← Book details Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 88

Sashe 16

Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kwance yake akan gadonshi daga shi sai singlet da gajeren wando. Ya kwanta rub da ciki.
Wani tunanin shima yake yi daban.
Yana jin dad'in yadda yarinyar take sonshi sosai, shima kuma yasan yana sonta, amma matsalar yarinyar 'Local ce'
Yusuf kenan ke tariyo (tunanin) irin rayuwar da sukeyi shi da Hafsah. Abin na bashi mamaki wani lokacin kuma yana jin takaicin hakan.
Kamanninta ya shigo tunowa.
Kyakykyawa ce, shi dai ta mishi kyau! yana son komai nata, amma me yasa bata mishi soyayya irin wacce yake so?
Ta iya kalamai masu sanyaya zuciya (sweet words) ta iya kwalliya, ita d'in kalar manyan yara ce.
"Her smile kills me!
Ya fad'a a hankali.
Yusuf yana son ya samo musu mafita ne akan k'in yarda dashi da Hafsah keyi.
A ganinshi "zama cikin mutane d'aya masu yare d'aya, al,ada d'aya, addini d'aya shiya sa ta rashin wayewa. A ganin shi Hafsa nayin rayuwar _kifi acikin rijiya ne._
Matsalalolin ya kasa kashi-kashi da niyyar samo musu mafita.
Na farko shine 'Rashin yarda dashi da Hafsah keyi, wanda ya danganta shi da 'rashin wayewa'..
Yasani cewa fushinsa na rikitata, saboda haka ya d'auki aniyar nuna mata fushinshi a duk sanda tayi mishi hakan, tare da yi mata barazanar rabuwa da ita, har lokacin da zata bada kai...
Yayi murmushi samun nasara don yasan Hafsah bata da jarumtar jure fushinshi.
Na biyu kuma Rashin wayewarta da zama waje d'aya, mafitarsu a wajensa shine d'aukarta su dinga fita yawon shak'atawa lokaci zuwa lokaci.
Sai kuma sauran banbance banbance dake tsakaninsu wanda zai mayar da hankali wajen sace zuciyarta, hakan zai sakata zama daidai da ra,ayinshi.
*TSOKACI*
Sau da dama zama baya yiyuwa idan ra,ayi ko kuma hali bai zo d'aya ba, sai dai idan d'aya ya rinjayi d'ayan bisa ga bin ra,ayinshi.

Akwai banbance - banbance da yawa tsakanin yusuf da kuma Hafsah. Wanda silar su shine samun dace da iyayen kirki da kuma tarbiyya, sai kuma aka sami akasin haka daga b'angaren 'Yusuf'
Haka fahimtar da suka yiwa soyayya ma da akwai banbanci.
A wajen Hafsah ta d'auki soyaya ne irin ta saurayi da budurwa a matsayin : 'Musayar kalaman soyyaya a tsakanin masoya sai kuma kyautatawa da kuma sadaukarwa ga juna da kuma fatan zama a Inuwa d'aya wato 'Aure'
A wajen Yusuf kuwa yana ganin soyayya Itace farantawa juna da kuma zama d'aya babu banbanci.
'Duk da addini da al,ada sun nuna banbancin inda aka saka wani geji 'iyaka' tsanin Mace da Namiji a wajen mu,amala.'
To shi Yusuf bai ga wannan ba gurinshi ma idan dai 'True Love' ake yi babu zancen wani addini ko kuma al,ada kawai a zauna a bi ra,ayin zuciyoyi.
Domin a wajen shi 'Sacrifice' wato sadaukarwar da Hafsah ke ik'irarin tana masa ba ita bace, tunda ita ganin ta bashi 'Dukkan yarda' shine ta sadaukar mishi komai.
Shi kuma yana ganin idan gaske ne sadaukarwar tata ya dace ya gani a aikace ba ik'irarin da kalmomin baki ba. Shi yasa yake tantama bisa son da take mishi.
Rashin dacen Yusuf da iyayen kirki yasashi fad'awa cikin wannan hali da kuma gurb'ataccen tunani.
Wato tun yana yaro d'an kimamin shekara goma sha biyu, ya tashi cikin wata 'wahalalliyar rayuwa', wanda shi yasanta kuma zai kirata da wahala.
Wato iyayenshi kanyi wasu abubu
agabanshi wanda sun d'auke shi shi yaro ne. Ba ruwan su, kasancewarshi a kusa da su baya hanasu yin wani abu daya shafi mu,amalar aurensu.. Sannan yana zuwa gidan abokanshi 'Turawa' yana ganin yadda suke yi.
Tunanin shi ya kulle da son gano hakan menene? Amma saboda k'arancin shekaru ya kasa ganowa, sai lokacin daya kai munzalin wasu shekaru 15 -16, kuma akayi rashin dacen yana da yanayin buk'atar hakan sosai. Alokacin ne kuma ya bazama nema wa kanshi mafita.
Yusuf nada k'awaye mata a makaranta wanda suke mu,amala tare, kasancewarsu turawa sai ra,ayinsu ya dace da na juna.
Sukanyi mu,amalarsu kamar babu banbancin 'Jinsi' a tsakaninsu.
Yusuf a lokacin nada budurwa 'Jessica' wacce suke soyayyarsu ta yarinta.
Mummy shi ta b'ata bude Diary nashi wata rana.
Yayi rubutu a cikin abin gwanin takaici, wanda ita hakan ya burgeta.

*'My Love Jessica and I'*
Our first time kiss was at school garden..
Rubutu ne sosai yadda abin ya faru, tsaf mummynshi ta karanta, amma ta share abin tayi murmushi.
Wai d'anta ashe ya girma haka?? 😡😒
Da irin wad'annan abubuwa ne kuke ganin rayuwar Yusuf da Hafsah zata tafi a Inuwa d'aya bayan kuma gefe ga Abba na shirin kafawa ya tsare??🤔
Anya ba ko dole wani daga cikin su yayi watsi da nashi ra,ayin ya bi na d'an uwanshi ba?
Idan hakane wa kuke ganin zai sauke nashi ra,ayin zuciyar YUSUF KO KUMA HAFSAH??🤔🤔
Muna Jiran ra,ayinku.
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔

Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to :Unique In Your Love Heart Members.
*AUNTY KHADIJAH (MK MAKEOVER💄💋)..GODIYA NKE,👏🏼 _KUMA MUNA BOOKING IDAN BIKIN HAFSAH DA YUSUF😅 YA ZO,_ KE ZAKI MATA KWALLIYA.*

Zamu hadu a page dinki na instagram #MK makeover.

*And also*
*D'AYA AUNTYN.*
*(AUNTY FATIMAH, MAMAN LITTLE MAMIE).. ALLAH Y A RAYA WANNAN BABY YA KUMA BATA GASHI IRIN NA FILLO KAMAR NAKI..*👍🏻👏🏼👏🏼

📄 *20*

*Washe gari* da asuba, abban ne da kanshi ya shigo ya tashe ta, kamar babu abinda ya faru..
A al,adarshi 'knocking' dama yake mata sai kuma ya tabbatar ta tashi ta bud'e kofa, sannan zai wuce masallaci.
Gabanta ya fad'i lokacin da taji shi yana kiranta, amma kuma hankalinta ya kwanta da taji yanayin kiran, dama baya d'aga muryarshi da asuba..
"Yaya,..Yaya, ki tashi kiyi sallah."
Ahankali ta mik'e ta bud'e kofar.
Tun da yaga ta bud'e ya juya.
Tayi hamdala a zuciyarta bata son had'a ido da abban nata.
Akan darduma ta zauna bayan ta idar da sallah ta, tunano ta ina zata fara tun karar Yusuf da maganar abbah ta ke.
Gashi ya k'wace wayar bare ta kira shi. Ta mik'e ta bud'e wata jaka ta dakko zoben da Yusuf ya bata, ta dawo ta zauna.
'Tun ranar da aka koma makaranta ta karb'a a wajen Mama tace mata, zata mayarwa da Basma, shine ta boy'e shi.'
Ta kur'a wa zoben ido, tana tunano wanda ya mallaka mata shi, ahankali kwallah ta cika idanunta.
Allah ka taimakeni.. Allah kasa kada Abba ya rabani da farin ciki nah!!
'Idan na rabu da Yusuf na rasa komai.
Ta janyo Diary d'inta da yake akan 'Bed side drawer' (gefen Gado)
*'Together forever'*
_Our love is built up with scriface and devotion.._
_I will not let it be possible..!!_
_And.._
_I promise you to be
_with you forever no matter what difficult and challenges I'm_ _gonna face.._
" _I love you my_ _Yusuf!_

Ta rufe Diaryn ta ajye, sannan ta mik'e ta nufi kitchen wajen Mama, tasan ita ma babu dad'i ta kwana.
Maman tana kitchen d'in kuwa.
Tayi sallama tare da cewa,
"Mama,Gudmorning"Maman ta kalleta
"An tashi lpia"
"Lpia lau."
"Bari in fere miki dankalin."
"Ok kiyi sauri to, kinga kada ku makara a school."
"Ta k'ara kallonta.
Idan kin gama kije ki bawa abbanku hak'uri."
"To Mama"
Tana gamawa ta mik'e ta nufi d'akin Abban, gabanta na fad'uwa.
A tsaye ta tarar dashi a falon shi ya rataya jakarshi yana shirin fita.
Tayi saurin durk'usawa har k'asa.
"Abba barka da safiya"
Ta fad'a kanta sunkuye.
"Barka, dai kun tashi lafiya?
Ya fad'a babu yabo babu fallasa.
"Lpia lau.
"To madallah"
ya fad'a yana shirin cigaba da tafiya.
Ahankali tace "Abba, don Allah kayi hak'uri kaji"
Ya d'anyi murmushi.
"Hmm, yaya kenan kinyi laifi ne?.. Ba kina ganin abinda kika yi dai dai ba ne koh?
Cikin raunin murya tace.
"Wallahi Abba ba haka bane, don Allah kayi hak'uri."
Ya juyo, ahankali ya kalleta sosai, sannan ya dawo ya zauna.
"To Me yasa kikayi haka?
"Babu komai"
" Um, dama na nunawa mama fa wayar"
"Tambayar ki nayi me yasa kikayi haka?
"Um babu komai"
" To a ina kika sanshi?
Anan ta d'an fad'a mishi yadda suka had'u da Yusuf d'in.
Da yadda ya bata waya.
Amma bata fad'a mishi sun tab'a had'uwa a wani waje ba, sai ma ta nuna ranar da suka had'u gidan Hajiyah shine ganinta na biyu ita da shi.
Abban ya d'anyi shiru sannan, fara mata magana cikin nasiha, don ya fahimci ita take buk'ata.
"Hafsah ke har yanzu yarinya ce, baki san me duniya take ciki ba.
Ba wai ina hanaki yin wasu abubuwa bane da nufin k'untata miki..Kin manta ni mahaifinki ne?.. Ki daina tunanin zanyi wani abu da niyyar takura miki kinji?
Ta gyad'a kai kawai.
"Ya cigaba.
"Idan kina son abu ki dinga tambayata ko menene shi, kinji yaya? Da kin fad'a min kina son waya da tuni na sai miki..
"Ina son kiyi karatune kinji.. Ko kin fi son in miki aure yanzu?
Tayi saurin girgiza kai.
"To, ki maida hankali kan karatunki kawai, in sha Allah zaki sami mijin da zakiyi alfahari da shi.
Ya mik'a mata wayarshi.
"Ungo saka min number shi.
Hannunta na rawa ta karb'a. Ita dai tana tsoron kada Abba, ya kira Yusuf.
Ta rubuta, ta mik'a mishi.
"Yauwa, yaya."
"Allah yai miki albarka.
Ahankali ta amsa da "Amin"
Ya mik'e.
"Maza ta shi kije kiyi shirin makaranta,nima yau da wuri zan fita.
"Abba a dawo lafiya"
Allah yasa.
Ya fad'a yana fita daga cikin falon.
Daya zo fita ta babban palour, yaran nata hayaniyar shirin Makaranta.
Chapter 16 · 0% Book details