← Book details Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 88

Sashe 26

Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

'Sai da suka sauke kowa sannan yusuf ya kai basman gidan mamanta, wai sai ta buk'aci ya shigo su gaisa, da yaki' ya nuna mata yana sauri ne, amma ko me ya tuna oho sai ya wuce suka shiga'
'Wata hamshakiyar mace ya gani taci ado sosai ta hakimce akan kujerar falon, suna shiga Basma ta fad'a jikin ta, "Mummy wallahi duk na gaji fa!"
'Matar tayi murmushi "oh sorry baby ai kece kun ja abin da yawa. Ta maido da kallonta kan yusuf dake zaune shima yana kallonsu yana murmushi, "mum good evening" how are you? "Am Fine, how's family" they're fine. Gud'
Ahaka sukayi gaisuwar tasu, sannan ya mik'e tare da cewa "Gud night"
'Ta sakar mishi fuska sosai tana cewa "Ok bye bye ka gaida Mum"..
'Ita dai fa sun gaisa ne kawai, amma bata san alak'ar su da Basma ba, amma taji aranta yayi mata, kuma duk da bata barin 'yarta kula samari to tabbas zata iya barinta dashi domin daga ganinshi d'an manya ne'..
'Basma ta mik'e ta bishi sukayi sallama, wannan karon har da rik'e hannunshi su gaisa, ya tsaya shiru hannunshi cikin nata yana nazarinta sosai, tuni wani abu ya tsarga mishi cikin zuciya, ya zare hannunshi tare da yi mata murmushi, ya d'aga mata hannu alamar bye-bye ta tsaya har ya shiga mota tana kallonshi, ta saki ajiyar zuciya a hankali tana fatan Allah yasa sak'onnin data aika mishi ayau sun isa, kuma zasuyi tasiri yadda take so...
😇Muje zuwa dai..👍🏻👍🏻
*Hajeeyah Kareemerh*🍒
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔

Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to: Unique In Love Heart Members*

📄 *29*

*Lokacin* da Yusuf ya bar Hafsah kuwa tunda ta shiga gida jikin ta yayi sanyi, kawai sai taji tana buk'atar kad'aici.
'So take kawai ta keb'e tayi kuka, amma tana shiga gida bayan ta bawa mama sak'on ta juya da nufin wucewa d'aki, Maman ta kirawota, hakan yasa tayi saurin saita yanayinta ta dawo ta zauna, Maman ta kalleta cikin ido, sannan tace, "Ki je ki d'ora mana abinci kinji." Babu yadda ta iya haka ta mik'e ta nufi kitchen d'in, gabanta sai fad'uwa yake haka kawai takejin zafin Yusuf, saboda kafewa da yayi sai yaje Birthday d'in.. Sai wajen ana kiran magriba ta kammala, sannan tayi sallah, lokacin kuma Abba ya dawo, hakan ya tilasta mata fitowa falo ta zauna don ta lura baya son ganinta cikin d'aki idan ba lokacin bacci ba.'
'A dining sukayi dinner d'in, sannan 'Abba yace ayi musu tatsuniya, yana murmushi yace "Mama ce yau zata fara yi musu."
_('Abbansu Hafsah yana da wani ra,ayi: 'Wato ba koyaushe yake barin su kalli TV ba')_
Chapter 26 · 0% Book details