Sashe 70
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ina sonki." taji yace mata, maganar da ta k'ara kashe mata jiki.
Ki shirya kinji, kada na saki kiyi late.. nagode, Allah ya tsare min ke."
Babu sauti amma ta motsa bakinta wajen cewa, "AMIIN."
Don taji dad`in kalaman shi.
Tanajin karar katse kiran shi amma bata motsa ba, ji take kamar ta sauke wani nauyi daga kanta, haka kawai ta yardarwa zuciyar ta, ukhashatu ba k'aramin sonta yake ba, daga jin muryar shi zaka tabbatar da haka.
A hankali ta motsa ta d`auki mai da niyyar shafawa, gaba-d`aya ji take kamar an kwashe mata duk wani _energy_ da ke jikin ta.
A sanyaye ta dinga yin komai, gefe kuma na zuciyarta tana mamakin kanta, da kuma tuhumar kanta kan kalmar da ta furta da sanyin safiyar nan.
Azuciyar ta take fata, _"Allah yasa takai Soyayyar ta inda zata sami kulawa, ba inda za,a cutar da ita ba."_
Bata sami nutsuwa ba, har sai da raunin da jiki da zuciyarta yayi ya kaita da fitar da wata 'yar kwalla, sai da ta goge a hankali, sannan taji ta sami k'wari.
Tun bakwai take shiri, amma saida nawa ta kaita har k'arfe takwas, hakan yasa mama biyota.
Ta ganta zaune ta gama saka kaya, tana d'aura d'ankwali.
Yaya, me kikeyi hakane, keda kika ce da wuri zaki fita kinga takwas har tayi fa.
Ita kanta ba zatace ga abinda ya tsaida ta d`in ba.
"Na gama mama."
"Kiyi sauri kizo kiyi break dai."
Ta gyada kai.
Gani nan mama."
Maman ta juya itama ta fita.
Ukhashatu, tsahon ranar yinin farin ciki yayi, jiyake babu wanda ya kaishi farin ciki a yau. Godiya yake kawai ga Allah don shi ya mallaka mishi ita. Zuciyar shi cike take fal da tsare tsaren yadda rayuwar su zata kasance shida ita.
Bai iya jurewa ba, har sai da kira wayarta da azahar amma Hafsah taki d'agawa, ji take bazata iya mishi magana a yau ba.
Yayi murmushi lokacin da kiran ya yanke.
Kawai sai ya zana mata _text messages_
_"Hmm, dole kik'i daga waya mana dama, kin rikita bawan Allah, kin barshi a rikice kuma.!!_
Text d`in dariya ya bata, ta dinga yinta, har abokiyar aikinta na tambayarta "meke faruwa."?
Sai kuma ta dinga jin kamar da ita yake, domin itace a rikice ai, tun safiyar yau."
Don ta kare kanta ta aika mishi da, _lots of work dear, let's phone to night.!!_
Sanda ya ida karantawa, sai da ya maimaita kalmar _Dear_ a fili.
Ya dinga murmushi shi kad'ai shima, yana fatan daren yayi da sauri.
Amma murnarshi ta koma ciki, daya tuna yana da meeting da daddaren..
📝
*HAJEEEYAH KHAREEMERH*
[17/03, 2:48 p.m.] UMAIMA BASHEER: ♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so (Guba ne)*
💔💔
*By*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Khareemerh)*
*Dedicated to unique in your love heart*
📄 *57*
____________________
Bai samu ya kuma kiranta ba a ranar, itama kuma sai taji tana da jiran kiranshi, amma bai kirata ba, haka ta hakura har zuwan lokacin baccinta.
Tana mamakin dalilin daya tare shi ga barin kiran nata.
Ranar data biyo baya, sukayi waya, dole ta saki jiki da shi, saboda salon shi, gareta. Duk wani abu da ukhasha zaiyi ya tabbatar mata da son da yake mata yayi shi, wani ta mayar mishi wani kuma ta bishi da murmushi ko tayi shuru, don yanzu ta gama fahimtar dawa take tare. _Wato shi mutum ne daya k'ware a ko ina, yana matuk'ar son yaga ya sakata farinciki kuma._
Daga k'arshe yake rok'onta akan ta barshi ya k'ara zuwa ya ganta.
Da take tambayar shi, yaushe yake so ce mata yayi.
Ko yaushe kika ce nazo zaki ganni."
Tayi dariya Kawai sannan tace, Aa dai mu bari sai k'arshen sati."
"Babu musu ya amince.
Allah ya kaimu lokacin."
Amiin tace mishi.
___________________
Shiri sosai Hafsah ta dinga yi ranar da ya kama zai zo d`in.
Har tunani ta shiga yi, me ya dace tayi mishi na tarbarshi."
Ta kasa tunana komai, k'arshe ta yanke shawarar bashi lemo da snacks kawai tunda suna da shi.
Shiri tayi alwashin yi sosai akan zuwan na shi. Ba su kara yin waya ba tun bayan wayar da sukayi, da rana.
Wani abu da ya da ya wargazawa Hafsah shiri, wanda badon zuwan Ukhasha ba babu abinda zatayi farinciki dashi kamar shi, amma sai zuciyarta ta kasu biyu gefe na jin dad`in hakan gefe kuma naga tunanin gudun samun matsala. Wato abin ba komai bane fa ce zuwan _Jamila_ a ranar.
Misalin k'arfe uku da rabi daidai na yamma, lokacin Hafsah na cikin toilet, don tayi alwashin shiryawa da wuri, ba zata b'ata mishi lokaci ba, sannan tayi alwashin zata nuna mishi soyayya daidai gwargwado yadda zai fahimci tana son shi itama.
Tana cikin band'akin taji sallama daga palourn mama kamar anyi bak'uwa. Bata damu ba take wankan ta a tsanake.
A falon kuma, mama ce zaune ita da mufida, tana mata tausa a k'afa, sukaji anyi sallama da wata iriyar muryar da ta sakasu juyawa duka, don basu gane wanene mai muryar ba.
Mama wata hamshak'iyar babbar mace ta gani, a cikin falonta, wacce ita a ganinta tafi mata kama da irin mata 'yan siyasa.
Mufida kuwa idonta ne yayi wani harr, sai da mai sallamar ta k'aras Shigowa sannan ta gane ta, don sun ganta Kwanaki ita da su yaya Hafsah.
Mama ce tace mata, "sannu da zuwa, zauna mana."
Ta tsuguna ta gaida maman kafin ta zauna a kujerar da aka bata.
Abun ya bawa mama mamaki matuk'a, kafin ta kai ga tambayarta wacece, ita taji tanacewa.
Mama, Hafsah na nan."?
Eh tana nan inji mama, tana k'ara kallon Jamila.
Sannan ta kalli mufida, "Jeki ki kira Hafsan."
Maman taga alamun kamar mufida tasan bak'uwar, amma babu damar ta tambaye ta, sannan da taji wajen Hafsah tazo, sai tafi alak'antata da abokan aikin Hafsah. Amma kuma taji kamar tasan muryar, amma ta manta a ina."?
Sanda mufida ta shigo d'akin hafsah na shirin fitowa daga toilet d`in, don haka ta d'an jirata ta fito.
"Yaya kinyi bak'uwa.
Hafsah na tsane ruwan jikinta da wani towel d`in banda wanda ta d'aura, ta kalli mufida. "Bak'uwa kuma."?
"Eh, Wannan da muka gani a park dinnan ce.!
Gaban Hafsah yayi wata iriyar bugawa.
"Toh, jamila!!
Ta fad'a a hankali.
Sannan ta goge fuskarta kafin ta kuma cewa, "Kice ina zuwa bari na shirya."
Tunda aka, fad'a mata zuwan bak'uwar taji jikinta yayi sanyi.
Da kyar ta tattaro nutsuwa, ta shafa mai sannan ta dakko kayan da tayi niyyar sakawa tasa.
Bata tsaya shafa ko da powder ba, shima kafin ta k'arasa sai da mama ta leko ta.
"Hafsah kiyi sauri mana kin barta tana jiranki."?
"Mama gani nan, yanzu zan fito." Ta bada amsa da haka.
Maman ta k'ara kallonta sannan ta juya ta fita.
Leshin ya amshe ta sosai, tayi kyau duk da bata shafa komai ba, d'an kunne da agogo kawai ta saka, sannan ta fito palourn bayan tayi amfani da turarukan ta.
A palourn sunyi shuru, duka, sai Jamila da jefi jefi take kallon wasu shashi na palourn.
Gidan ya chanja sosai ba kamar yadda tasan shi da ba, an sami cigaba a tsarin gidan da komai ma.
Mama ce ta gaji da hasashen son gano wacece, don haka ta kalli Jamila tana murmushi tace, "Um kema wajen aikin naku d'aya da Hafasan ne."?
Jamila tayi yar dariya sannan tace, Aa, mama baki ganeni ba koh."?
Mama ta jinjina kai, naga kamar na san fuskar koh kina zuwa gidan ne.
Babu jiran komai Jamila tace, "Mama Jamila ce fah."
Tana murmushi.
Mama kallonta ta tsayi sosai, kallon mamaki da tambayoyi, da k'yar ta d`auke ido, tace tana 'yar dariya.
Laa, ai ban ganeki ba sam, ashe kece."
Daga nan ta rufe bakinta.
A Kofar shigowa daga waje ta palourn, Basheer ne ya shigo da sallama.
Mama ta amsa mishi, ya k'araso ciki, daidai lokacin kuma Hafsah itama ta fito daga d'akinta tana takowa zuwa cikin palourn.
Sai da Basheer yazo Tsakiyar palourn sannan yaga fuskar bak'uwar don kujerar da take kai cikin falon take kallowa, sai kuma yaga Hafsah ta fito tana fara,a cikin shigar da tafi kama data fita, badon bata saka mayafi ba, sannan yaji cikin fara,a tana ambaton sunan Jamila.
"Ah, Jamila Sannu da zuwa ashe kece.!!
Maganar data saka Basheer, juyawa ya kalli Jamila sosai.
Ta ganshi itama. Amma basu yiwa juna magana ba, ya nemi guri a kujera 1 _seater_ ya zauna.
Yana bin Hafsah da wani kallo na tuhuma lokacin da take cewaJamila, "shigo ciki mana."
Jamila ta mik'e ta bita. Mama bata ce musu komai ba sai kallo da tabi Jamila da shi, sannan ta k'ara sauke kallon akan Basheer.
Suna nesa dasu, bakin Basheer ya bude rai a b'ace yace, "Mama wai meyasa Yaya zata dinga yin irin haka ne."
Mama ta gane akan me yake magana, amma sai ta cigaba da kallonshi don neman k'arin bayani.
Meyasa dole tace sai ta kula waccan, bata ganin yanzu ba da bace, kinga ta gayyato mana ita gida koh."?
Mama ta danyi murmushi sannan tace, "Haba Basheer ai ba,a gudun mutum a duk halin da yake ciki, kuma ni yarinyar shekarunta nawa rabon da ka ganta a nan gidan, tun sanda akace _tabar gidansu fah._ Ba yawo sukayi da yayarka ba bare kace janta take suna fita."
Basheer ya sake bata rai, "Nidai mama bana son tana kulata bare har ta dinga zuwar mana gida, dama na sani tun ranar da muka ganta a park, Yaya ta wani rikice data ganta, saida taje sukayi magana sannan taji dad`i, shine fa sukayi exchange numbers"
Mama ta d'anyi shuru kafin tace, "Ba fad'a ya dace kayi ba, bayani zakayi mata yadda zata fahimta, amma ka fara zuba ido kaga tunda ai yau ka fara ganin tazo gidan koh."? Kuma ko babu komai Hafsah fa yayarka ce dole ka bi ta a hankali."
Basheer yayi shuru yana had'e rai, _shidai sam bai gamsu da zuwan Jamila ba, kuma har su shige daki ita da yayarshi._
A cikin d'akin kuma, suna shiga Hafsah cikin farin ciki, ta nunawa Jamila gefen gado, "Zauna mana."
Jamila tayi murmushi sannan ta nemi guri ta zauna.
Hafsah cikin rawar jiki ta fito don nemawa Jamila ruwa.
Ki shirya kinji, kada na saki kiyi late.. nagode, Allah ya tsare min ke."
Babu sauti amma ta motsa bakinta wajen cewa, "AMIIN."
Don taji dad`in kalaman shi.
Tanajin karar katse kiran shi amma bata motsa ba, ji take kamar ta sauke wani nauyi daga kanta, haka kawai ta yardarwa zuciyar ta, ukhashatu ba k'aramin sonta yake ba, daga jin muryar shi zaka tabbatar da haka.
A hankali ta motsa ta d`auki mai da niyyar shafawa, gaba-d`aya ji take kamar an kwashe mata duk wani _energy_ da ke jikin ta.
A sanyaye ta dinga yin komai, gefe kuma na zuciyarta tana mamakin kanta, da kuma tuhumar kanta kan kalmar da ta furta da sanyin safiyar nan.
Azuciyar ta take fata, _"Allah yasa takai Soyayyar ta inda zata sami kulawa, ba inda za,a cutar da ita ba."_
Bata sami nutsuwa ba, har sai da raunin da jiki da zuciyarta yayi ya kaita da fitar da wata 'yar kwalla, sai da ta goge a hankali, sannan taji ta sami k'wari.
Tun bakwai take shiri, amma saida nawa ta kaita har k'arfe takwas, hakan yasa mama biyota.
Ta ganta zaune ta gama saka kaya, tana d'aura d'ankwali.
Yaya, me kikeyi hakane, keda kika ce da wuri zaki fita kinga takwas har tayi fa.
Ita kanta ba zatace ga abinda ya tsaida ta d`in ba.
"Na gama mama."
"Kiyi sauri kizo kiyi break dai."
Ta gyada kai.
Gani nan mama."
Maman ta juya itama ta fita.
Ukhashatu, tsahon ranar yinin farin ciki yayi, jiyake babu wanda ya kaishi farin ciki a yau. Godiya yake kawai ga Allah don shi ya mallaka mishi ita. Zuciyar shi cike take fal da tsare tsaren yadda rayuwar su zata kasance shida ita.
Bai iya jurewa ba, har sai da kira wayarta da azahar amma Hafsah taki d'agawa, ji take bazata iya mishi magana a yau ba.
Yayi murmushi lokacin da kiran ya yanke.
Kawai sai ya zana mata _text messages_
_"Hmm, dole kik'i daga waya mana dama, kin rikita bawan Allah, kin barshi a rikice kuma.!!_
Text d`in dariya ya bata, ta dinga yinta, har abokiyar aikinta na tambayarta "meke faruwa."?
Sai kuma ta dinga jin kamar da ita yake, domin itace a rikice ai, tun safiyar yau."
Don ta kare kanta ta aika mishi da, _lots of work dear, let's phone to night.!!_
Sanda ya ida karantawa, sai da ya maimaita kalmar _Dear_ a fili.
Ya dinga murmushi shi kad'ai shima, yana fatan daren yayi da sauri.
Amma murnarshi ta koma ciki, daya tuna yana da meeting da daddaren..
📝
*HAJEEEYAH KHAREEMERH*
[17/03, 2:48 p.m.] UMAIMA BASHEER: ♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so (Guba ne)*
💔💔
*By*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Khareemerh)*
*Dedicated to unique in your love heart*
📄 *57*
____________________
Bai samu ya kuma kiranta ba a ranar, itama kuma sai taji tana da jiran kiranshi, amma bai kirata ba, haka ta hakura har zuwan lokacin baccinta.
Tana mamakin dalilin daya tare shi ga barin kiran nata.
Ranar data biyo baya, sukayi waya, dole ta saki jiki da shi, saboda salon shi, gareta. Duk wani abu da ukhasha zaiyi ya tabbatar mata da son da yake mata yayi shi, wani ta mayar mishi wani kuma ta bishi da murmushi ko tayi shuru, don yanzu ta gama fahimtar dawa take tare. _Wato shi mutum ne daya k'ware a ko ina, yana matuk'ar son yaga ya sakata farinciki kuma._
Daga k'arshe yake rok'onta akan ta barshi ya k'ara zuwa ya ganta.
Da take tambayar shi, yaushe yake so ce mata yayi.
Ko yaushe kika ce nazo zaki ganni."
Tayi dariya Kawai sannan tace, Aa dai mu bari sai k'arshen sati."
"Babu musu ya amince.
Allah ya kaimu lokacin."
Amiin tace mishi.
___________________
Shiri sosai Hafsah ta dinga yi ranar da ya kama zai zo d`in.
Har tunani ta shiga yi, me ya dace tayi mishi na tarbarshi."
Ta kasa tunana komai, k'arshe ta yanke shawarar bashi lemo da snacks kawai tunda suna da shi.
Shiri tayi alwashin yi sosai akan zuwan na shi. Ba su kara yin waya ba tun bayan wayar da sukayi, da rana.
Wani abu da ya da ya wargazawa Hafsah shiri, wanda badon zuwan Ukhasha ba babu abinda zatayi farinciki dashi kamar shi, amma sai zuciyarta ta kasu biyu gefe na jin dad`in hakan gefe kuma naga tunanin gudun samun matsala. Wato abin ba komai bane fa ce zuwan _Jamila_ a ranar.
Misalin k'arfe uku da rabi daidai na yamma, lokacin Hafsah na cikin toilet, don tayi alwashin shiryawa da wuri, ba zata b'ata mishi lokaci ba, sannan tayi alwashin zata nuna mishi soyayya daidai gwargwado yadda zai fahimci tana son shi itama.
Tana cikin band'akin taji sallama daga palourn mama kamar anyi bak'uwa. Bata damu ba take wankan ta a tsanake.
A falon kuma, mama ce zaune ita da mufida, tana mata tausa a k'afa, sukaji anyi sallama da wata iriyar muryar da ta sakasu juyawa duka, don basu gane wanene mai muryar ba.
Mama wata hamshak'iyar babbar mace ta gani, a cikin falonta, wacce ita a ganinta tafi mata kama da irin mata 'yan siyasa.
Mufida kuwa idonta ne yayi wani harr, sai da mai sallamar ta k'aras Shigowa sannan ta gane ta, don sun ganta Kwanaki ita da su yaya Hafsah.
Mama ce tace mata, "sannu da zuwa, zauna mana."
Ta tsuguna ta gaida maman kafin ta zauna a kujerar da aka bata.
Abun ya bawa mama mamaki matuk'a, kafin ta kai ga tambayarta wacece, ita taji tanacewa.
Mama, Hafsah na nan."?
Eh tana nan inji mama, tana k'ara kallon Jamila.
Sannan ta kalli mufida, "Jeki ki kira Hafsan."
Maman taga alamun kamar mufida tasan bak'uwar, amma babu damar ta tambaye ta, sannan da taji wajen Hafsah tazo, sai tafi alak'antata da abokan aikin Hafsah. Amma kuma taji kamar tasan muryar, amma ta manta a ina."?
Sanda mufida ta shigo d'akin hafsah na shirin fitowa daga toilet d`in, don haka ta d'an jirata ta fito.
"Yaya kinyi bak'uwa.
Hafsah na tsane ruwan jikinta da wani towel d`in banda wanda ta d'aura, ta kalli mufida. "Bak'uwa kuma."?
"Eh, Wannan da muka gani a park dinnan ce.!
Gaban Hafsah yayi wata iriyar bugawa.
"Toh, jamila!!
Ta fad'a a hankali.
Sannan ta goge fuskarta kafin ta kuma cewa, "Kice ina zuwa bari na shirya."
Tunda aka, fad'a mata zuwan bak'uwar taji jikinta yayi sanyi.
Da kyar ta tattaro nutsuwa, ta shafa mai sannan ta dakko kayan da tayi niyyar sakawa tasa.
Bata tsaya shafa ko da powder ba, shima kafin ta k'arasa sai da mama ta leko ta.
"Hafsah kiyi sauri mana kin barta tana jiranki."?
"Mama gani nan, yanzu zan fito." Ta bada amsa da haka.
Maman ta k'ara kallonta sannan ta juya ta fita.
Leshin ya amshe ta sosai, tayi kyau duk da bata shafa komai ba, d'an kunne da agogo kawai ta saka, sannan ta fito palourn bayan tayi amfani da turarukan ta.
A palourn sunyi shuru, duka, sai Jamila da jefi jefi take kallon wasu shashi na palourn.
Gidan ya chanja sosai ba kamar yadda tasan shi da ba, an sami cigaba a tsarin gidan da komai ma.
Mama ce ta gaji da hasashen son gano wacece, don haka ta kalli Jamila tana murmushi tace, "Um kema wajen aikin naku d'aya da Hafasan ne."?
Jamila tayi yar dariya sannan tace, Aa, mama baki ganeni ba koh."?
Mama ta jinjina kai, naga kamar na san fuskar koh kina zuwa gidan ne.
Babu jiran komai Jamila tace, "Mama Jamila ce fah."
Tana murmushi.
Mama kallonta ta tsayi sosai, kallon mamaki da tambayoyi, da k'yar ta d`auke ido, tace tana 'yar dariya.
Laa, ai ban ganeki ba sam, ashe kece."
Daga nan ta rufe bakinta.
A Kofar shigowa daga waje ta palourn, Basheer ne ya shigo da sallama.
Mama ta amsa mishi, ya k'araso ciki, daidai lokacin kuma Hafsah itama ta fito daga d'akinta tana takowa zuwa cikin palourn.
Sai da Basheer yazo Tsakiyar palourn sannan yaga fuskar bak'uwar don kujerar da take kai cikin falon take kallowa, sai kuma yaga Hafsah ta fito tana fara,a cikin shigar da tafi kama data fita, badon bata saka mayafi ba, sannan yaji cikin fara,a tana ambaton sunan Jamila.
"Ah, Jamila Sannu da zuwa ashe kece.!!
Maganar data saka Basheer, juyawa ya kalli Jamila sosai.
Ta ganshi itama. Amma basu yiwa juna magana ba, ya nemi guri a kujera 1 _seater_ ya zauna.
Yana bin Hafsah da wani kallo na tuhuma lokacin da take cewaJamila, "shigo ciki mana."
Jamila ta mik'e ta bita. Mama bata ce musu komai ba sai kallo da tabi Jamila da shi, sannan ta k'ara sauke kallon akan Basheer.
Suna nesa dasu, bakin Basheer ya bude rai a b'ace yace, "Mama wai meyasa Yaya zata dinga yin irin haka ne."
Mama ta gane akan me yake magana, amma sai ta cigaba da kallonshi don neman k'arin bayani.
Meyasa dole tace sai ta kula waccan, bata ganin yanzu ba da bace, kinga ta gayyato mana ita gida koh."?
Mama ta danyi murmushi sannan tace, "Haba Basheer ai ba,a gudun mutum a duk halin da yake ciki, kuma ni yarinyar shekarunta nawa rabon da ka ganta a nan gidan, tun sanda akace _tabar gidansu fah._ Ba yawo sukayi da yayarka ba bare kace janta take suna fita."
Basheer ya sake bata rai, "Nidai mama bana son tana kulata bare har ta dinga zuwar mana gida, dama na sani tun ranar da muka ganta a park, Yaya ta wani rikice data ganta, saida taje sukayi magana sannan taji dad`i, shine fa sukayi exchange numbers"
Mama ta d'anyi shuru kafin tace, "Ba fad'a ya dace kayi ba, bayani zakayi mata yadda zata fahimta, amma ka fara zuba ido kaga tunda ai yau ka fara ganin tazo gidan koh."? Kuma ko babu komai Hafsah fa yayarka ce dole ka bi ta a hankali."
Basheer yayi shuru yana had'e rai, _shidai sam bai gamsu da zuwan Jamila ba, kuma har su shige daki ita da yayarshi._
A cikin d'akin kuma, suna shiga Hafsah cikin farin ciki, ta nunawa Jamila gefen gado, "Zauna mana."
Jamila tayi murmushi sannan ta nemi guri ta zauna.
Hafsah cikin rawar jiki ta fito don nemawa Jamila ruwa.