← Book details Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 88

Sashe 27

Zazzafan So Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Maman tayi dariya, sannan fara yi musu, ta tsuniyar "Na goma" duk sun nutsu suna sauraronta, har da Hafsan itama, sai da ta gama, Abba yace Hafsah tayi musu, tayi d'an murmushin kan leb'e, sannan tace, "Abba bashir yayi mana, ni sai na tuno wacce zanyi"
'Dukansu suka hau yi mata dariya, suna tsokanarta wai ta kasa.'
'Ita kuwa d'adi taji don sam batajin yin magana mai tsawo ko sauraron wani dogon zance a lokacin, sai da suka gama lokacin kuma baifi k'arfe takwas ba sannan Abba ya kunna musu 'Solar' kasancewar babu wuta, sannan suka saka wani tsohon film d'in ',(Home alone') suna kalla cikin nishad'i, hakan yasa hafsah taji d'adi sosai ta mik'e, 'Abba ya bita da kallo, sai ta kawo mishi uzurin cewa bacci take ji'
'Ya jinjina kai, sannan yace "Shikenan, kiyi addu,a," ya Kalli mama, ita ma ta kalleshi, itama ta karanta mishi nata mamakin', Na baccin da hafsah tace tanaji, a irin lokacin k'arfe takwas baifi da rabi ba'.. 'Abinda yaran sai k'arfe tara da rabi ko goma suke bacci, shima sai Abban ya kora su, saboda makaranta.'
'Hafsa ta kwanta shiru, ta takurawa zuciyarta kan dole sai ta gano, abin da ke tsakanin Yusuf da Basma.. Da har ya sashi kafewa kan zuwa birthday d'in don kada ran Basma ya b'aci.' Yadda zuciyarta ta karanta mata kenan..'
'Abubuwa da yawa zuciyarta tayi ta karanto mata wanda ita kuma gefe guda tayi ta k'okarin sai ta k'aryata hakan, don kada ta jawo wa kanta tarwatsewar farin ciki babu shiri'
'Da farko kawai ta sa wa ranta, Basma tace wa Yusuf 'Tana Sonshi ne..
'Sai kuma ta tuna a irin class na basma tana fad'ar cewa ita babu namijin daya isa tace tana sonshi'.. Sai ta sauya tunanin da cewa ' kodai kawai son kula maza ne da iyayi irin na basma yake jan hankalin Yusuf d'in zuwa ga kulata, ??
'Kishi ya baibayeta Wani b'angaren kuma na zuciyarta ya shiga rarrashinta, da nuna mata sam fa wannan tunanin ba haka bane, 'Idan ta lura da irin kallon da yusuf yayi wa basma ranar da suka fara had'uwa, sai kuma d'inbin soyyayyarta (ita Hafsan) da ke dank'are cikin zuciyarshi, wacce bata da kokontonta, idan ba lokacin da ta shiga rudu, irin wannan ba'..
'Da taga dai, ta rasa abin kamawa, sai kawai ta bari kalmomin Yusuf sukayi tasiri, itama zuciyar ta ta ta,allak'a abin da, 'Ganin kirkin basma da Yusuf d'in keyi, kamar yadda ya fad'a mata, wanda kuma hakan sanadinta ne ita Hafsan.'..
'Ta saki nannauyar ajiyar zuciya, sai lokacin taji dama-dama, sai kuma ta shiga nemawa zuciyarta hujjar da zata k'ara yarda da hakan.' sai tunaninta yakai kan ranar da yusuf d'in ya turowa Aysha katin 2000' wanda shima fa kawai albarkacinta taci don kawai, suna waya da wayarta.'
'Ahankali taji zuciyarta na hak'ura da lamarin har taji tausayin Yusuf d'in bisa mummunar fahimtar datayi mishi, take taji zuciyarta ta k'ara kamuwa da sonshi, taji kawai babu abinda take son ji sai muryarshi. Amma ina babu dama, hakan yasa ta tsunduma tunanin yadda suka rabu d'azu tana k'ara halarto irin kyan da ga yayi yau d'in...
'Ahakan har tayi bacci'
'Washe garin ranar Yusuf na kwance a d'akinshi da daddare, yaji kira ciki wayarshi, ya duba yaga basma ce, ya d'aga kiran tare da kai wayar kunnanshi. "Hello"
Takai k'arshe wajen kashe muryarta wacce ta yi tasiri sosai a kunnuwanshi tace, "Hi, ya kake"? Am fine" "Ok gud, ya gajiyar birthday yai dariya, "Hah babu gajiya kuke cewa koh"?
'Itama tayi dariya "Oh Na manta fa you're Californian.!" suka k'ara yin dariya, sannan ta mayar da muryarta kalar ta tausayi, kamar mai yin kuka tace, "Yusuf,..
"Na,am." shima ya amsa cikin taushin murya'
'Sai kawai ta saki kuka, hankalinshi ya tashi, ya rud'e ya hau rarrashinta, bai san ma me yake fad'a mata ba.'
"Am sorry baby, kiyi ha'kuri please calm down, ki fad'a
min make faruwa waya tab'a ki ko Hafsah wani abu ya faru"?
Sai da tayi kukan sosai sannan ta saita muryarta cikin shashshek'a ta fara magana, wanda shi yanayin muryar ya d'auki hankalin shi'
"Am na rasa wa zan fad'a wa, damuwata sai kai,.. Cikin nutsuwa yace "Mata ina jinki" tayi ajiyar zuciya sanan ta cigaba,"
'Saurayina ne kawai don kazo birthday kuma yaga yadda kayi treating ena shine yace wai ya rabu dani!! Ta k'arashe maganar cikin kuka"..
Yusuf yayi shiru, yama rasa me zaice, tausayin basma ya rufe shi, cikin in, ina ya faro magana, " Um, d.. Do youu mean kun rabu kenan"??
"Of course".. Ta fad'a tare da k'ara rushewa da kuka..' "Oh my God"!
Yusuf ya fad'a, to Meyasa? A wanne dalilin, wato kishi yake da shi kenan,?? Yama rasa me zaice, sai kawai ya b'ige da rarrashinta "please kiyi ha'kuri, kada ki damu, I know it will hurt, but kiyi ha'kuri in sha Allah zaku sasanta kinji..'
'Zuciyarta ta dugun zuma, ita ba haka tasoji ba, amma sai ta kanne kawai, tace mishi, " I told you mun rabu kuma bana jin zamu k'ara yin wata soyayya ni da shi, so just pray for me 'Allah ya bani wanda ya fishi'
'Ya sauke ajiyar zuciya tare da cewa, "Amin."
Sai kuma ya shiga yi mata 'yar hira, yana kod'a kyan datayi a ranar birthday d'in
Duk a k'okarinshi,
na ganin ya kwantar mata da hankali, domin ji yake, shine sanadin tarwatsewar farincikin ta, ita kuma abin nema ne yasamu, taji dad'in hakan sosai.'
'Da k'yar sukayi sallama.'
'Wai ko anya zancen Basma gaskiya t
ne??
'A gaskiyar zancen dai, shine, basma bata gayyaci manyan samarinta, wad'anda tasan zasu ji haushin ganinta da yusuf ba,..Amma da gaske ne tayi fad'a da wani saurayinta amma shima d'in kawai na rage zafi ne, baza,a kirashi da saurayinta na sosai ba, shine ta fa ke da hakan ta d'ora kukan makircinta akai, buk'atar ta kawai Yusuf ya tausaya mata, tana son tausayinshi yayi tasiri akanta, wanda shine zai zama mabud'in cimma dukkan manufarta, kuma gashi cikin sa,a ta sami hakan.'
'Domin ita tayarda da cewa, tausayi shike jawo soyayya..'!
'Basma ta kwanta har da burgima don murna, tabbas ta juyo k'amshin nasara.'
'Ana cikin haka kira ya shigo cikin wayarta tana dubawa tayi tsaki sanan ta d'aga.
"Hello basma iam Aysha d'aheer"
"Ok, so ya kike"?
"Lafiya lau"
'Suka d'anyi shiru sannan Aysha tace,
"Basma Yunus Manyan gari,"
"Hmm, basman tace cikin rashin kulawa, domin tun ranar birthday d'inta taji ta tsani Ayshan, saboda gani take kamar munafurci ne ya kawota.. Hafsah
ce ta turo ta donta kaimata munafurcin abinda ya faru kawai.'
'Amma dake ance bariki iyawa ne sai, ayshan ta chanja salonta, ta gyara muryarta tace,
'Gaskiya Basma, kin burgeni ranar nan fa, sai ranar na tabbatar H.Hamid jaka ce'
Basma ta shek'e da dariya,
'Aysha ta cigaba, wato in banda hauka irin nata, ko yaushe zaki bari number Saurayinki a wayar k'awayenki?? 'Sannan kuma Kalli yadda don k'auyanci ta ki zuwa birthday d'in ta barshi shi kad'ai yazo, Basma tace "Hmm.'' So take ta gano inda Aysha ta nufa, Don tana tsoron kada dai bugar cikinta takeyi.'.. Amma hankalinta ya kwanta da taji Ayshan tace, "Ni wallahi ma sam gayen bai wani dace da ita ba, bafa type enshi bace."
'Sukayi dariya sosai ita da Basman, har Basman ta samu damar cewa, "Kema dai kya fad'a Aysha'.. "Hmm ai wallahi sam babu colour, yarinyar da babu inda take zuwa!!"
'Anan basma ta saki jiki sukayi hira, sosai da zata fad'awa Ayshan wayar da sukayi da Yusuf d'azu, amma sai ta fasa, suka kashe waya, Basma na farin ciki ta samu wata mai bata shawara akan al,amarin...

🤥 *Sabon salo*

.
*Khareemerh tijjani Mansur (Hajeeyah Kareemerh*
[1/11, 12:09 AM] Hajeeyah Karimah (Writer): ♥♥♥♥
*ZAZZAFAN SO*
(Guba ne)
*A broken*
*heart story*
💔💔

Story and writing by:
*Karima Tijjani Mansur*
*(Hajeeyah Kareemerh)*
*Dedicated to: Unique In Love Heart Members*

📄 *30*
Chapter 27 · 0% Book details