← Book details Ragon Miji Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 85 OF 130

Sashe 85

Ragon Miji Complete Hausa Novel · about 8 min read

Musa yace "hakika wannan ba abun mamaki bane don ikon Allah yawuce mamaki azamanin manzon Allah (S. A. W) wata unguwa takama da wuta duk gidajen suka kone daakazo akafada ma sahabin daya daga cikin mutanen unguwar se ya karyata yace wlh banda gidana saboda bana fitowa gida harse nayi adduar da manzo ya koyar damu (fans namanta adduar) kuma ana zuwa akaga gidanshi lpya lau amma duk nakusa dashi akone,"

Ya cigaba da cewa" nan kusa akwai wani abokin mahaifina shide yakasance kullum baya manta karanta ayoyin karshen suratul tauba, lakadjaakum sau 7 koda yana tafiya yakan karanta ta koda besamu yin kowane azkhar ba yanayin wannan, se wani amininshi ya kawo mashi ziyara daga sudan shikuma abokin mahaifin nawa yana zaune a kaduna, bayan ya kwana se suka shirya suka nufi abuja don ziyarar abukkansu, tareda driver suke amma se abokin mahaifina yaamshi driving, kasancewar beiya dogon driving yake fara bacci suna cikin tafiya yafara gyangyadi dole yadawo gidan baya ya kwanta amininshi da driver suna gaba, baadade ba bacci ya daukeshi,yana bacci sukai accident koda yafarka sede yaganshi yashe a gefen titi mutane suna zagaye dashi bako kwarzane jikinshi, seyafada musu suna tare da yanuwanshi a mota, daaka bi daji ashe motar yankar daji tai taita tafiya tayi raga raga driver ya mutu yana ciki yayi jina jina, hankalinshi yatashi aka dukufa neman amininshi baagano amininshi ba se da akai tafiyar kilometers 25 sannan akaganshi kwance a mace cikin kungurmin daji, ya kidima sosai abun yabawa mutane mamaki, a kd akai janaizar amininshi da driver ana zaman gaisuwa wanda ina daga cikin wadanda ke gun anata jajanta lamarin sewani malami yake tambayar shi wace addua yayi ayau seyace "wlh ban karanta komi ba se lakadjaakum kafa 7 wanda kuma a riyadul janna nasamu falalarta hadisin da yakawota a rauda ta 18 ankarbo hadisin ne daga Muhammad bn abubakar cewa wanda ya lazimci karanta lakadjaakum ila akirul sura lam ya mut hadman wala garqan wala harkan wala darban hadid,shine na lazimceta kowane lokaci "

,malamin yace"hakika karshen suratul tauba kariya ce daga dukkan abun ki, nima zankara dukufa wurin yinta "

Musa ya cigaba dacewa daganan sena rike ta inayi danaji falalarta ,ban wata biyu da riketa ba zanje Lagos motar mu ta kife karamar macapolo ce amma bawanda ya fita seni nima cikin jini nake domin naji ciwo sosai "ya bude kafarshi zuwa bakin gwiwa wani katon tabo ya bayyana harda rami ajiki yace "kaga tabon da yakasa bacewa daga cikin tabunnan danayi a kalla anyi shekara biyar amma har yanzu be cike ba sede ina tafiya da kafata lpy lau duk dan temakon Allah "(it's true life story ya faru dagaske)

khalil yace"ina yawan karantata domin tana daga cikin jerin azkhar dake cikin littafi na sede bansan falalarta ba, hakika nagode ma Allah daya kareni domin koda mutuwa hutuce aguna zanso nakara rayuwa dan nakara aikata aikin alheri ,inada mahaifiya ita kadai ta ragemin inason na rayu har zuwa tsufanta zuwa lokacin da zata kasa yiwa kanta komi yazama nine me mata hidima don samun rahmar ubangiji da albarkarta dafatan Allah yabani wanda zemin haka nima"

musa yace "Allah ya yarda wane gari kake zan temaka maka nakaika duk da dare yayi "

khalil yace "cikin katsina nake idan har zaka temaka mun ba gida nakeso kakaini ba, don ina samun matsala da matata da mahaifiyata nasan in sukaji labarin mutuwa ta zasu saduda mahaifiyata zata sauko domin tana sona sonda takemin ne yayi yawa haryake kawo mana matsala take kishi da matata kamar kishiyarta, inso samu ne zanso na zama bakonka nawani lokaci sannan zan koma garinmu "

Musa yace "ba matsala nima zanso nasamu ladar bakuntarka, na tausaya maka Allah ya ganar da mahaifiyarka"

Khalil yace "amin nagode Allah ya baka ladar "

musa yace"amin ni sunana musa ina zaune babbar riga da matata da yara na uku "

khalil yace "ni sunana khalil ina zaune a layout matata yarinya ce aurenmu beyi shekara ba"

musa yace "masha Allah Allah yabada zuria dayyiba zamu iya tafiya "

khalil yatashi suka nufi motar musa suka shiga suka kama hanyar babbar ruga batareda kowa yasan khalil na raye ba.

ya Allah kajikan musulmai maza da mata ka musu rahma 👏🏼

*zakuji inata yiwa mamatanmu addua wata falala naji daga bakin sheikh daurawa cewa duk wanda ya nemawa muminai gafara zaarubuta masa lada adadin musulman da suka mutun , dukda de inayi akowace sallata domin nikan tuno da yanuwana da abokaina da suka rasu, to jiya kuma hatsarin nan yakara tadamin hankali har natuno garabasar nan shine nace bari nafada maku nasan akwai wadanda basu sani ba se sufarayi, Allah kakaramana ilimi*
➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰

By

*MAMAN MAMY*
*(SHALELE)*

✍🏽✍🏽 *GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION*✍🏽✍🏽✍🏽

We are bearer's of so golden a pen🖊
We write assidiously perceiven no pain
So magical
Our creative golden pen🖊
Be hold our words
A product of our pen🖊
Savour our words
For it will cause you no pain.✍🏽

https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/

7⃣3⃣

*shafin nakine AISHA ALTO writer of SANA'ACE,da begenki arai na nayi typing inafatan zakiji dadin page dinnan nakine ke kadai uwargidan fahad🤣*

Har suka isa babbar ruga bawanda yace uffan dukkansu suna tunani daban, a kofar wani karamin gida suka tsaya duk suka fito waje, musa ya kalli khalil yace "nan shine gida na,muna zaune ne tareda mahaifiya ta "

Khalil yayi shiru yana tsaye musa ya shiga gida ba dadewa ya fito bakin gidan akwai kofar wani daki yasa key ya bude dakin yashiga few minutes yafito yacewa khalil "bismillah"

Khalil ya karasa ciki dakine karami da toilet aciki bakomai ciki se katifa da praying mat musa yace "nan shine masaukinka duk abinda kake bukata kamin magana "

Khalil yace "nagode sosai Allah yabaka ladar"

Musa yace "amin "ya juya ya fita,

Da fitarshi khalil yashiga toilet yayo alwala ya dawo ya shimfida carpet ya tada sallar laasar da Maghreb ,yana sallar yana hawaye yana tuno mutanen da suke tare a mota dukda shi yana gaba amma a bayanshi yanajin wata mata na waya tanafadin Sun kusa karasowa abata minty 10 kawai, da danta ahannu yanata kuka,sanda yagama sallar addua yayi ta masu akan Allah yajikansu ya musu rahma ,

Aisha ta dawo da drinks a leda tazauna tabude kwalin happy hour tadansha ta aje sauran, har lokacin amira tana ta kiran anty,

Mommy ta kalli Aisha tace "wai ina antin tata ita bazata zo dubata bane? "

Aisha ta yamutsa fuska tace "itama bata lpy tananan asibitin akwance "

Mommy tace "mtswww meyasa meta ne ita kuma? "

Aisha tace "I don't know me tamishi yayita jibgar ta ina shiga dakin na ganta cikin jini inaga tayi miscarriage abinda ya tsorata amira kenan har ta suma "

Mommy tace "amma naji dadi shegiya Allah yakara

Aisha ta girgiza kai ta nunamata amira da ido, mommy tai shiru,

amira tace "nide kukaini wurin anty inason naganta "

mommy tace "to zan kaiki wurinta kisha tea nikuma sena kaiki "ta dorawa amira cup,

Amira ta dan sha ta janye fuska,

mommy ta kalli Aisha tace "bari naje naga likitan inda yiwuwa se mukoma gida seya cigaba da zuwa yana dubata acan kamin ta warware "

Aisha tace "to "

Mommy ta dauki amira suka tafi office din doctor, ta zauna ta mishi magana yace ba matsala zasuiya tafiya mommy tai payment suka koma dakin, Aisha ta tashi suka shiga mota suka nufi gidan mommy,

Kafin su isa amira tai bacci suna zuwa mommy ta kwantar daita Aisha kuma tashiga toilet ta watsa ruwa,

Hawaye faseelat taketa yi don ma batada karfin yin kuka ,

ummi tagaji tace "shin ce miki akai ya mutu komi?"

faseelat tace "toyana ina?"

ummi tace "yananan zuwa ki kwantar da hankalinki "

Sannan tai shiru tana ta son taganshi don tsoro take karde sakinta yayi ,

Suna haka omer yashigo dakin faseelat tai sauri ta kulle ido, badan yadena jin takaici ba yace "faseelat ya jikinki? "

tai shiru saboda kunya dama he warned her amma bataji ba ga abinda yake gujewar yazo yana faruwa,haka akai ga auren khalil bata dauki shawararshi ba abinda yazatan kuma shi yafaru,

Ummi tace mishi "jiki kam aiba sauki kana ganin yadda take a kumbure, sonake jinin nan yakare in kamata in dan gasa mata jikin kotaji dama "

Omer yace "Allah ya sawwake "

Gidan sabeer fahad ya nufa yana parking yafito ya nufi gun sabeer dake waya da fatouma, sabeer naganinshi yace wa fatouma "pretty ga kanenki nan yazo bari nayi attending dinshi I will call you back"

yakashe kiran ya kalli fahad da yazauna a seat ya dafe kai ,sabeer yace "lpy de fahad naganka haka Very tensed? "

Fahad ya dago fuskarshi da tayi jawur yace "ina cikin tashin hankali sabeer kabani shawara plss "

sabeer yace "inajinka"

Fahad ya furzar da iska shikanshi haushin kanshi yakeji yace "something bad happened, kishi ya rufemin ido na doki faseelat hartayi miscarriage after I took her to hospital..."

sabeer yakatse shi yana fada "kana cikin hankalin ka kuwa? wane irin kishi ne da zesa ka bugi matarka har tayi bari? haba dude sekace baka waye ba ga hanyoyi nan birjik da zakai punishing nata seka tsaya ga duka saboda kajawa kanka raini agunta da iyayenta?"

Fahad ya dagamai hannu yace "please karka ce zakamin fada banzo wurinka don ka karamin tension ba nazo ne kafadamin mafita,in kuma fada zakamin sena tashi nai tafiya ta kobari bakai ba nakai numfashina ba "

sabeer yaja tsoki yace "badole nai masifa ba karika abu like mad person yanzu inajinka "

Shima fahad yaja tsokin bacin yana neman mafita da tafiyarshi zeyi, ya cigaba da cewa "after na kaita asibity nafita in duba princess dabata lpy se dawowa nai na tarar batanan yanuwanta sun dauketa naje gidansu many times a kulle "

sabeer yace"wow sunyi dede dasuka dauke diyarsu, kai kana tunanin kamar Aisha ce da kake jibga son rai dan tana kanwar ka? to yanzu de kaga da banbanci, seka jira hukuncin da zasu yanke "
Chapter 85 · 0% Book details