Sashe 47
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai kawai, sukaji an turo kofar, mama ce ta shigo, babu mamaki idan aka ce taji duk abinda Hafsah ta fad'awa Fateema, don basu san dad'ewarta ba, ajikin k'ofar ta zo, ne da niyyar kiran Hafsah, don su d'ora daga inda suka tsaya, a tuhumar da maman ke yi mata, sai kuma taji Hafsah nayin magana, nan ta dakata taji komai, ita kanta abun ya shigeta, _Tabbas qawaye suna iya chanjawa 'yarka tarbiyya cikin kankanin lokaci._
Amma sai ta shigo kamar bataji komai ba, tayi wa Hafsah nuni data biyo ta, _Hafsah ta miqe ta fi maman suka wuce, d'akin ta, fatanta Allah yasa, maman bataji koda kalma d'aya cikin abinda ta labartawa Fateema ba..._
📝
*HAJEEYAH*
*KHAREEMERH.*
♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so (Guba ne)*
💔💔
*By*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Khareemerh)*
*Dedicated to unique in your love heart*
📄 *43*
*"Kinyi sallar"?*
Kalmomin da mama ta fara da su kenan, daga isar su d'akinta.
Ahankali Hafsah ta girgiza kai..
"To me kika tsaya yi."?
"Babu komai."
Tayi mata nuni da toilet d'inta dake cikin d'akin, "shiga nan kiyi."
Ta wuce da sauri, babu b'ata lokaci tayo alwalar ta dawo ta tada sallah.
Bayan ta idar, har zuwa lokacin cin abinci, har zuwa lokacin bacci, mama bata k'ara yi mata tambaya mai kama da tuhuma, ko neman k'arin bayani akan fitar da tayi ba.
Ta tsammaci haka, a lokuta da dama, ko kwakwkwaran motsi maman tayi, sai Hafsah ta tsargu.
Amma maman sam ta share zancen. Hafsah kam ta zargi abubuwa da dama acikin zuciyarta, a hankali ta d'an saki jiki daga zaman d`ar-d`ar d`in da take da maman, ga kunyar marin da maman tayi mata ta lullub'eta. Ya akayi tayi kuskuren yi mata laifin da har ta iya kai hannu jikinta.? Tana matuqar nadamar yin laifin, da ta sani tayi mata koda k'aryar zuwa wani waje ce, duk da dai koma menene ya riga da ya faru, gashi tsoron had'a idonta da na maman take ko magana take mata kanta a k'asa, don wani kwarjini na musamman maman ta kara a idon hafsan, tun bayan ta tasha yatsunta biyar.
"Dakina zaki kwana Hafsah."
Maman ta fad'a lokacin da fateema ke shirin barin parlour don zuwa bacci, Hafsah ma ta mik`e da niyyar binta.
A sanyaye ta dawo da alama bataji dadin hakan ba.
"Ki je ki dakko duk wani abinda zaki buk'ata."
Mama ta sake kallonta ta fada mata haka.
Da sauri ta mik`e ta fice.
Tana isa dak'in ta tarar Fateema na kad'e zanin gado, ( _bed sheet_ ) taji shigowar mutum don haka ta ta waigo.
Ta saki murmushi, Aike Hafsah kin zama 'yar dakin mama.)
"Allah Fateema kunyar mama nakeji."
"Hmm, Hafsah kenan Allah baki da matsala fa, rashin sani ne ya sakaki yanke hukunci da kanki, amma mama sam bata da matsala, kinga ko ni da ni da nake matsayin 'yarta wallahi bana boye mata komai akan al,amran samari na."
Hafsah tayi ajiyar zuciya, "Ya zanyi in fara tunkarar mama da irin wannan zantukan shirmen.."? Ta girgiza kai, "Bazan iya ba.!!
"Hmm, shikenan."
Cewar Fateema.
Hafsah ta chanja kayanta zuwa na bacci, sannan ta d`auki blanket, "Sai da safenki!!
Ta fad'awa Fateema, sannan ta fice. Fateema ta bita da kallo tana murmushi, tabbas tana da yak`inin cewa mama ba zata tab'a barin Hafsah ta shiga garari ba, don ta tabbatar maman taji hirar su kaf, daga ganin yanayinta.
"Ki kwanta a kan gado, ni ba kullum nake kwanan gado ba."
Maman tacewa Hafsah, bayan ta shigo, tana kan dardumarta tana jan carbi.
Ta d'ora, "Amma kiyo alwala tukuna, sannan kiyi addu,a."
Hafsah ta daga kai alamar "Toh."
Salin-alin Hafsah tayi baccinta, kuma taji dad`i da ba gefen mama ta kwanta ba, ji tayi ma kamar ba ayi mata chanjin wajen kwana ba.
Da asuba mama ta tashe ta, sannan ta fita tashin sauran yaran.
Bata barta ta koma bacci ba, _"Zauna yau kema kiyi lazimi."_ haka ta fada mata. Sai da rana ta b'ullo lokacin kuma maman ta gama shirinta na fita office, "Tunda ba zaki karya yanzu ba, sai ki kwanta, maybe karfe 2:00pm, ma ni na dawo, sannan asabe ( _tana nufin me aikinta_ ) zata zo, sai kuyi aikin tare kiyi mana abincin rana."
"To, mama me za,a dafa."? Inji Hafsah cikin ladabi.
Cikin murmushi tace, "Kin iya tuwo."?
Hafsa tayi murmushi itama tana d'aga kai.
"To kiyi mana shi, miyar agushi kuma saura naga bai tuk'u ba." Maman tayi maganar da sigar zolaya.
Sannan ta cigaba da cewa, "ki duba akwai komai cikin kitchen d'in, da kwai nama a fridge."
"To mama."
Suka fito palour tare.. Lokacin duk yaran sun Ida shiryawa har da Fateema. "Yawwa kuyi sauri tare duk zamu fita tun da kunga Nazeer baya nan bare ya kaiku." _Mama ta fada musu haka._
Kamar kuma tayi mantuwa sai, tayi sauri, ta koma d'akinta tare da kwalowa Hafsah kira.
Tana shigowa ta durqusa "mama gani, maman na tsaye bata zauna ba, tayi mata nuni, "Tashi tashi sauri nake."
Tana ida mik'ewa ta nuna ta da yatsa.
"Kada ki ga sai ke kad'ai a gida, kiyi tunanin, fita koda bakin gate ne, zan fad'awa mai gadi ma, kuma muddin kikayi attempting fita zaki gamu da fushi na.!!
Babu alamun wasa a fuskar maman tayi mata wannan maganar.
Daga kai kawai Hafsah, ke faman yi alamar, "Toh."
Azuciyarta, tana cewa, ( _"wane Tsautsayin ne zai qara fitar dani.!!_)
Sai na dawo, maman ta fad`a da murmushi kamar ba ita tayi wannan maganar yanzu ba.
"Adawo lafiya."
"Allah yasa, Maza ayi bacci, bye."
Ta fita tana daga mata hannu. Hafsah taji wata 'yar dariya tazo mata, ko ta mecece oho, ta fada kan gadon tayi shuru har bacci ya d`auke ta.
Sai wajen, sha d'aya, ta farka, ta nemi abu mai sauk'i tayi break dashi lokacin kuma, me aikin har, taci rabin wanke-wanke.
Hafsah tayi wanka sannan ta, fara shirin dora girkin, suna yi suna hira ita da me aikin, wacce bazata wuce shekaru 35 ba, tana da 'ya'ya uku da mijinta ya rasu ya bar mata. Duk a hirar su ne take fad'awa Hafsah.
Hafsah ta k'ara godewa Allah, a zuciyarta tana cewa, _"Gaskiya akwai masu buqatar taimako a duniyar nan!_
Sanda mama ta dawo, fara,arta ta zarce ta safiya, musamman da taga an gama komai gidan tsaf, kamar babu abinda ya faru, sai zolayar Hafsah ta take, "Toh zubo min Tuwon naki mana, nayi testing, ice ko babu hannun asabe a girkin."?
Suna dariya asabe tace, "Ita tayi abinta wallah, ai d'iyar taki ba daga nan ba, nima nace 'ko training d`in aure aka kawota ta d'auka.? Mama tayi murmushi kawai, Hafsah tabar gurin da sauri da alama taji kunya."!
Wasa wasa har kwana hud`u, da alama ma mama ta manta Hafsah tayi wani laifi.( _A ganin Hafsan don ganin yadda maman ke janta a jiki fiye da koyaushe_)
Tunda, Nazeer ya tafi taji gidan ya k'ara yi mata dad'i, jiya ne ma daya kira Fateema, suna waya yace ta bawa Hafsan, babu yadda zatayi haka ta karba suka gaisa.
Da yammacin ranar Juma,a tana taya mama gyaran drawer, sai ga ledar da Yusuf ya bata, dam, gabanta ya fadi tare dajin wani farin ciki ya mamaye zuciyarta, gaskiya tana cikin tsananin kewa, in ba don idon maman yakai kai ba, da babu abinda zai hanata da fe abarta ta b'oye.
Maman ta fi ta hanzari wajen sunkuyawa ta dakko ledar, ta lura sosai da yanayin Hafsan."
"In ba don Laifin da kikayi min ba ai da tuni na baki abubuwan ki ai."
'Inji mama, tana so ne ta shigar da Hafsah hayyacin ta, ta dinga gane abubuwan da suke rufe mata ido suna kaita ne kawai suna baro ta babu wani riba.
_Don a kasan zuciyarta ko hafsah batayi mata wanna laifin ba, bata da niyyar bata wayar yanzu, don bata ga amfanin hakan ba._
Hafsah ta langab'ar da kai kawai, tana bawa kanta laifi.
Hakan ya bawa mama damar cigaba da magana, tabar wancen zancen ta kamo wani, don ta samu ta aika sak'oninta ga Hafsah.
"Hafsah.!!
Ta kira sunan Hafsah a hankali,
Cikin sanyi ta amsa itama.
Kuna zuwa islamiyya koh, Hafsah ta jinjina kai,
"Yawwa." inji mama.
Kinsan shikashikan musulinci koh"?
Hafsah ta k'ara jinjina kai, har yanzu da mamakin tambayoyin a fuskar ta.
"To fad'a min su."
Ta d`anyi shuru sai kuma ta tuna kada mama ta zaci ko bata sani bane, yasa ta shuru. Don Allah a hankali ta fara zayyyano su.
Tana gamawa mama tace _"To saura na imami."_
Hafsah ta fad'o su guda shiddan nan, tanayi tana kallon mama, so take taji dalilin tambayoyin.
Yawwa, 'ya ta."
Ashe dai baki manta karatun islamiyyar ba.
( _zuwa yanzu sun kammala gyaran, amma har yanzu ledar na hannun mama._ )
Mama ta zauna gefen gadon, Hafsah ta zauna kasa gefenta.
"To me ake nufi kaddarar da naji kin fad`a. aciki"?
Hafsah ta kulle baki da alama bata san yadda zata faro bada amsar ba.
"Uhum."? Inji mama.
"Baki sani ba."
"Ta jinjina kai."
"Hmm.. To marin da na yi miki rannan shi ma ai kaddara sunan shi koh."
Kunya sosai ta lullub'e Hafsah ta sinne kai a cinyoyin ta tana dariya.
"Hmm, bada wasa nake miki ba Hafsah, tunda har an koya miki a makaranta, kuma kin iya kina fad'a to kuwa dole kiyi amfani dashi.
"Kinaji nah.."? Hafsah ta daga kai.
Cikin muryar nutsuwa mama ta fara mata jawabi.
_"Kin sani a makaranta, an koya muku, dole ne mutum ya nemi ilimi kuma dole yayi amfani da ilimin sa Koh?._
Hafsah ta daga kai.
Ta tausasa muryar ta. "Ki fada min gaskiya kinji kada ki boye min ni maman kice. " _Kina son Yusuf_ "?
Hartar cikin Hafsah ta kad`a wani irin tsoro ya mamayeta. _Sunan Yusuf, kuma daga bakin mama."_?
_Kina son shi._"?
Mama ta k'ara maimaita mata tambayar. _"To ko kuma wannan wata dama ce ta samu, wajen dawo da yusuf bisa hanya, tunda har mama ta shigo cikin zancen."_ ?
Amma sai ta shigo kamar bataji komai ba, tayi wa Hafsah nuni data biyo ta, _Hafsah ta miqe ta fi maman suka wuce, d'akin ta, fatanta Allah yasa, maman bataji koda kalma d'aya cikin abinda ta labartawa Fateema ba..._
📝
*HAJEEYAH*
*KHAREEMERH.*
♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(Masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so (Guba ne)*
💔💔
*By*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Khareemerh)*
*Dedicated to unique in your love heart*
📄 *43*
*"Kinyi sallar"?*
Kalmomin da mama ta fara da su kenan, daga isar su d'akinta.
Ahankali Hafsah ta girgiza kai..
"To me kika tsaya yi."?
"Babu komai."
Tayi mata nuni da toilet d'inta dake cikin d'akin, "shiga nan kiyi."
Ta wuce da sauri, babu b'ata lokaci tayo alwalar ta dawo ta tada sallah.
Bayan ta idar, har zuwa lokacin cin abinci, har zuwa lokacin bacci, mama bata k'ara yi mata tambaya mai kama da tuhuma, ko neman k'arin bayani akan fitar da tayi ba.
Ta tsammaci haka, a lokuta da dama, ko kwakwkwaran motsi maman tayi, sai Hafsah ta tsargu.
Amma maman sam ta share zancen. Hafsah kam ta zargi abubuwa da dama acikin zuciyarta, a hankali ta d'an saki jiki daga zaman d`ar-d`ar d`in da take da maman, ga kunyar marin da maman tayi mata ta lullub'eta. Ya akayi tayi kuskuren yi mata laifin da har ta iya kai hannu jikinta.? Tana matuqar nadamar yin laifin, da ta sani tayi mata koda k'aryar zuwa wani waje ce, duk da dai koma menene ya riga da ya faru, gashi tsoron had'a idonta da na maman take ko magana take mata kanta a k'asa, don wani kwarjini na musamman maman ta kara a idon hafsan, tun bayan ta tasha yatsunta biyar.
"Dakina zaki kwana Hafsah."
Maman ta fad'a lokacin da fateema ke shirin barin parlour don zuwa bacci, Hafsah ma ta mik`e da niyyar binta.
A sanyaye ta dawo da alama bataji dadin hakan ba.
"Ki je ki dakko duk wani abinda zaki buk'ata."
Mama ta sake kallonta ta fada mata haka.
Da sauri ta mik`e ta fice.
Tana isa dak'in ta tarar Fateema na kad'e zanin gado, ( _bed sheet_ ) taji shigowar mutum don haka ta ta waigo.
Ta saki murmushi, Aike Hafsah kin zama 'yar dakin mama.)
"Allah Fateema kunyar mama nakeji."
"Hmm, Hafsah kenan Allah baki da matsala fa, rashin sani ne ya sakaki yanke hukunci da kanki, amma mama sam bata da matsala, kinga ko ni da ni da nake matsayin 'yarta wallahi bana boye mata komai akan al,amran samari na."
Hafsah tayi ajiyar zuciya, "Ya zanyi in fara tunkarar mama da irin wannan zantukan shirmen.."? Ta girgiza kai, "Bazan iya ba.!!
"Hmm, shikenan."
Cewar Fateema.
Hafsah ta chanja kayanta zuwa na bacci, sannan ta d`auki blanket, "Sai da safenki!!
Ta fad'awa Fateema, sannan ta fice. Fateema ta bita da kallo tana murmushi, tabbas tana da yak`inin cewa mama ba zata tab'a barin Hafsah ta shiga garari ba, don ta tabbatar maman taji hirar su kaf, daga ganin yanayinta.
"Ki kwanta a kan gado, ni ba kullum nake kwanan gado ba."
Maman tacewa Hafsah, bayan ta shigo, tana kan dardumarta tana jan carbi.
Ta d'ora, "Amma kiyo alwala tukuna, sannan kiyi addu,a."
Hafsah ta daga kai alamar "Toh."
Salin-alin Hafsah tayi baccinta, kuma taji dad`i da ba gefen mama ta kwanta ba, ji tayi ma kamar ba ayi mata chanjin wajen kwana ba.
Da asuba mama ta tashe ta, sannan ta fita tashin sauran yaran.
Bata barta ta koma bacci ba, _"Zauna yau kema kiyi lazimi."_ haka ta fada mata. Sai da rana ta b'ullo lokacin kuma maman ta gama shirinta na fita office, "Tunda ba zaki karya yanzu ba, sai ki kwanta, maybe karfe 2:00pm, ma ni na dawo, sannan asabe ( _tana nufin me aikinta_ ) zata zo, sai kuyi aikin tare kiyi mana abincin rana."
"To, mama me za,a dafa."? Inji Hafsah cikin ladabi.
Cikin murmushi tace, "Kin iya tuwo."?
Hafsa tayi murmushi itama tana d'aga kai.
"To kiyi mana shi, miyar agushi kuma saura naga bai tuk'u ba." Maman tayi maganar da sigar zolaya.
Sannan ta cigaba da cewa, "ki duba akwai komai cikin kitchen d'in, da kwai nama a fridge."
"To mama."
Suka fito palour tare.. Lokacin duk yaran sun Ida shiryawa har da Fateema. "Yawwa kuyi sauri tare duk zamu fita tun da kunga Nazeer baya nan bare ya kaiku." _Mama ta fada musu haka._
Kamar kuma tayi mantuwa sai, tayi sauri, ta koma d'akinta tare da kwalowa Hafsah kira.
Tana shigowa ta durqusa "mama gani, maman na tsaye bata zauna ba, tayi mata nuni, "Tashi tashi sauri nake."
Tana ida mik'ewa ta nuna ta da yatsa.
"Kada ki ga sai ke kad'ai a gida, kiyi tunanin, fita koda bakin gate ne, zan fad'awa mai gadi ma, kuma muddin kikayi attempting fita zaki gamu da fushi na.!!
Babu alamun wasa a fuskar maman tayi mata wannan maganar.
Daga kai kawai Hafsah, ke faman yi alamar, "Toh."
Azuciyarta, tana cewa, ( _"wane Tsautsayin ne zai qara fitar dani.!!_)
Sai na dawo, maman ta fad`a da murmushi kamar ba ita tayi wannan maganar yanzu ba.
"Adawo lafiya."
"Allah yasa, Maza ayi bacci, bye."
Ta fita tana daga mata hannu. Hafsah taji wata 'yar dariya tazo mata, ko ta mecece oho, ta fada kan gadon tayi shuru har bacci ya d`auke ta.
Sai wajen, sha d'aya, ta farka, ta nemi abu mai sauk'i tayi break dashi lokacin kuma, me aikin har, taci rabin wanke-wanke.
Hafsah tayi wanka sannan ta, fara shirin dora girkin, suna yi suna hira ita da me aikin, wacce bazata wuce shekaru 35 ba, tana da 'ya'ya uku da mijinta ya rasu ya bar mata. Duk a hirar su ne take fad'awa Hafsah.
Hafsah ta k'ara godewa Allah, a zuciyarta tana cewa, _"Gaskiya akwai masu buqatar taimako a duniyar nan!_
Sanda mama ta dawo, fara,arta ta zarce ta safiya, musamman da taga an gama komai gidan tsaf, kamar babu abinda ya faru, sai zolayar Hafsah ta take, "Toh zubo min Tuwon naki mana, nayi testing, ice ko babu hannun asabe a girkin."?
Suna dariya asabe tace, "Ita tayi abinta wallah, ai d'iyar taki ba daga nan ba, nima nace 'ko training d`in aure aka kawota ta d'auka.? Mama tayi murmushi kawai, Hafsah tabar gurin da sauri da alama taji kunya."!
Wasa wasa har kwana hud`u, da alama ma mama ta manta Hafsah tayi wani laifi.( _A ganin Hafsan don ganin yadda maman ke janta a jiki fiye da koyaushe_)
Tunda, Nazeer ya tafi taji gidan ya k'ara yi mata dad'i, jiya ne ma daya kira Fateema, suna waya yace ta bawa Hafsan, babu yadda zatayi haka ta karba suka gaisa.
Da yammacin ranar Juma,a tana taya mama gyaran drawer, sai ga ledar da Yusuf ya bata, dam, gabanta ya fadi tare dajin wani farin ciki ya mamaye zuciyarta, gaskiya tana cikin tsananin kewa, in ba don idon maman yakai kai ba, da babu abinda zai hanata da fe abarta ta b'oye.
Maman ta fi ta hanzari wajen sunkuyawa ta dakko ledar, ta lura sosai da yanayin Hafsan."
"In ba don Laifin da kikayi min ba ai da tuni na baki abubuwan ki ai."
'Inji mama, tana so ne ta shigar da Hafsah hayyacin ta, ta dinga gane abubuwan da suke rufe mata ido suna kaita ne kawai suna baro ta babu wani riba.
_Don a kasan zuciyarta ko hafsah batayi mata wanna laifin ba, bata da niyyar bata wayar yanzu, don bata ga amfanin hakan ba._
Hafsah ta langab'ar da kai kawai, tana bawa kanta laifi.
Hakan ya bawa mama damar cigaba da magana, tabar wancen zancen ta kamo wani, don ta samu ta aika sak'oninta ga Hafsah.
"Hafsah.!!
Ta kira sunan Hafsah a hankali,
Cikin sanyi ta amsa itama.
Kuna zuwa islamiyya koh, Hafsah ta jinjina kai,
"Yawwa." inji mama.
Kinsan shikashikan musulinci koh"?
Hafsah ta k'ara jinjina kai, har yanzu da mamakin tambayoyin a fuskar ta.
"To fad'a min su."
Ta d`anyi shuru sai kuma ta tuna kada mama ta zaci ko bata sani bane, yasa ta shuru. Don Allah a hankali ta fara zayyyano su.
Tana gamawa mama tace _"To saura na imami."_
Hafsah ta fad'o su guda shiddan nan, tanayi tana kallon mama, so take taji dalilin tambayoyin.
Yawwa, 'ya ta."
Ashe dai baki manta karatun islamiyyar ba.
( _zuwa yanzu sun kammala gyaran, amma har yanzu ledar na hannun mama._ )
Mama ta zauna gefen gadon, Hafsah ta zauna kasa gefenta.
"To me ake nufi kaddarar da naji kin fad`a. aciki"?
Hafsah ta kulle baki da alama bata san yadda zata faro bada amsar ba.
"Uhum."? Inji mama.
"Baki sani ba."
"Ta jinjina kai."
"Hmm.. To marin da na yi miki rannan shi ma ai kaddara sunan shi koh."
Kunya sosai ta lullub'e Hafsah ta sinne kai a cinyoyin ta tana dariya.
"Hmm, bada wasa nake miki ba Hafsah, tunda har an koya miki a makaranta, kuma kin iya kina fad'a to kuwa dole kiyi amfani dashi.
"Kinaji nah.."? Hafsah ta daga kai.
Cikin muryar nutsuwa mama ta fara mata jawabi.
_"Kin sani a makaranta, an koya muku, dole ne mutum ya nemi ilimi kuma dole yayi amfani da ilimin sa Koh?._
Hafsah ta daga kai.
Ta tausasa muryar ta. "Ki fada min gaskiya kinji kada ki boye min ni maman kice. " _Kina son Yusuf_ "?
Hartar cikin Hafsah ta kad`a wani irin tsoro ya mamayeta. _Sunan Yusuf, kuma daga bakin mama."_?
_Kina son shi._"?
Mama ta k'ara maimaita mata tambayar. _"To ko kuma wannan wata dama ce ta samu, wajen dawo da yusuf bisa hanya, tunda har mama ta shigo cikin zancen."_ ?