← Book details Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 69 OF 88

Sashe 69

Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sai ta bige da kunna Data, kai tsaye ta shiga wajen sunanshi. Taga rabon da suyi hira, tun randa ya roketa zaizo wajenta, asama taga _last seen_ dinshi k'arfe tun 9:30 na dare.
Nan ma zatayi mishi magana sai kuma ta fasa.

Ta duba profile d'inshi babu komai ma akai ya cire, takaici ya kamata dama bata taba ganin yasa photonshi ba kamar yadda itama bata sawa kodan mutane.

Ganin tana bata lokutan ta, akan bibiyarshi da tunaninshi yasa ta matse wayar tata ta kashe ta, gaba-d`aya. Sannan ta nutse kanta cikin bargo wai ita dole sai tayi bacci. Dama kuma tana da fita gobe tana da wani aiki da sassafe.
Data rufe idon sai taji tana son tunano kamannin shi, ji tayi ta kasa, amma abin mamaki sai ta shiga yiwa kanta dole, da haka tayi bacci.

______________
Kwance take ta nutsa kanta cikin pillow tana risgar kuka, ji take duk duniya babu wanda ya kaita bak'in ciki. Gashi a yau d`in dai gaba-d`aya wayoyinta abbanta ya karb'e, ta rasa wanne irin abun bakin ciki ya same ta haka, duk wani da zatayi _sharing_ damuwarta yau ita dashi babu hanya, banda takunkumin hana fita da abbanta ya saka mata, sannan ya dad'a da kwace wayoyinta.?
Duk bayan minti sai ta tuno da wasu bakaken kalamai da sukafi komai muni a xuciyarta wato.
_"Basma yau dai Allah yayi ikonshi na bada ke, in sha Allah aurenki saura wata biyu, kiyi hak'uri kiyi min biyayya, ina kyautata zaton banyi miki zaben tumun dare ba.!!_
Ya had'e rai sannan ya mik'a mata hannu.
"Bani wayoyinki duka.!!
"Zan baki amma sai lokacin da aka d'aura miki aure.!!"

Tuno wad'annan kalamai da suke muna na, a kunnenta yasa ta bude baki ta kwalla wata muguwar k'ara, wacce lokaci guda kuma tayi saurin toshe bakinta, tuno cewa abbanta na iya jiyo ta, kuma babu abinda zai hanashi hukuntata, koda kuwa da duka ne, don ta kaishi bango.
A hankali take zubar da hawaye tana wani marayan kuka, tana kiran mamanta. Har muryata ta dashe, amma bata daina ba, sai da ta raba dare, sannan dakyar bacci ya sace ta..

_______________

Yau da wuri, ya tashi, bayan ya dawo daga masallaci, ya wuce d'akin abbansu don ya gaida shi.

_Khaady_ Yana zaune yana jan doguwar tasbaharashi, gefe kuma ga wasu manyan litattafai kusa dashi, sai kuma al'Qurani mai girma. Yau shima yana da wata shari,a da yake saka ran yanke hukunci a yau.

Ukhasha yayi sallama, _khadi_ ya amsa.
Sannan ya shiga gaida shi.
"Abba barka da asuba." Cikin sakin fuska ya amsa.
Barka dai malam, ( _kamar yadda yake kiranshi wani lokacin._) an tashi lafiya?
"Lafiya lau, Akaramakallahu."
"To Masha Allah.

Ukhasha ya k'ara duk'ar da kai sannan yayi magana cikin nutsuwa.

"Abba!! yaya ne yayi min magana akan wani d'an company da zasu bud'e shida abokan shi."
Khady ya bada hankalin yana sauraron shi.
Ukhasha ya cigaba.

"To yace idan ina so nima zan iya saka nawa kud'in."

Khady ya nunfasa sannan ya fara magana, "Eh nasan da zancen, ya fad'a min zasu bud'e companyn sarrafa shinkafa ne koh."?
Ukhashatu ya gyad'a kai, "Eh shine."
"Yayi kyau hakan, nawa zaka saka aciki kai."? Cewar Khady yana kallon Ukhashatu.
Cikin ladabi Ukhasha yace, "Shine nake so a bani shawara Abba."

Khady yayi yar dariya, sannan yace, _malam_ kenan, "To ai shawara na wajenka, kai kasan nawa zaka iya sawa."

Ukhasha ya d'anyi murmushi, ya sosa kai.

Cikin Hikima Khady yace, "To komai dai za,ayi ayi daidai misali dai, yadda ba za,a takura ba, idan Allah ya sawa abin albarka sai kuga yana ta hab'aka."

Ukhashatu ya jinjina kai.
"Shi nawa yace ka kawo."? Khady ya tambaya.
"Bai kayyade min ba, amma ya bani shawara.
Yace ka saka nawa.
"Million hud'u." Ukhasha ya fad'a yana sunkuyar dakai.
Khady yayi dariya me d'an tsaho.

"Kana da million hud'u Ukhashatu."?
Ukhashatu ya hau shafa kai.
Khady ya cigaba da magana.
"Amma baka fara ginin ka ba koh."?

Ukhasha yayi tsit, saboda anzo wajen.

Khady ya takaita zancen da cewa, "Ka saka million uku kaga babu takura koh, tunda shima million shidda ya bada."

"Nagode, Abba Allah ya k'ara girma."
Ya shiga godiya kamar wanda akayi wa kyauta.

Sannan cikin nutsuwa Khady ya kira sunanshi. "Ukhashatu!!
Ya amsa a sanyaye.
"Na,am Abba."
Khady bai jira komai ba ya fara maganar da zaiyi.
"Basai an fad'amin ba, nasan kana da isassun kud'in da zaka fara gini, idan aure ya zo maka ma kuma kayi shi, hakane koh."?

_Yana sane ya maida zancen salon tambaya._

Cikin sanyi Ukhasha ya hau gyad'a kai.

"To ka samu ka fara gininka cikin watan nan. Abba ya fad'a yana d`auke murmushin fuskar shi don Ukhasha ya san bada wasa yake mishi ba.

Cikin ladabi ya shiga d'aga kai, zanyi Abba in sha Allah, a taya mu da addu,a."

"Addu,a ai kullum cikin yi muku ita ake Ukhasha kuma in sha Allah, Allah yana amsawa."

Ukhasha, ya motsa kamar zai mik'e don yin sallama da Abba ya tafi, yaji Abban na wata magana.

"Kaji yau in sha Allah, masu kawo lefen maryam zasu zo koh, kuma za,ayi bikin cikin sati uku"

"Allah ya sanya alkhairi Abba. Inji Ukhashatu.

Amiin ya allah, Khady ya fad'a yana k'ara kallon Ukhasha kamar zai mishi magana, sai kuma bai ce komai ba. Shi kanshi Ukhasha a tsarge yake, Allah-Allah kawai yake a sallame shi ya tafi.

Sai kuma ya tsinkayi abban nacewa, "Yau baka je daukar karatun ba ne."? ( _yana nufin makarantar manya da Ukhasha yake zuwa da asuba, a wani masallaci kusa da su_)
Yayi murmushin jin dad'i, don bai zaci haka abban zaice mishi ba.
Eh Abba, yau ana idar da sallah gida na yo, saboda inason zan fita da wuri.
"Khady ya gyada kai, amma gashi ka b'ata lokaci anan.

Ukhashatu yayi yar dariya, "Aa, Abba, dama inason ganawa da kai d`in.
To yayi kyau tashi maza kada a makara.
Ukhasha ya mik'e.
Nagode Abba a huta lafiya.
Khady yayi murmushi yana bin shi da kallo.

_____________
Fitowar ta daga wanka, kenan tana goge jikinta da towel, wayarta ta shiga yin d'an kida.
Batayi mamaki ba don tayi zaton abokan aiki ke neman ta.

Tayi saurin k'arasawa inda wayar take don dubawa ta d'aga.

Wata iriyar faduwa gaba taji, wacce sai da ta d'an had'a da da fe k'irjinta.
Cikin mamaki tayi saurin d'agawa zuciyarta tana cewa, lafiya kuma kiranshi da sassafe."?
Cikin sanyin murya tayi sallama, sai kuma taji shi muryarshi ras ya amsa mata.
Hakan yasa taji babu wata ragowar damuwa a tattare da ita.
Ranki ya dad'e Barka da safiya, Allah yasa dai bani na tasheki ba da safenan.
Ya fada da nutsuwar murya kamar ko yaushe, wanda tunda ya fara magana take murmushin boye, na jin dad`in muryarshi.
Uhum."?
Taji yace, ta kalli kanta, daga ita sai towel, sai taji tana jin kunya gani takeyi kamar zai gano ta.

Tayi murmushi mai sauti, dayaji shi sosai har cikin jininshi.

Ga mamakinshi sai yaji tace, ka tashi lafiya."?
Ta gano farinciki tsababa cikin muryarshi sanda yake amsa mata.
"Lafiya lau _my queen,_ ai da tunaninki na tashi.
Tayi murmushi itama.
Jiya bamuyi waya ba, ji nake kamar mun shekara."
Itama a zuciyarta haka ne amma bata furta komai ba sai murmushi.

Cikin rage sauti yace mata, I miss you dear, you do miss me too."?
Ya fad'a kamar rad'a.
Babu wani tunani ko bata lokaci taji bakinta ya furta _"yeah!!."_
Ukhasha tsaye yake, amma babu shiri ya zauna, a gefen gado.

Really."? Yace mata cikin taushin murya.
Ta toshe bakinta, tana yar dariya, tuno abinda bakinta ya fad'a.

"I have to go to work earlier today, ina son in shirya."
Ta fa ke da fadar haka.
"Dariya, yayi mata shima, yasan dalilinta na fad'ar haka, "me too."
Yace mata, kinga nima shiri nake, amma ina son inji ki..
"bazan iya aiki ba idan banji muryarki ki da safen nan ba."
Tayi murmushin jin dad`in kalaman shi.
Lokaci d'aya kuma taji yace, kada na tsaida ke koh, bye."

Itama "OK bye" tace mishi.
Ya k'ara mata da "I love you."
To fa anzo wajen sai tayi tsit kamar babu ita.
A hankali taji yace mata, "Kinji."?
"Um." tace mishi.
Cikin marairaice murya ya ce, to ni me zaki ce min."?
Tayi shuru tana tunanowa, wato yau dai k'ure ta zaiyi.
Uhum."?
Ya k'ara tambayar ta.
"Thank you!! tace mishi.
Yayi kamar baiji ta ba, ya d'ora da.
"please Say you love me too, please Hafsah.!!
Ta nemi guri itama babu shiri ta zauna jin yanayin muryarshi.
"Please!! taji ya k'ara fad'a.

Nan ma shuru tayi,
please Hafsah ki taimake ni!! Ya fad'a murya can k'asa sosai.
(Kiran sunanta da yake ba k'aramin tasiri yake ba.)

"Nan ta shiga tunani akan ta fad'a ko kada ta fad'a."?

Cikin sanyi ta juyo shi, yana cewa "Okey can't you."?
Bata son su kuma maimaita irin na rannan, don haka da sauri wanda shima babu zatonshi yaji tace, _"me too."!!_

a k'age yace, "You too what.."?
Hmm, tace.
"Ki daina min rowa don Allah wallah kina wahalar dani.!!

Tayi jim na wasu muntuna tana hasashe.

ta jiyo shi yana cewa, idan nine bazan kasa fad'a miki ina sonki ba, wallah I love you with all my heart Hafsah.

Da alama zancen zuci yake, ta fahimci wasu abubuwan suna zuwa bikinshi ne batare da niyyar shi tayin hakan ba, haka kuwa na nuni da zallar soyayyarta ne cikin zuciyarshi.

murya na d'an karkarwa tace don ta huta itama, _ilove you too.!!_

Zo ki ga farin ciki gurin ukhasha, har sai da ya zame ya kwanta.
Yana rik'e da wayar amma yayi shuru.
Itama wani iri take ji, har wani zif-zif take ji a jikinta.
_Anya kuwa tayi wa kanta daidai.?_

Sai da ya gama saita kanshi sannan ya sauke wata ajiyar zuciya a hankali yace, "Nagode, "Nagode Hafsah, in sha Allah by time zaki fahimci irin son da nake miki, kuma in sha Allah bazan taba baki kunya ba, zakiyi farin ciki dani.
Thank you.!!
Ita dai bata da bakin magana, ya san ba zatayi d`in ba, don haka yace..
"Hafsah.! A hankali.
Ta kasa amsawa don bata son ya k'ara jin muryarta a lokacin saboda kunyarshi.
Chapter 69 · 0% Book details