Sashe 11
Ragon Miji Complete Hausa Novel · about 8 min read
Alhaji ya zuba mata idanuwa he can't seee sense in her brain, yace "hjy are you out of your sense ?"
Tace "ni ban damu ko kakirani mad person amma a fasa aurennan kawai "
Ya tashi tsaye yana tafiya yace "ni inada hankali na inke naki ya bar jikinki, wa zan tura ya tunkari dattijon nan da wannan maganar? Mutane masu mutunci masu halacci, ki gama duk haukanki ki dawo dede na gayamiki, ni na fita wurin sanaata"
yayi tafiyar shi da ido kawai tabishi ita yake kira mahaukaciya, toyayi kyau, ta jawo waya ta kira khalil,
Yana school yayi saurin baro makarantar saboda muryar ta da yaji some how.
Yana zuwa ya shiga dakin yana binta da kallo dan haryanzu bata tashi daga zaunen da take ba yace "hjy lpya? "
Ta sauke tagumin da tayi tace "khalil ni na hada aurenka da faseelat yanzu kuma banason kasancewar sa "
Yace"bangane ba hjy"
tace "nade fadamaka ka gaggauta zuwa kasamu alhaji kace kafasa "
Yayi sauri ya tashi tsaye cikin tashin hankali, how he will live with out faseelat se kawai ya duke akan gwiwoyinsa ya hade tafukan hannayensa yace "hjy Dan Allah kiyi hakuri inma wani abu ya faru be dace kiyi wannan hukuncin ba, kiyi hakuri dan Allah wlh inasonta hjy "
tatashi tai kanshi ta falla mishi mari tareda cewa "shasha kawai katashi kaje kai abinda nace tunkan in saba maka"
Idanuwan khalil cike da hawaye hannunshi daya dafe da kumcinsa ya tashi tsaye ya fita daga dakin yanata zazzaro ido saboda tashin hankali, direct shagon alhaji ya nufa, alhaji naganinshi yasan ba lpy ba ya ja hannunshi ya fito dashi waje, suka matsa can suka zauna kan wani slope,
Alhaji ya fara magana "ka rabu da maganar saratu mutane kawai ke zugata, ita kuma ta dauka ka kwantar da hankalinka ka je ka cigaba da hidimiminka "
Khalil yace "tace dole se anfasa shi inde inason zaman lpy "
Alhaji yayi murmushi "kayi hakuri da abubuwan da zatai tayi komi ze wuce, nide ne me daura auren kuma se an daura "
Khalil jiki sanyaye yabar wurin be koma gida ba har dare koda ya koma ta rufeshi da fada alhaji ne ya saka ta dole tai shiru shikenan ta dauki fushi da khalil da alhaji ta dena bacci da duk wata hidima,
Yau kwana ukku kenan ana jidali amma da alamu de aurennan se anyi shi, danhaka ba bata lokaci ta tafi gidan rakiya suka shige daki,
Hjy tafada wa rakiya yadda ake Ciki rakiya tai shiru can zuwa tace "akwai mafita "
hjy tace "tame? "
Rakiya tace "kawo kunnenki kiji "hjy ta mika kunne rakiya tafada mata, se hjy tai kasake rakiya tace "Allah kuwa hankalinki kwance ba wani tension "
Hjy tace "kuma fa kai Nagode kawalliya shiyasa nike sonki" suka tafa hannu hjy tace "bari natashi na tafi se Kinzo har hankali na ya kwanta?"ta tashi ta tafi.
Shikenan hankali kwance ta cigaba da hidimar biki. Se kuma lokacin ta sakarwa alhaji da khalil mara,
Faseelat da friends nata sunata shirye shirye kuma tunda ta dawo ummi ta cigaba da nata gyaran ,gaba daya faseelat ta rame saboda tunani har yanzu ko digon son khalil babu a ranta tayi adduar tayi adduar shiru haryanzu batajin sonshi, duk wanda ya ganta se yayi tunanin ko rabuwa yasata rama kuma de it's normal thing mafiya yawan amare na rama,.
Yau saura kwana biyu biki yan biki tuni suka fara cika gida mutanen Niger su dije da ammah dasu fadila duk har suniso, anata hidima faseelat tasha kunshi anyi mata relaxer da kitso jelar gashin har kafada,tayi kyau sosai,
shima angon duk ya rame yayi wuri -wuri dashi saboda hidima, abubuwa sunyi yawa,
Yau din kuma akaje akaiwa faseelat jere, anata yaba kyan kayan har dakin khalil ansakawa kujeru da karamin gado.
Gobe NE daurin aure dukda de bawani event amma maza zasuuyi walima ita kuma faseelat yau sukayi setting, wannan yasa duk suke busy khalil rabindshi ma da faseelat tun jiya,
Can bayan Maghreb alhaji yaji duk bejin dadi tunda hjy ta sako fitina hawan jininshi ya tashi hakanan yake shan drugs be kwanta ba, yau abun yayi yawa gida ya dawo ya shige daki ya kulle, bawanda ma yagansa suna can ciki suna hidima,
Yayi kwance yana dafe da zuciyarshi yana meda numfashi,
Sega rakiya tazo hjy saratu ta jawota kofar dakin alhaji dan privacy, suna magana kasa kasa rakiya tace "inafatan kinnyi duk yadda malam yace? "
hjy saratu ta babbake da dariya "yo mi zanjira? Kede Allah yabarmu tare "suka cigaba da magana alhaji yanajinsu, gabadaya tunda suka fara magana hankalin shi ya tashi nan ciwonshi ya taso haikan, yanata meda numfashi yana fiddo, suko su hjy suna Gama magana sukabar gun bayan Sun kamo wata fira daban,
Alhaji ko zuciyarshi kamar zata fashe haka ya keji dandanan yafara karanto hailala yana ta memetawa har ya cika,
Se bayan ishai sosai wajen karfe 10 :30 hjy taje kofar dakin tasan de yanzu yaisa ya dawo ta fara kwankwasa kofar shiru gata kuma a kulle daga ciki, se ta koma ta window ta haska torchlight saboda ba haske dakin seta hango alhaji kwance, tai ta kiran alhaji amma shiru ta kwartsa ihu "ni yau nashiga ukku na Lalace ni saratu alhaji ya mutu "
ihunta yasa duk kowa ya fito su siyama da sauran yanbiki duk suka yo out, kowa nata sallallami suna leka windon itako ta zube kasa tanata ihu, siyama na kuka takira khalil ta fada masa ,hankali tashe yayo gida da temakon zarto aka yanke kubar suka shiga dakin, alhaji de ya mutu, kuka kawai sukeyi ba yaro ba babba dandanan labarin mutuwarshi ta game dangi da yanuwa,
Su ummi tunda akadamata tafara hawaye, Allah kenan me iko akan komi, shine kadai yakeyin komi a duk lokacin da yaso,mutuwa bata da notice kuma baajin alert ko wani sign zuwa kawai take, ana gobe daurin auren dansa shi kuma ya mutu,
Allah yajikan musulmai ya musu gafara.
Su faseelat anbaje kan bed itada friends da dangi labarin aure kawai suke yadda zasu kula da mazajensu se ga ummi da wannan labarin suma Sukai jingum jingum.
da karfe bakwai aka kai alhaji gidanshi na gaskiya, sabon gida inda mutum ke girbar abinda ya shuka.
tare da baba babba akai janaiza bayan sunkoma wurin zaman makoki shi da daya daga cikin wakilan khalil Sukai magana akan daurin aure zaa dagashi se next week,
Waccan dattijon ya juya ya na kallon khalil da kanshi ke sunkuye hannunsa kan gwiwa duk Bayan seconds yana share hawaye, ya girgiza kai.
Hjy saratu da siyama sunsha kuka kuma suna kanshi gidan biki yazama gidan makoki ,bayan kwana ukku da yawa daga cikin yanbiki suka koma gida kafin ran bikin yayinda yan niger tuni sunkoma gida senanda 4 days din.
Tunda abun Yafaru khalil ya sake komawa wani kala dan haryanzu a hurhurce yake, faseelat de takirashi ta mai gaisuwa, har yanzu basu ga juna ba,
*************
Bayan kwana hudu yau daurin aure yan biki tuni duk sundawo abubuwa ake da sanyin jiki,
Taro yayi taro a masallacin abu ubaida, bayan gama salla aka daura auren khalil usman da faseelat maaruf akan sadaki dubu 40 lakadan ba ajalan ba.
Ango khalil ansha tsadaddun hill din corver shoe's hakan yasa ya kara tsayi yasha milk shadda, as usual hular nan na kusa da ido se washe baki yake yana gaiswa da mutane a bangare guda akai walima da hotuna.
Bangaren amarya faseelat ............
yo Anya tayi wanka ma ita 🤔
[7/12, 10:59 PM] Maman Mamy: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰
By
*MAMAN MAMY*
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*
*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*
1⃣6⃣
*dedicated to umar dalha my bazawari 😂 & all golden pen members luv u all*
Faseelat kau kukanta take ta sha tunda garin Allah ya waye bawanda besa baki ba amma taki tai shiru, da yake tana gidan baba babba,dan nan sukayi setting kuma nan zaa dau amarya,
Matasan yanmata irinsu fadila husna da manya irinsu fatouma da rahma Sun sakata tsakiya suna ta kallo kowacen su taci gayu banda faseelat, sun rasa kukan me take saboda cikinsu bawadda tasan batasan auren se fadila kuma bata fadawa kowa ba,
Baaba ta shigo dakin taga haryanzu faseelat bata bar kuka ba taje wurinta ta zauna faseelat ta dago jikakkun eyelashes dinta ta zuba mata amma kanta na a sadde, baaba tace "kiyi hakuri haka faseelat Kowa da kikagani dakin miji seda yaga irin wannan ranar, nasani akwai damuwa saboda rabuwa da iyaye amma hakuri akeyi, yanzu kina ta kuka so kike ciwo ya kamaki ne? "
Faseelat ta girgiza kai ,baaba tace "Tom kiyi hakuri ki tashi kije kiyi wanka tun dilkar safe har ta bushe jikinki kinki ki wanka kitashi, nasan zuwa yanzu an daura aure, kitashi ki shirya kuje gidan ummi wurin waazi kafin dare "
Faseelat hawaye suka kara zuraro mata ta share duk wurin Sun zubamata ido fadila ma ta danyi mata kwalla saboda ita kadai tasan reality na abun,
Rahma cousing dinta yar ban dariya bata da kunya ko kadan tace "baaba kubarta tayi kuka zata je gidan Sandar famfo ku barta tayi "yanmatan suka fashe da dariya,
baaba ta girgiza kai taja faseelat har bakin toilet seda taga shigarta sannan ta bar dakin,
Tana fitowa wanka wata kawarta makeup artist ce tai mata kwalliya, tsantsarar rar kwalliya wadda me karamin tunani baze iya ganinta ba, ta saka lace wanda daka ganshi kasan dole yayi tsada, white and red ga uban stones jikinshi head din ta ja, haka purse dinta da takalminta se tayi gyale da dankwalin lace din, wow sukaita fada, nan fa suka fara shooting pictures cikin farin ciki itako hjyar ko murmushi amma kuma tanayin kyau,
Kawarta ta zainab ta raba gefe ta kira abokin khalil ta fada mashi yazo ya daukesu zuwa gidansu faseelat din ,
Tace "ni ban damu ko kakirani mad person amma a fasa aurennan kawai "
Ya tashi tsaye yana tafiya yace "ni inada hankali na inke naki ya bar jikinki, wa zan tura ya tunkari dattijon nan da wannan maganar? Mutane masu mutunci masu halacci, ki gama duk haukanki ki dawo dede na gayamiki, ni na fita wurin sanaata"
yayi tafiyar shi da ido kawai tabishi ita yake kira mahaukaciya, toyayi kyau, ta jawo waya ta kira khalil,
Yana school yayi saurin baro makarantar saboda muryar ta da yaji some how.
Yana zuwa ya shiga dakin yana binta da kallo dan haryanzu bata tashi daga zaunen da take ba yace "hjy lpya? "
Ta sauke tagumin da tayi tace "khalil ni na hada aurenka da faseelat yanzu kuma banason kasancewar sa "
Yace"bangane ba hjy"
tace "nade fadamaka ka gaggauta zuwa kasamu alhaji kace kafasa "
Yayi sauri ya tashi tsaye cikin tashin hankali, how he will live with out faseelat se kawai ya duke akan gwiwoyinsa ya hade tafukan hannayensa yace "hjy Dan Allah kiyi hakuri inma wani abu ya faru be dace kiyi wannan hukuncin ba, kiyi hakuri dan Allah wlh inasonta hjy "
tatashi tai kanshi ta falla mishi mari tareda cewa "shasha kawai katashi kaje kai abinda nace tunkan in saba maka"
Idanuwan khalil cike da hawaye hannunshi daya dafe da kumcinsa ya tashi tsaye ya fita daga dakin yanata zazzaro ido saboda tashin hankali, direct shagon alhaji ya nufa, alhaji naganinshi yasan ba lpy ba ya ja hannunshi ya fito dashi waje, suka matsa can suka zauna kan wani slope,
Alhaji ya fara magana "ka rabu da maganar saratu mutane kawai ke zugata, ita kuma ta dauka ka kwantar da hankalinka ka je ka cigaba da hidimiminka "
Khalil yace "tace dole se anfasa shi inde inason zaman lpy "
Alhaji yayi murmushi "kayi hakuri da abubuwan da zatai tayi komi ze wuce, nide ne me daura auren kuma se an daura "
Khalil jiki sanyaye yabar wurin be koma gida ba har dare koda ya koma ta rufeshi da fada alhaji ne ya saka ta dole tai shiru shikenan ta dauki fushi da khalil da alhaji ta dena bacci da duk wata hidima,
Yau kwana ukku kenan ana jidali amma da alamu de aurennan se anyi shi, danhaka ba bata lokaci ta tafi gidan rakiya suka shige daki,
Hjy tafada wa rakiya yadda ake Ciki rakiya tai shiru can zuwa tace "akwai mafita "
hjy tace "tame? "
Rakiya tace "kawo kunnenki kiji "hjy ta mika kunne rakiya tafada mata, se hjy tai kasake rakiya tace "Allah kuwa hankalinki kwance ba wani tension "
Hjy tace "kuma fa kai Nagode kawalliya shiyasa nike sonki" suka tafa hannu hjy tace "bari natashi na tafi se Kinzo har hankali na ya kwanta?"ta tashi ta tafi.
Shikenan hankali kwance ta cigaba da hidimar biki. Se kuma lokacin ta sakarwa alhaji da khalil mara,
Faseelat da friends nata sunata shirye shirye kuma tunda ta dawo ummi ta cigaba da nata gyaran ,gaba daya faseelat ta rame saboda tunani har yanzu ko digon son khalil babu a ranta tayi adduar tayi adduar shiru haryanzu batajin sonshi, duk wanda ya ganta se yayi tunanin ko rabuwa yasata rama kuma de it's normal thing mafiya yawan amare na rama,.
Yau saura kwana biyu biki yan biki tuni suka fara cika gida mutanen Niger su dije da ammah dasu fadila duk har suniso, anata hidima faseelat tasha kunshi anyi mata relaxer da kitso jelar gashin har kafada,tayi kyau sosai,
shima angon duk ya rame yayi wuri -wuri dashi saboda hidima, abubuwa sunyi yawa,
Yau din kuma akaje akaiwa faseelat jere, anata yaba kyan kayan har dakin khalil ansakawa kujeru da karamin gado.
Gobe NE daurin aure dukda de bawani event amma maza zasuuyi walima ita kuma faseelat yau sukayi setting, wannan yasa duk suke busy khalil rabindshi ma da faseelat tun jiya,
Can bayan Maghreb alhaji yaji duk bejin dadi tunda hjy ta sako fitina hawan jininshi ya tashi hakanan yake shan drugs be kwanta ba, yau abun yayi yawa gida ya dawo ya shige daki ya kulle, bawanda ma yagansa suna can ciki suna hidima,
Yayi kwance yana dafe da zuciyarshi yana meda numfashi,
Sega rakiya tazo hjy saratu ta jawota kofar dakin alhaji dan privacy, suna magana kasa kasa rakiya tace "inafatan kinnyi duk yadda malam yace? "
hjy saratu ta babbake da dariya "yo mi zanjira? Kede Allah yabarmu tare "suka cigaba da magana alhaji yanajinsu, gabadaya tunda suka fara magana hankalin shi ya tashi nan ciwonshi ya taso haikan, yanata meda numfashi yana fiddo, suko su hjy suna Gama magana sukabar gun bayan Sun kamo wata fira daban,
Alhaji ko zuciyarshi kamar zata fashe haka ya keji dandanan yafara karanto hailala yana ta memetawa har ya cika,
Se bayan ishai sosai wajen karfe 10 :30 hjy taje kofar dakin tasan de yanzu yaisa ya dawo ta fara kwankwasa kofar shiru gata kuma a kulle daga ciki, se ta koma ta window ta haska torchlight saboda ba haske dakin seta hango alhaji kwance, tai ta kiran alhaji amma shiru ta kwartsa ihu "ni yau nashiga ukku na Lalace ni saratu alhaji ya mutu "
ihunta yasa duk kowa ya fito su siyama da sauran yanbiki duk suka yo out, kowa nata sallallami suna leka windon itako ta zube kasa tanata ihu, siyama na kuka takira khalil ta fada masa ,hankali tashe yayo gida da temakon zarto aka yanke kubar suka shiga dakin, alhaji de ya mutu, kuka kawai sukeyi ba yaro ba babba dandanan labarin mutuwarshi ta game dangi da yanuwa,
Su ummi tunda akadamata tafara hawaye, Allah kenan me iko akan komi, shine kadai yakeyin komi a duk lokacin da yaso,mutuwa bata da notice kuma baajin alert ko wani sign zuwa kawai take, ana gobe daurin auren dansa shi kuma ya mutu,
Allah yajikan musulmai ya musu gafara.
Su faseelat anbaje kan bed itada friends da dangi labarin aure kawai suke yadda zasu kula da mazajensu se ga ummi da wannan labarin suma Sukai jingum jingum.
da karfe bakwai aka kai alhaji gidanshi na gaskiya, sabon gida inda mutum ke girbar abinda ya shuka.
tare da baba babba akai janaiza bayan sunkoma wurin zaman makoki shi da daya daga cikin wakilan khalil Sukai magana akan daurin aure zaa dagashi se next week,
Waccan dattijon ya juya ya na kallon khalil da kanshi ke sunkuye hannunsa kan gwiwa duk Bayan seconds yana share hawaye, ya girgiza kai.
Hjy saratu da siyama sunsha kuka kuma suna kanshi gidan biki yazama gidan makoki ,bayan kwana ukku da yawa daga cikin yanbiki suka koma gida kafin ran bikin yayinda yan niger tuni sunkoma gida senanda 4 days din.
Tunda abun Yafaru khalil ya sake komawa wani kala dan haryanzu a hurhurce yake, faseelat de takirashi ta mai gaisuwa, har yanzu basu ga juna ba,
*************
Bayan kwana hudu yau daurin aure yan biki tuni duk sundawo abubuwa ake da sanyin jiki,
Taro yayi taro a masallacin abu ubaida, bayan gama salla aka daura auren khalil usman da faseelat maaruf akan sadaki dubu 40 lakadan ba ajalan ba.
Ango khalil ansha tsadaddun hill din corver shoe's hakan yasa ya kara tsayi yasha milk shadda, as usual hular nan na kusa da ido se washe baki yake yana gaiswa da mutane a bangare guda akai walima da hotuna.
Bangaren amarya faseelat ............
yo Anya tayi wanka ma ita 🤔
[7/12, 10:59 PM] Maman Mamy: ➰➰➰➰➰
*RAGGON MIJI*
➰➰➰➰➰
By
*MAMAN MAMY*
https://www.facebook.com/groups/1569379426621615/
*~GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION💫💫💫~*
*~❄We beare's of soon golden We writer's assiduously percieven No pain so Magical Our creative golden pen Be hold our worlds A production of our pen savour Our worlds for it cause u np pain~*
1⃣6⃣
*dedicated to umar dalha my bazawari 😂 & all golden pen members luv u all*
Faseelat kau kukanta take ta sha tunda garin Allah ya waye bawanda besa baki ba amma taki tai shiru, da yake tana gidan baba babba,dan nan sukayi setting kuma nan zaa dau amarya,
Matasan yanmata irinsu fadila husna da manya irinsu fatouma da rahma Sun sakata tsakiya suna ta kallo kowacen su taci gayu banda faseelat, sun rasa kukan me take saboda cikinsu bawadda tasan batasan auren se fadila kuma bata fadawa kowa ba,
Baaba ta shigo dakin taga haryanzu faseelat bata bar kuka ba taje wurinta ta zauna faseelat ta dago jikakkun eyelashes dinta ta zuba mata amma kanta na a sadde, baaba tace "kiyi hakuri haka faseelat Kowa da kikagani dakin miji seda yaga irin wannan ranar, nasani akwai damuwa saboda rabuwa da iyaye amma hakuri akeyi, yanzu kina ta kuka so kike ciwo ya kamaki ne? "
Faseelat ta girgiza kai ,baaba tace "Tom kiyi hakuri ki tashi kije kiyi wanka tun dilkar safe har ta bushe jikinki kinki ki wanka kitashi, nasan zuwa yanzu an daura aure, kitashi ki shirya kuje gidan ummi wurin waazi kafin dare "
Faseelat hawaye suka kara zuraro mata ta share duk wurin Sun zubamata ido fadila ma ta danyi mata kwalla saboda ita kadai tasan reality na abun,
Rahma cousing dinta yar ban dariya bata da kunya ko kadan tace "baaba kubarta tayi kuka zata je gidan Sandar famfo ku barta tayi "yanmatan suka fashe da dariya,
baaba ta girgiza kai taja faseelat har bakin toilet seda taga shigarta sannan ta bar dakin,
Tana fitowa wanka wata kawarta makeup artist ce tai mata kwalliya, tsantsarar rar kwalliya wadda me karamin tunani baze iya ganinta ba, ta saka lace wanda daka ganshi kasan dole yayi tsada, white and red ga uban stones jikinshi head din ta ja, haka purse dinta da takalminta se tayi gyale da dankwalin lace din, wow sukaita fada, nan fa suka fara shooting pictures cikin farin ciki itako hjyar ko murmushi amma kuma tanayin kyau,
Kawarta ta zainab ta raba gefe ta kira abokin khalil ta fada mashi yazo ya daukesu zuwa gidansu faseelat din ,