo irin nasu na manya yace, "Wajen aikin ku d'aya kenan."?
Ukhashatu ya girgiza kai, fata yake kawai Abba ya fahimta basai ya fito b'aro-b'aro ba.
"Am um dama ina zuwa ne muna gaisawa."
Abba yayi murmushi, cikin matsanancin farinciki, "Alhamdulillah ya furta a fili."
Yana yiwa Allah godiya, da ya bawa Hafsah miji irin wanda yake mata fata. _(Dan gidan manyan mutane ba girma irin na naira ba, sai dai duka kuma Allah yayi an had'a kudi da sanin yakamata ga kyakykyawan asali)_
Ukhashatu yana iya karantar irin farin cikin daya bayyana kan fuskar Abba.
"Masha Allah, Allah yayi albarka."
Kai tsaye yace, Za,a iya yiwa manyan magana sai a zo agaisa koh."?
ukhashatu ya gane me Abba yake nufi, cikin farin ciki, shima ya ke zuba godiya.
"Nagode Abba Allah ya saka da alkhairi."
"Amin Amin."
Sai a bani number shi Abban naka koh."?
Abba ya ciro wayar shi ya mik'o.
Ukhashatu ya karb'a da hannu biyu ya rubuta number, sannan ya mik'awa Abba.
Abba yayi saving, sannan zana tashi number akan wayarshi, ya k'ara mik'awa ukhashatu.
"To gashi, koh sai a d`auki tawa saboda a sanar idan an shirya zuwan."
Ukhashatu ya karba yasaka, a wayarshi.
Sannan ya mik'awa Abba wayar.
Yana fad`in "Angode Abba."
Abba yayi murmushi sannan ya mik'a mishi hannu sukayi musabiha, yana fad`in agaida mutanen gidan, naga magriba ta k'arato.
Ukhashatu ya mik'a bayan sun saki hannun juna, "Na Barka lafiya Abba."
Ya fita cikin matsanancin farin ciki, ji yake kamar ango ne shi.
Godiya yake ga Allah daya sauk'ak'a mishi komai. Ya sani ba dabarar shi bace Allah ne ya saukaka mishi komai yadda zai sanya mahaufanshi cikin farin ciki.
*______________*
A wani masallaci ya tsaya a hanya yayi sallar magriba inda babu wani jira ya, k'ara tarar napep Kai tsaye ya wuce gidan abokin shi, da k'yar ya lallabashi kan ya taso ya raka shi gadon k'aya gidan Baffa..Babu irin mitar da Mubarak bai mishi ba a mota. _kai ka cika zumudi daga haka sai ayi haka, wa yaga farin shiga."? Banda na matsu kayi aure nima da babu abinda zai hana ni zamana a gada. Kawai ka taso mutane suna hutawarsu._
Shidai ukhashatu kus yayi yana jinshi don yana cikin farin ciki, baya son ya tanka mishi ya ce bazai raka shi ba.
Yanayinsu da Baffa ya gani ya tabbatar mishi da akwai magana, kuma shima ya sakar musu fuska kamar yadda ya gansu cikin farin ciki.
Bayan gaisuwarsu kamar ko yaushe, _ta musabiha._
Baffa cikin fara,a yake tambaya.
Ya akayi ne, ya Abban naku."?
"Yana lafiya lau Baffa."
"To Masha Allah." Suka k'ara yin shuru.
Baffa ya k'ara tambaya.
Komai kalau dai koh."?
"Lafiya lau Abba suka fad'a cikin ladabi, Mubarak ya gyara zama, ganin dare ya farayi ya fara magana.
"Baffa ayi mana afwa munzo da daddare."
Baffa ya gyada kai, yana murmushi, "Ai ku ba bak'i bane, babu komai, ai shi ya sha amsa kiran dare ma a gidan nan." Ya kalli Ukhashatu yana k'arashe zancen.
Ukhashatu shidai kanshi na k'asa.
Sannan baffa ya juya ga Mubarak yana, tambaya. "Me ya faru ne."?
Mubarak ya gyaran zama ya fara bayani.
"Dama Baffa, akwai gurin da Ukhasha yake zuwa amma bai jima ba, to yau d'innan sai mahaifin yarinyar yace a turo magabata."
Tunda ya fara magana Baffa najinshi yana gyada kai, sai da yakai k'arshe sannan suka ga wata fara,a da basu taba gani ba musamman ukhashatu a fuskar Baffa.
Masha Allah Alhamdulillah Allah ya tabbatar da alkhairi, ai wannan abu ne da muke nema."
Sannan ya juya ga ukhasha da kunya ta cika yace, "Har kwananka nawa da fara zuwa zaka ce, baku dad'e ba."
Kai a k'asa yace, wata d'aya zuwa biyu, amma zuwanta na biyu kenan gurinta."
"Baffa ya ca fe, ahaf ai tunda kun daidaita kuma har tana saurarar ka ai zance ya k'are."
Ya juya ga Mubarak, "Abban nashi ya sani."?
Mubarak ya girgiza kai.
"A,a Baffa ai yanzu ne akayi maganar."
"OK tom babu komai."
"Sun bada number ne da zaayi magana."?
Mubarak ya kalli Ukhashatu, shi kuma da sauri ya lalubo wayarshi a aljihu, ya danno number _Abban Hafsah_ ya mik'awa Mubarak.
Cikin ladabi Mubarak da hannu biyu ya mik'awa Baffa.
Baffa ya amsa yana murmushi yana cewa, "Ai kuwa gaka anyi dabara da aka bada number."
"Sai ayi magana yadda ya dace."
A wanne unguwa suke. Mubarak ya amsa, "Sallari."
"To ya sunan shi mahaifin yarinyar da yarinyar."?
"Alhaji Habeeb Hamid."!!
"Ita kuma Hafsah."
Duk Mubarak ne ya bada amsa.
"Masha Allah, "Allah ya tabbatar da alkhairi.
"Amin." Inji Mubarak.
"Zamuyi magana da Yayan." Baffa ya fad'a.
Ukhashatu ya d'an tab'a mubarak alamun ya tashi su tafi.
Mubarak ya mik'e shima ya mik'e, cikin ladabi suka mishi sallama.
"Baffa zamu tafi kada dare yayi." Inji su.
Tom Allah yayi albarka tunda har kun mik'e ku gaida gida, an gode kaji Mubarak."?
Suka fita, kowa fuskar shi da murmushi.
A waje mubarak yake ta tsokanar Ukhashatu, "Aikin banza ka wani zama silent a ciki don gulma koh."
Ya gyada kai Eh mana, ni wuce ka kaini gida malam.
Cab bazai yuwu ba wallahi, sai dai na ajyeka a titi, kawai na baro iyali na salon ka hura min wuta kai kana kokarin gida naka gidan."?
Dukansu sukayi dariya, Ukhasha ya zagayo ta daya barin yana cewa "Eh naji saukeni a titin."
Suna zuwa titin kuwa yayi parking. Ukhashatu ya mishi godiya ya fice ya tari Napep yayi gida.
_______________
D'akin Hajiyarshi ya nufa daga shigowar shi gidan, fara,ar shi ta musamman a lokacin, yana nufo d'akin, Mahseem ta nushi da gudu ta d'ane shi, "Yaaya!!
Ya daga ta da k'yar.
Kin girma fa "Mahseem na daina daukar ki daga yau."
Ya sakko ta ya rik'e hannunta suka k'arasa cikin gidan.
Yayi sallama ya zauna.
Hajiya ta kalleshi.
"Ina kaje ne haka tun yamma."?
Ya sunkuyar da kai, "naje gidan baffa hajiya."
"Acan ka dad'e haka."? Hajiya ta k'ara tambaya.
"A,a naje gidan abokinah..."
Yana cikin fad'a Fadwa ta ca fe, tana dariya "Hajiya zance yaje fah."
Ya aika mata da wata hararar data sa ta saurin to she bakinta da hannu.
Ya jinjina kai sannan ya mik'e, hajiya ta bishi da kallo, to ya Hajiyar ka baro su lafiya."?
"Lafiya lau Hajiya."
Mahseem ta biyo shi ta rik'e hannunshi suka nufi d'akin shi.
"Yaya tasbahar da kace zaka siyo min."
Yayi murmushi, Eh na siyo miki "Mahseem har da chocolates ma."
"Yawwa brother nagode."
Ya bude d'akin suka shiga, mahseem na mishi tambayar da ta saka shi juyo wa.
"Yaya wai da gaske zance kaje."
Ya tsaya ya kalleta har tasha jinin jikinta kafin yayi murmushi.
Museem ki min addu,a kinji Allah ya zaba min abinda yafi alkhairi.
Tayi murmushi, "Tom Yaya inayi."
Ya bude drawer ya dakko mata ledar, ungo kije ki kwanta, kice maryam ko Fadwa su kawo min abinci kinji."
"Tom Yaya sai da safe." "Yawwa Mahseem.
Yace da ita.
Sai da yazo kwanciya bacci ya tuno yadda suka rabu da Mutuniyar tashi, nan ya dinga dariya kamar bazai daina ba, Yanajin kewarta a zuciyar shi daga k'arshe, ya lalubi number ta amma tak`i d'auka.
Yayi murmushi a fili yace, "Hmm yarinya na kusa mallakar ki na huta.!!
_____________________________
Khady yayi mamakin jin batun da, k'aninshi yazo mishi dashi, _wai ukhashatu da neman aure.!!_ Bayan cikin kwanakin nan ma ya mishi maganar amma ya nuna ba wani shiri da yake.
Badon bikin maryam sati biyu kawai sukayi saura ba, da babu abinda zai hana yace a had'e.
Ya nuna jin dad`in shi ga kanin nashi, sannan suka shawarta yadda abubuwan zasu kankama, sun tsara zasuyi bincike kafin suyi magana da mahaifin yarinyar.
Sukayi sallama kowa cikin farin ciki da mamakin Ukhashatu.
___________________________
Maman su Hafsah ta lura da kalar farincikin da Abban Hafsah ya shigo dashi d`auke a fuskar shi, itama sai ta tare shi da hakan.
Sai da ya nutsu yake mata jawabi yadda zata fahimta.
Amina, naga wani yaro yazo wajen Hafsanki, kuma na yaba dashi har na nemi daya turo iyayenshi."
Mama ta waro ido, "Abba da wuri haka."?
Ya gyd'a kai to me za,a jira tunda Allah ya kawo."?
Kuma yaron dan gidan sanannun mutane ne, amma duk da haka zanyi d'an takaitaccen bincike, kedai ki taya ta da Addu,a Allah ya mata zabin alkhairi.
"Amin."
Inji mama, taji dad`in hakan amma kuma tana tsoron gaggawar da akayi kan al,amarin."
"Kada Ki sanar mata har sai sunzo, sannan zan sanar mata da kaina."
Mama ta gyada kai alamar "Toh."
Sanda Basheer ya shigo ya shiga d'akin Abban don tsaigun ta mishi bak'on Hafsah.
Shima Abba a k'age yake yana son jin zancen daga bakin Bashir d`in tunda bakon ya tabbatar mishi sun san juna shida Basheer.
Akwai magana ne malam Bashari."?
Basheer ya sosa kai sannan yace,
Kafin shi Abban ya zauna, amma sai da ukhashatu ya bari Abba ya zauna sannan ya zauna a k'asan kujerar da aka mishi nuni da ita.
Abba yaji dad`in wannan ladabin. Ya fuskace shi kuma da murmushi a fuskar shi.
"Ya mutanen gidan suna lafiya."
Ukhashatu yayi murmushi, yana dan sunkwi da kai.
Lafiya lau Abba.
Abba ya d'anyi gyaran murya.
"Sai dai ban shaida fuskar ba daga ina ake."
Ukhashatu ya k'ara k'asa da kanshi.
Nassarawa."
"To Masha Allahu." yana murmushi yace, "Za,a fad'a mana sunan mai Gidan ko nafi ganewa."
Ukhashatu yayi murmushi shima, Eh, "Alhaji Abubakar Khady."
Abba ya fad'ad'a fara,arshi.
To Masha Allah, Khady dai da na sani mai sharia na majestry court"?
Ukhashatu ya jinjina kai cikin ladabi.
Abba cikin fara,a Alhamdulillah. "Ai Khady na mu ne, Allah ya k'ara mishi lafiya."
"Amin Abba."
Cewar ukhasha.
Sannan Abba ya d`an shaki numfashi kafin yace, "To wajen Basheer aka zo ne."?
( _baya son ya mishi tambayar gurin wa yazo cikin yayanshi mata kai tsaye._)
Ukhashatu ya sosa k'eya yana gyara zama cikin jin nauyin abba yace, "Eh Abba mun gaisa dashi kuma nazo wajen mun gaisa da Hafsah ma."
Abba jira kawai yake yaji alak'ar Basheer da Hafsah.
Cikin son mishi wayo irin nasu na manya yace, "Wajen aikin ku d'aya kenan."?
Ukhashatu ya girgiza kai, fata yake kawai Abba ya fahimta basai ya fito b'aro-b'aro ba.
"Am um dama ina zuwa ne muna gaisawa."
Abba yayi murmushi, cikin matsanancin farinciki, "Alhamdulillah ya furta a fili."
Yana yiwa Allah godiya, da ya bawa Hafsah miji irin wanda yake mata fata. _(Dan gidan manyan mutane ba girma irin na naira ba, sai dai duka kuma Allah yayi an had'a kudi da sanin yakamata ga kyakykyawan asali)_
Ukhashatu yana iya karantar irin farin cikin daya bayyana kan fuskar Abba.
"Masha Allah, Allah yayi albarka."
Kai tsaye yace, Za,a iya yiwa manyan magana sai a zo agaisa koh."?
ukhashatu ya gane me Abba yake nufi, cikin farin ciki, shima ya ke zuba godiya.
"Nagode Abba Allah ya saka da alkhairi."
"Amin Amin."
Sai a bani number shi Abban naka koh."?
Abba ya ciro wayar shi ya mik'o.
Ukhashatu ya karb'a da hannu biyu ya rubuta number, sannan ya mik'awa Abba.
Abba yayi saving, sannan zana tashi number akan wayarshi, ya k'ara mik'awa ukhashatu.
"To gashi, koh sai a d`auki tawa saboda a sanar idan an shirya zuwan."
Ukhashatu ya karba yasaka, a wayarshi.
Sannan ya mik'awa Abba wayar.
Yana fad`in "Angode Abba."
Abba yayi murmushi sannan ya mik'a mishi hannu sukayi musabiha, yana fad`in agaida mutanen gidan, naga magriba ta k'arato.
Ukhashatu ya mik'a bayan sun saki hannun juna, "Na Barka lafiya Abba."
Ya fita cikin matsanancin farin ciki, ji yake kamar ango ne shi.
Godiya yake ga Allah daya sauk'ak'a mishi komai. Ya sani ba dabarar shi bace Allah ne ya saukaka mishi komai yadda zai sanya mahaufanshi cikin farin ciki.
*______________*
A wani masallaci ya tsaya a hanya yayi sallar magriba inda babu wani jira ya, k'ara tarar napep Kai tsaye ya wuce gidan abokin shi, da k'yar ya lallabashi kan ya taso ya raka shi gadon k'aya gidan Baffa..Babu irin mitar da Mubarak bai mishi ba a mota. _kai ka cika zumudi daga haka sai ayi haka, wa yaga farin shiga."? Banda na matsu kayi aure nima da babu abinda zai hana ni zamana a gada. Kawai ka taso mutane suna hutawarsu._
Shidai ukhashatu kus yayi yana jinshi don yana cikin farin ciki, baya son ya tanka mishi ya ce bazai raka shi ba.
Yanayinsu da Baffa ya gani ya tabbatar mishi da akwai magana, kuma shima ya sakar musu fuska kamar yadda ya gansu cikin farin ciki.
Bayan gaisuwarsu kamar ko yaushe, _ta musabiha._
Baffa cikin fara,a yake tambaya.
Ya akayi ne, ya Abban naku."?
"Yana lafiya lau Baffa."
"To Masha Allah." Suka k'ara yin shuru.
Baffa ya k'ara tambaya.
Komai kalau dai koh."?
"Lafiya lau Abba suka fad'a cikin ladabi, Mubarak ya gyara zama, ganin dare ya farayi ya fara magana.
"Baffa ayi mana afwa munzo da daddare."
Baffa ya gyada kai, yana murmushi, "Ai ku ba bak'i bane, babu komai, ai shi ya sha amsa kiran dare ma a gidan nan." Ya kalli Ukhashatu yana k'arashe zancen.
Ukhashatu shidai kanshi na k'asa.
Sannan baffa ya juya ga Mubarak yana, tambaya. "Me ya faru ne."?
Mubarak ya gyaran zama ya fara bayani.
"Dama Baffa, akwai gurin da Ukhasha yake zuwa amma bai jima ba, to yau d'innan sai mahaifin yarinyar yace a turo magabata."
Tunda ya fara magana Baffa najinshi yana gyada kai, sai da yakai k'arshe sannan suka ga wata fara,a da basu taba gani ba musamman ukhashatu a fuskar Baffa.
Masha Allah Alhamdulillah Allah ya tabbatar da alkhairi, ai wannan abu ne da muke nema."
Sannan ya juya ga ukhasha da kunya ta cika yace, "Har kwananka nawa da fara zuwa zaka ce, baku dad'e ba."
Kai a k'asa yace, wata d'aya zuwa biyu, amma zuwanta na biyu kenan gurinta."
"Baffa ya ca fe, ahaf ai tunda kun daidaita kuma har tana saurarar ka ai zance ya k'are."
Ya juya ga Mubarak, "Abban nashi ya sani."?
Mubarak ya girgiza kai.
"A,a Baffa ai yanzu ne akayi maganar."
"OK tom babu komai."
"Sun bada number ne da zaayi magana."?
Mubarak ya kalli Ukhashatu, shi kuma da sauri ya lalubo wayarshi a aljihu, ya danno number _Abban Hafsah_ ya mik'awa Mubarak.
Cikin ladabi Mubarak da hannu biyu ya mik'awa Baffa.
Baffa ya amsa yana murmushi yana cewa, "Ai kuwa gaka anyi dabara da aka bada number."
"Sai ayi magana yadda ya dace."
A wanne unguwa suke. Mubarak ya amsa, "Sallari."
"To ya sunan shi mahaifin yarinyar da yarinyar."?
"Alhaji Habeeb Hamid."!!
"Ita kuma Hafsah."
Duk Mubarak ne ya bada amsa.
"Masha Allah, "Allah ya tabbatar da alkhairi.
"Amin." Inji Mubarak.
"Zamuyi magana da Yayan." Baffa ya fad'a.
Ukhashatu ya d'an tab'a mubarak alamun ya tashi su tafi.
Mubarak ya mik'e shima ya mik'e, cikin ladabi suka mishi sallama.
"Baffa zamu tafi kada dare yayi." Inji su.
Tom Allah yayi albarka tunda har kun mik'e ku gaida gida, an gode kaji Mubarak."?
Suka fita, kowa fuskar shi da murmushi.
A waje mubarak yake ta tsokanar Ukhashatu, "Aikin banza ka wani zama silent a ciki don gulma koh."
Ya gyada kai Eh mana, ni wuce ka kaini gida malam.
Cab bazai yuwu ba wallahi, sai dai na ajyeka a titi, kawai na baro iyali na salon ka hura min wuta kai kana kokarin gida naka gidan."?
Dukansu sukayi dariya, Ukhasha ya zagayo ta daya barin yana cewa "Eh naji saukeni a titin."
Suna zuwa titin kuwa yayi parking. Ukhashatu ya mishi godiya ya fice ya tari Napep yayi gida.
_______________
D'akin Hajiyarshi ya nufa daga shigowar shi gidan, fara,ar shi ta musamman a lokacin, yana nufo d'akin, Mahseem ta nushi da gudu ta d'ane shi, "Yaaya!!
Ya daga ta da k'yar.
Kin girma fa "Mahseem na daina daukar ki daga yau."
Ya sakko ta ya rik'e hannunta suka k'arasa cikin gidan.
Yayi sallama ya zauna.
Hajiya ta kalleshi.
"Ina kaje ne haka tun yamma."?
Ya sunkuyar da kai, "naje gidan baffa hajiya."
"Acan ka dad'e haka."? Hajiya ta k'ara tambaya.
"A,a naje gidan abokinah..."
Yana cikin fad'a Fadwa ta ca fe, tana dariya "Hajiya zance yaje fah."
Ya aika mata da wata hararar data sa ta saurin to she bakinta da hannu.
Ya jinjina kai sannan ya mik'e, hajiya ta bishi da kallo, to ya Hajiyar ka baro su lafiya."?
"Lafiya lau Hajiya."
Mahseem ta biyo shi ta rik'e hannunshi suka nufi d'akin shi.
"Yaya tasbahar da kace zaka siyo min."
Yayi murmushi, Eh na siyo miki "Mahseem har da chocolates ma."
"Yawwa brother nagode."
Ya bude d'akin suka shiga, mahseem na mishi tambayar da ta saka shi juyo wa.
"Yaya wai da gaske zance kaje."
Ya tsaya ya kalleta har tasha jinin jikinta kafin yayi murmushi.
Museem ki min addu,a kinji Allah ya zaba min abinda yafi alkhairi.
Tayi murmushi, "Tom Yaya inayi."
Ya bude drawer ya dakko mata ledar, ungo kije ki kwanta, kice maryam ko Fadwa su kawo min abinci kinji."
"Tom Yaya sai da safe." "Yawwa Mahseem.
Yace da ita.
Sai da yazo kwanciya bacci ya tuno yadda suka rabu da Mutuniyar tashi, nan ya dinga dariya kamar bazai daina ba, Yanajin kewarta a zuciyar shi daga k'arshe, ya lalubi number ta amma tak`i d'auka.
Yayi murmushi a fili yace, "Hmm yarinya na kusa mallakar ki na huta.!!
_____________________________
Khady yayi mamakin jin batun da, k'aninshi yazo mishi dashi, _wai ukhashatu da neman aure.!!_ Bayan cikin kwanakin nan ma ya mishi maganar amma ya nuna ba wani shiri da yake.
Badon bikin maryam sati biyu kawai sukayi saura ba, da babu abinda zai hana yace a had'e.
Ya nuna jin dad`in shi ga kanin nashi, sannan suka shawarta yadda abubuwan zasu kankama, sun tsara zasuyi bincike kafin suyi magana da mahaifin yarinyar.
Sukayi sallama kowa cikin farin ciki da mamakin Ukhashatu.
___________________________
Maman su Hafsah ta lura da kalar farincikin da Abban Hafsah ya shigo dashi d`auke a fuskar shi, itama sai ta tare shi da hakan.
Sai da ya nutsu yake mata jawabi yadda zata fahimta.
Amina, naga wani yaro yazo wajen Hafsanki, kuma na yaba dashi har na nemi daya turo iyayenshi."
Mama ta waro ido, "Abba da wuri haka."?
Ya gyd'a kai to me za,a jira tunda Allah ya kawo."?
Kuma yaron dan gidan sanannun mutane ne, amma duk da haka zanyi d'an takaitaccen bincike, kedai ki taya ta da Addu,a Allah ya mata zabin alkhairi.
"Amin."
Inji mama, taji dad`in hakan amma kuma tana tsoron gaggawar da akayi kan al,amarin."
"Kada Ki sanar mata har sai sunzo, sannan zan sanar mata da kaina."
Mama ta gyada kai alamar "Toh."
Sanda Basheer ya shigo ya shiga d'akin Abban don tsaigun ta mishi bak'on Hafsah.
Shima Abba a k'age yake yana son jin zancen daga bakin Bashir d`in tunda bakon ya tabbatar mishi sun san juna shida Basheer.
Akwai magana ne malam Bashari."?
Basheer ya sosa kai sannan yace,