Sashe 60
Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Ya samu ya ci abincin da tea d'in sosai, sannan ya mike yayi sallar isha'i, ya dan jima a zaune yana jan tasbaha, sannan ya d'akko maganin shi yasha.
Wayar shi nacan gefe tana chaji amma jin kiwuyar dakkota yake yi. Sau biyu yaji kira na shigowa amma kuma bai son tashi bare ya d'akko.
'Wasa wasa Ciwon ya dauke shi kwana biyu, har sai da Hajiya ta matsa aka rakashi asibiti, an mishi 'yan gwaje- gwaje, babu komai, sunfi ta,allak'a hakan, da yawan ayyuka, da yakeyi babu hutu.'
Yad'an sami sauk'i babu laifi, abokan shi sun zo dubiya, ranar ne ma yaji ya k'ara warwarewa.'
Duk kwanakin nan kusan hud'u sam bai kira Hafsah ba, a ganinshi, gwara ya bari sai ya sami sauk'i sannan ya kirata, duk da cewa yasha kewarta sosai da sosai.'
__________________
Itama nata b'angaren tayi mamaki sosai, tunane-tunane dayawa sunzo, cikin ranta ciki kuwa har da fargabar "Shin mai ya jawo shirun nashi haka.."?
Amma cikin k'arfin hali irin nata take ta kokawar, kawar da tunanin, ita ala tilas, bata son ace, abinda takeji game dashi _'Kewar shi ce.'_
Ganin an d'ebi kwanaki haka, yasa har ta fara wani tunani, 'wai ko ta gwada kiranshi ne."?
Nan da nan tayi saurin kawar da wannan tunanin, _yaushe suka dad'e..? Yaushe sukayi sabon da har zata damu haka."?_ Sai taji takaicin hakan ma.
Ak'ok'arin tayi watsi da tunanin nashi ne, yasa ta d`akko wayarta, ta kunna Data, facebook ta fara dubawa inda taci karo da wani abin mamaki... Sunan Yusuf ta gani wai ya turo mata _'friend request.'_
Taji abin wani iri, meye hadin biri da gada kuma."? Kodai bai san ita bace? Kai ya sani.. Yasan sunanta sarai, kamar tayi delete d'in request d'in sai kuma ta fasa, ta fita daga facebook din gaba-d'aya ma.
Bata wani dami ranta da tunanin shi ba, saboda bata da wani damuwa akanshi sam, ta dai san yanzu baya k'asar, don labari baya b'uya, har labarin Basma tana dashi, duk da cewa ba bibiyar rayuwar su take yi ba, amma hakan baya rasa nasaba da yadda har yanzu suna tare da wasu daga cikin 'yan makarantar su ana zumunci.'
Aisha Daheer tayi aure wata biyar kenan da bikin, dama yawancin zantuka a wajenta Hafsah keji.
Duk da ba d'auka take yi ba, takan watsar da zancen ne a inda tajishi, domin ita a yanzu ta kama wani layi daban na rayuwar ta, _kowa tasa ta fishsheshi._
bata da wani abin buk'ata daga garesu ( _Yusuf da b
Basma_ ) dukansu...
__________________
"Hello.!!
Hello, Barkanka da yamma
Barka dai
" I hope you're fine naji kwana biyu baka picking call."
Ya d'anyi ajiyar zuciya, wato ita dai bata tab'a watsar dashi, duk da yanzu ta k'arfi da yaji ya canja mata ra,ayi akanshi, amma har yanzu sabon nan nata na kiranshi yana nan har yanzu.
"Hmm, Bahijja kenan, bana jin dad'i ne kwana biyu."
"Subhanallah meya sameka.?
"Ciwon kai nake fama dashi amma naji sauk'i sosai ma."
Ta d'anyi ajiyar zuciya ahankali,
"Allah ya k'ara lafiya sannu fa."
"Yawwa thank you."
Suka d'anyi shiru, can tace, "ko inzo dubiya ne."?
"No naji sauki fa nagode ba sai kin zo ba."
"Hmm, kai dai kawai baka son nazo ne."
"No ba haka bane."
"Hmm, tayi murmushi kawai."
"Okey shikenan Allah ya k'ara sauk'i."
"Amiin k'anwata."
Ita abin ma dariya ya bata duk da gefe guda tana tausayawa kanta, amma sai taji tayi dariya kawai, ya ta iya da kaddara."?
Shima dariyar ta danji yayi,
"Sai anjimanka."
"Okey thank you."
Kiran nashi da tayi, ya k'ara sashi jin kewar Hafsah, sosai, ya kalli agogo, yanzu ne daidai lokacin da takeyin program d'innan a television, ya mik'e a hankali ya nufi falon Hajiya, cikin d'an mamaki Hajiya ta kalleshi, ya nemi guri ya zauna, sai dai abin taikaici ba tashar suke kallo ba, ya dai daure ya zauna, har zaman ya gundure shi, ya tashi kawai zai fita sai kuma yaga Hajiyar ta dauki remote ta canja tashar zuwa can d'in.
Sai kawai ya dawo ya zauna, nan ma Hajiya ta bishi da kallo kawai.
"Ya jikin naka?"
"Da sauk'i."
Kasha maganin yau."?
Idon shi kan TV yace "Eh Hajiya."
Allah ya k'ara sauki."
"Amiin."
Ba,a fi minti 15 ba, aka gama shirin, yaji dad'in kallon aranshi sai yaji an sauke mishi wani nauyi daga kanshi.
Ya dan zauna kad'an, sannan ya mik'e ya wuce d'akinshi.
'Sai dare sannan yayi tunanin kiranta.'
Tana falo ita da kowa na gidan kiran nashi ya shigo, mufida ce ta miko mata wayar, ta kalli sunan daya bayyana, sai taji sanyi aranta, gefe kuma ya haddasa mata fad'uwar gaba, ko meye dalili oho.
Tana jin kunyar a kirata ta mike tabar su a parlour ta wuce d'aki, ciki kuwa ga abbansu da Mama, amma tasan ita da kanta tafi samun nutsuwa, idan ta keb'e tana waya, ko da wanene takeyin wayar kuwa.
Ganin wayar zata tsinke ne, yasa ta d'aga tare da mik'ewa tayi hanyar bed room d'inta.
📝
*HAJEEYAH*
*KHAREEMERH.*
♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so*
*(Guba ne)*
💔💔
*By:*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah khareemerh )*
*Dedicated to Unique in your love heart group members.*
📄 *50*
*"Hello"*
Taji yace.
"Hello"
Ta mayar mishi.
Ta taka da sauri tashige bedroom din ta zauna gefen gado.
"Kina lpia."?
Lpia lau,
Kwana biyu kinjini shiru koh.."?
Bata san amsar da zata bashi ba don haka tayi shiru.
"Uhum."?
Yace da ita.
"Um."
Tace dashi.
"Hhum"
Yayi ajiyar zuciya, ya kwantar da murya.
"Hafsah."
Taji kiran ya ratsata, amma sai bata amsa ba.
Shima badon ta amsa din ya kirata ba don haka yacigaba da magana bayan d'an shiru da yayi, cikin nutsuwar murya yace,
"Baki nemeni ba kuma koh."?
Sai taji 'yar kunya, har ta fara k'ok'arin kama kanta da laifi.
"Um um."
Tace mishi,
"Hmm yayi murmushi mai sauti,
"Um um kikace."?
Sai tayi saurin kama kanta, kada fa yaga zak'ewarta.
Ya cigaba da cewa, "Bani da lafiya ne!"
Sai taji gabanta ya fad'i.
Takuma jiyo shi yana maimaita,
"Rashin lafiya nayi Hafsah, wajen _5days_ ina ciwonkai."
"Ya salam." Taji bakinta ya furta ahankali.
"Sannu"
Cikin murmushi yace, "Yawwa naji sauk'i alhamdulillah."
"Allah ya k'ara sauki."
"Amiin"
Yace cike da jindad'in yadda ta nuna kulawa.'
Ya danyi shiru sannan yace,
"Ai na ganki kina program d'inki a TV."
Murmushi kawai tayi.'
"Bani da lafiya amma sai da na fito na kalla."
Ta k'ara yin murmushin daya ji dad'inshi sosai cikin kunnuwanshi, har ya furta babu shiri.
"I Miss you!
Jin kalmar tayi bazato, ahankali ta sauke ajiyar zuciya, tare da zamewa ta kwanta.
"Kinji,"?
Yace da ita.
"Uhum"?
Tace, cike da jin nauyin shi.
"Hmm, cewa nayi "I miss you, I miss ur voice.!!
Lumshe idanunta tayi, sannan ahankali ta bud'e, daidai lokacin da yakecewa,
"Kinji me nace yanzu."
"Um."
Tace,
"Okey thank you."
yace.'
Ta rasa dalilin godiyar amma taji d'ad'inshi da zata ce mishi, ~_"For what."?_~
Sai kuma tayi shiru.'
"Ina son inzo wajenki, idan zan samu."
Sai taji gabanta ya fad'i.
Na sami sauk'i, naji kawai inason zuwa inganki, kinga da na mutu a rashin lafiyar nan shikenan koh.?
Shiru taji kawai, ta daiji jikinta ya d'anyi sanyi.
"Idan zaki bani dama _Friday_ nazo."?
Tayi shiru tana tuno yaushene ma _Friday_ d'in.
"Uhum"? "ko baki shirya ganina ba."?
Tayi shiru.
Okey ki bani lokaci, duk sanda kika shirya kinji."
"Okey tace mishi."
"Kada na dameki koh."?
"Goodnight!!
"Bye bye."
Tace.
"Okey..
Ya kashe wayar yayin da itama ta janye wayar daga kunne.
Bata motsa daga inda take ba har zuwa mintuna, tana mamakin yadda take jinta kamar bata tab'a waya da namiji ba, idan tana waya dashi, meyasa haka oho."?
Mamakin yanayin da take shiga take, da kuma yadda take, amsa wayarshi da irin biye mishin da takeyi..
Wayar shi nacan gefe tana chaji amma jin kiwuyar dakkota yake yi. Sau biyu yaji kira na shigowa amma kuma bai son tashi bare ya d'akko.
'Wasa wasa Ciwon ya dauke shi kwana biyu, har sai da Hajiya ta matsa aka rakashi asibiti, an mishi 'yan gwaje- gwaje, babu komai, sunfi ta,allak'a hakan, da yawan ayyuka, da yakeyi babu hutu.'
Yad'an sami sauk'i babu laifi, abokan shi sun zo dubiya, ranar ne ma yaji ya k'ara warwarewa.'
Duk kwanakin nan kusan hud'u sam bai kira Hafsah ba, a ganinshi, gwara ya bari sai ya sami sauk'i sannan ya kirata, duk da cewa yasha kewarta sosai da sosai.'
__________________
Itama nata b'angaren tayi mamaki sosai, tunane-tunane dayawa sunzo, cikin ranta ciki kuwa har da fargabar "Shin mai ya jawo shirun nashi haka.."?
Amma cikin k'arfin hali irin nata take ta kokawar, kawar da tunanin, ita ala tilas, bata son ace, abinda takeji game dashi _'Kewar shi ce.'_
Ganin an d'ebi kwanaki haka, yasa har ta fara wani tunani, 'wai ko ta gwada kiranshi ne."?
Nan da nan tayi saurin kawar da wannan tunanin, _yaushe suka dad'e..? Yaushe sukayi sabon da har zata damu haka."?_ Sai taji takaicin hakan ma.
Ak'ok'arin tayi watsi da tunanin nashi ne, yasa ta d`akko wayarta, ta kunna Data, facebook ta fara dubawa inda taci karo da wani abin mamaki... Sunan Yusuf ta gani wai ya turo mata _'friend request.'_
Taji abin wani iri, meye hadin biri da gada kuma."? Kodai bai san ita bace? Kai ya sani.. Yasan sunanta sarai, kamar tayi delete d'in request d'in sai kuma ta fasa, ta fita daga facebook din gaba-d'aya ma.
Bata wani dami ranta da tunanin shi ba, saboda bata da wani damuwa akanshi sam, ta dai san yanzu baya k'asar, don labari baya b'uya, har labarin Basma tana dashi, duk da cewa ba bibiyar rayuwar su take yi ba, amma hakan baya rasa nasaba da yadda har yanzu suna tare da wasu daga cikin 'yan makarantar su ana zumunci.'
Aisha Daheer tayi aure wata biyar kenan da bikin, dama yawancin zantuka a wajenta Hafsah keji.
Duk da ba d'auka take yi ba, takan watsar da zancen ne a inda tajishi, domin ita a yanzu ta kama wani layi daban na rayuwar ta, _kowa tasa ta fishsheshi._
bata da wani abin buk'ata daga garesu ( _Yusuf da b
Basma_ ) dukansu...
__________________
"Hello.!!
Hello, Barkanka da yamma
Barka dai
" I hope you're fine naji kwana biyu baka picking call."
Ya d'anyi ajiyar zuciya, wato ita dai bata tab'a watsar dashi, duk da yanzu ta k'arfi da yaji ya canja mata ra,ayi akanshi, amma har yanzu sabon nan nata na kiranshi yana nan har yanzu.
"Hmm, Bahijja kenan, bana jin dad'i ne kwana biyu."
"Subhanallah meya sameka.?
"Ciwon kai nake fama dashi amma naji sauk'i sosai ma."
Ta d'anyi ajiyar zuciya ahankali,
"Allah ya k'ara lafiya sannu fa."
"Yawwa thank you."
Suka d'anyi shiru, can tace, "ko inzo dubiya ne."?
"No naji sauki fa nagode ba sai kin zo ba."
"Hmm, kai dai kawai baka son nazo ne."
"No ba haka bane."
"Hmm, tayi murmushi kawai."
"Okey shikenan Allah ya k'ara sauk'i."
"Amiin k'anwata."
Ita abin ma dariya ya bata duk da gefe guda tana tausayawa kanta, amma sai taji tayi dariya kawai, ya ta iya da kaddara."?
Shima dariyar ta danji yayi,
"Sai anjimanka."
"Okey thank you."
Kiran nashi da tayi, ya k'ara sashi jin kewar Hafsah, sosai, ya kalli agogo, yanzu ne daidai lokacin da takeyin program d'innan a television, ya mik'e a hankali ya nufi falon Hajiya, cikin d'an mamaki Hajiya ta kalleshi, ya nemi guri ya zauna, sai dai abin taikaici ba tashar suke kallo ba, ya dai daure ya zauna, har zaman ya gundure shi, ya tashi kawai zai fita sai kuma yaga Hajiyar ta dauki remote ta canja tashar zuwa can d'in.
Sai kawai ya dawo ya zauna, nan ma Hajiya ta bishi da kallo kawai.
"Ya jikin naka?"
"Da sauk'i."
Kasha maganin yau."?
Idon shi kan TV yace "Eh Hajiya."
Allah ya k'ara sauki."
"Amiin."
Ba,a fi minti 15 ba, aka gama shirin, yaji dad'in kallon aranshi sai yaji an sauke mishi wani nauyi daga kanshi.
Ya dan zauna kad'an, sannan ya mik'e ya wuce d'akinshi.
'Sai dare sannan yayi tunanin kiranta.'
Tana falo ita da kowa na gidan kiran nashi ya shigo, mufida ce ta miko mata wayar, ta kalli sunan daya bayyana, sai taji sanyi aranta, gefe kuma ya haddasa mata fad'uwar gaba, ko meye dalili oho.
Tana jin kunyar a kirata ta mike tabar su a parlour ta wuce d'aki, ciki kuwa ga abbansu da Mama, amma tasan ita da kanta tafi samun nutsuwa, idan ta keb'e tana waya, ko da wanene takeyin wayar kuwa.
Ganin wayar zata tsinke ne, yasa ta d'aga tare da mik'ewa tayi hanyar bed room d'inta.
📝
*HAJEEYAH*
*KHAREEMERH.*
♥️♥️♥️♥️
*ZAZZAFAN SO*
(masoyin k'warai)
*Cigaban littafin Zazzafan so*
*(Guba ne)*
💔💔
*By:*
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah khareemerh )*
*Dedicated to Unique in your love heart group members.*
📄 *50*
*"Hello"*
Taji yace.
"Hello"
Ta mayar mishi.
Ta taka da sauri tashige bedroom din ta zauna gefen gado.
"Kina lpia."?
Lpia lau,
Kwana biyu kinjini shiru koh.."?
Bata san amsar da zata bashi ba don haka tayi shiru.
"Uhum."?
Yace da ita.
"Um."
Tace dashi.
"Hhum"
Yayi ajiyar zuciya, ya kwantar da murya.
"Hafsah."
Taji kiran ya ratsata, amma sai bata amsa ba.
Shima badon ta amsa din ya kirata ba don haka yacigaba da magana bayan d'an shiru da yayi, cikin nutsuwar murya yace,
"Baki nemeni ba kuma koh."?
Sai taji 'yar kunya, har ta fara k'ok'arin kama kanta da laifi.
"Um um."
Tace mishi,
"Hmm yayi murmushi mai sauti,
"Um um kikace."?
Sai tayi saurin kama kanta, kada fa yaga zak'ewarta.
Ya cigaba da cewa, "Bani da lafiya ne!"
Sai taji gabanta ya fad'i.
Takuma jiyo shi yana maimaita,
"Rashin lafiya nayi Hafsah, wajen _5days_ ina ciwonkai."
"Ya salam." Taji bakinta ya furta ahankali.
"Sannu"
Cikin murmushi yace, "Yawwa naji sauk'i alhamdulillah."
"Allah ya k'ara sauki."
"Amiin"
Yace cike da jindad'in yadda ta nuna kulawa.'
Ya danyi shiru sannan yace,
"Ai na ganki kina program d'inki a TV."
Murmushi kawai tayi.'
"Bani da lafiya amma sai da na fito na kalla."
Ta k'ara yin murmushin daya ji dad'inshi sosai cikin kunnuwanshi, har ya furta babu shiri.
"I Miss you!
Jin kalmar tayi bazato, ahankali ta sauke ajiyar zuciya, tare da zamewa ta kwanta.
"Kinji,"?
Yace da ita.
"Uhum"?
Tace, cike da jin nauyin shi.
"Hmm, cewa nayi "I miss you, I miss ur voice.!!
Lumshe idanunta tayi, sannan ahankali ta bud'e, daidai lokacin da yakecewa,
"Kinji me nace yanzu."
"Um."
Tace,
"Okey thank you."
yace.'
Ta rasa dalilin godiyar amma taji d'ad'inshi da zata ce mishi, ~_"For what."?_~
Sai kuma tayi shiru.'
"Ina son inzo wajenki, idan zan samu."
Sai taji gabanta ya fad'i.
Na sami sauk'i, naji kawai inason zuwa inganki, kinga da na mutu a rashin lafiyar nan shikenan koh.?
Shiru taji kawai, ta daiji jikinta ya d'anyi sanyi.
"Idan zaki bani dama _Friday_ nazo."?
Tayi shiru tana tuno yaushene ma _Friday_ d'in.
"Uhum"? "ko baki shirya ganina ba."?
Tayi shiru.
Okey ki bani lokaci, duk sanda kika shirya kinji."
"Okey tace mishi."
"Kada na dameki koh."?
"Goodnight!!
"Bye bye."
Tace.
"Okey..
Ya kashe wayar yayin da itama ta janye wayar daga kunne.
Bata motsa daga inda take ba har zuwa mintuna, tana mamakin yadda take jinta kamar bata tab'a waya da namiji ba, idan tana waya dashi, meyasa haka oho."?
Mamakin yanayin da take shiga take, da kuma yadda take, amsa wayarshi da irin biye mishin da takeyi..