Sashe 64
Mahabeer Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
🌊🌊🌊🌊🌊 🅿4⃣3⃣ 🌊🌊🌊 ..yanzun hakama kwance take ta lumshe idanunta sai taji an runtse mata idanuwa gam ana qyalqyata dariya, kamo hannuwan tayi cikin murmushi tace''naganeki sister ay,, sakar fuskar tata nabeela tayi tana sakin dariya ta zauna nan gefen ummu hani din tace "kaii sister kinyi kyau fa wlh sosai, kinga yanda kika sake fresh haka kamar irin kin fara karbar hot nesseges haka daga wajen yaya mahabeer amakson kuwa?" hararta ummu hani tayi tace "wani irin saqo kuma zaimun haka ga jikina kuma harna canza? fahimtar dani please kinsan ba hausa na fiye ganewa sosai bama a cukurku dan gskia hausarku namun tsauri har yanzun sister nabee? nabeela tayi dariya tace "mubar maganar kawai sister share nan gaba nasan zaki fahimta ay, badai har momy ta gama had'a miki kayan kiba? cewar nabeela tana kallon jikkunan ummu hani na tafiya guda 2 manya manya, ummu hani ta yamutsa fuskarta tace "uhmm kindai gansu can dan wlh tun shekaran jia mah take cewa inyi parking nawa sam nakasa wlh sai yau din nan ma da safe ta shigo da kanta taimun har ina cewa momy wannan kaya sunmin yawa ay, kinsan mitace kuwa sister? girgiza kai nabeela tayi tace "em em," ummu hani tace "cewa tayi in son samu ne in yi dressing sama da nawa a rana indai amakson na nan a gida sai narasa gane ma'anar hakan da tace sister kuma na kasa tambayar ta, koke kin sani? kallon ta kawai nabeela keyi a zuciyarta tace lallaikm ummu hani har yanzu da sauranki ta yarinta sosai dan nabeela kam zata tserewa ummu hani da shekaru kamar 5 haka, tasan kuma intace mata danta jawo hankalin mahabeer ne momy ke nufi tofa da wiya tayi hakan kuwa, dan tasan bawai wani jituwa suke ba bare har wani yaji kwadayin farantawa wani cikinsu, a fili kuma sai tace "a'a sister amman may be qilan tana nufin kullum ki kasance mace mai tsabta da'iman kina cikin gayu shiyasa nikega nidai a fahimta na fa" shiru ummu hani tayi tace "eh nim raina yaban hakan" murmushi nabeela tayi tace "bare ma ni nasan sister na daman ta iya daukan gayu yanzun sai dai ma ta qara akan nada ko? yar siririyar dariya sukayi sannan nabeela tasake cewa "kai sister yanzu gobe zaku tafi kinga bakinan za'ayi bikina inda yanzu baifi 'yan kwanaki ba tunda an q'ara saukosa dud bnji dadi ba sister na ummu hani bata nan za ai bikina"! tayi maganar kamar tai kuka kuma har cikin ranta abun,, rungume juna sukayi sannan ummu ta d'ago tace "kiyi haquri sister nabee ko bananan akai bikinki fatan alheri na nagareki koda yaushe kuma kinga ai muma zamu dawo bacen zamuyi ta zama ba koko yakikace sister na? ", tayi maganar cikin murmushi nason farantawa nabeela din. gyada kai nabeela tayi tace "hakane ngd my sis kuma yanzun ma taso muje daki wajen annah muyi fira. hakan kuwa suka sauka qasa, zuciyar ummu hani cikeda tsananin kewar son ganin mommonta da baffanta sai dai tasan dole ta haqurarwa zuciyar ta dan ganinsu kam ba yanzu ba. washe gari a cikin airport banda kuka babu abunda ummu hani keyi tariqe annah da momy umaimah gam da hannu 1 hannunta dayan kuma ta riqe nabeela ganin da gaske dai tafiyar zasuyi, daqyar2 su annah suka rarrasheta tayi shiru. mahabeer na gefe kamar ya faffala mata mari yakeji danshi ya tsani gunjin kuka kamar dai wadda zai sace? a haka suka shiga jirgi suna d'agawa juna hannu jirgin harya qule saman sararin samaniya sannan ummu ta daina ganin su momyn, sai a lokacin ne kuma tsoro ya shigeta dan tunda take ko jirgi kusa da ita bata taba gani ba bare har ta shigesa ma, jin yanda jirgin ke tsula gudu ne yasa taji lokaci day'a 'yan hanjin cikin cikinta kad'awa tayi saurin kallon mahabeer dayai kishingidawar sa wato ya kwantar da kansa da bayan sa a saman kujerar da yake akai, gashi ya rufe fuskarsa da pacing cap dinsa ansa hand belt dudta kasa motsin kirkima tana gani yanda ake rarraba abubuwan motsa baki a cikin jirgin amman ko kadan takasa kar6a bare tasha. tsoro ne kawai ke qara ratsata jitakeyi kamar numfasinta nayin sama sama ma dole tasa ta yakice hand belt din jikinta da gudu cikin sassarfa tayi kan mahabeer dake gefenta ta fad'a jikinsa tasaki kuka mai sauti, daga kwancen da yake bazato ba tsammani yajita cikin jikinsa ta ruqunqume sa tana masa kukan jarabar nan nata kamar yanda yake cewa, wani dogon tsoki yaja kuwa dan jin wasu mulmulallun abubuwa tausasan gaske sun tokare masa q'irji suna qara lumewa saman qirjinsa kamar mabusa tun yana kasa fahimtar miye su din har takai ya fahimci mamantane nan a wajen suke tunkurarsa. nan take kuwa yaji yanayin jikinsa yaso sauyawa yadinga jin wabi abu nabin jikinsa wanda yasan bakomi bane face tada masa hankali da yarinyar ke sonyi yanzu batareda ya shirya wa hakan ba, miqewa yake sonyi zaune sosai amman taqi basa damar hakan sai qara cusa fuskarta datakeyi tsakan qirjinsa tana manne masa dan tsoro dan gaba dayan ta a gigice take ya lura , gaba day'a ya rasa yanda zai mata ma shi, ba abun ya zare mata idanuwa ba bata ganin sa kuma, shi kuma ba abin ya kwatsa mata tsawa ba kuma ga mutane kurkusa dasu nan, yarasa yanda zaiyi dole yasa ya yakice komi a ransa a lokacin har yakai bakinsa saitin kunnen ta ahankali yake furta kalmar "ke?.. ke?.. waimi ye hakane kike? baki ganin mutane zaki shigen jiki ko kunya bakiji? tana qwaqumen dashi yaji tace "wlh nikam bazan iya sakin kaba har sai mun sauka dan.. danni.. nidai tsoro nikeji..tayi maganar muryarta na rawa. ganin yanda jama'ar wajen ke kallonsu yasa ya nutsu yabar qoqarin turetan daga jikinsa kan dole badon yaso ba yabarta manne bisa jikin nasa yana sakan mata numfashin sa sanyayye a gefen kunnen ta na dama, haka jirgi ya dinga keta hazo tsawon wasu lokuttan sai gasu sun sauka filin jirgi na qasar london. mutane suka fara saukowa mahabeer na gaba ummu hani na bayansa sai kalle kallen tsaunukan ginannun gidajen su na qasar takeyi gwanin sha'awa, a zuciyar ta tace "o'ni ummu hani yau nice a qasar turawa dole kuwa na tsaya qara kashe kwarkwatan idanuwa na yanda zanbawa baffa na mommona labari na gani da zahari danai, wajen kalle kallen nata kuwa har mahabeer yai mata nisa batama ankara ba, dan kuwa hankalin ta ma gaba day'a ya tafi ga wasu tsoffin turawa da suke soyayyar su lokacin da sukazo giftawa ta wajenta, sakin baki tayi ummu hani tayi tana kallonsu takuwa tab'e d'an pink din bakin nan nata tace "kaii Wayyo ni!! su din tsofaffi ma dasu ko kunya ma bassa ji suna abubuwan qyama na tsotsan baki a hanya?? mtsss Allah sawaqa mun nikam lah inji larabawa bazanyi wannan abun ba"!. jitayi an sakar mata wani iriyar zazzafan ranqwashi qwamm a smn tsakiyan kai, da sauri ta dafe kan nata kuwa har siririn mayafin doguwar rigarta na sulalewa qasa kitson gashin kanta ya bayyana, takuwa bud'e baki tareda zaro harshe tana karkad'awa tareda furta "wash!! lalalala minaiwa mutum nito?!!! ganin mahabeer datayia tsaye a gabanta a dalilin juyowa dayayi shima ya hangota bata tafi ba ya sashi yadawo a fusace harya kaiga sakar mata ranqwashin nan sannan yace "baq'auyar yarinya kawai, ya fuzgo hannunta da qarfi ita kuwa sai faman turo masa bakinta takeyi dantaji zafun ranqwashin kuwa sosai a kan nata. a haka har ya tulla ta cikin drop motor dinda ya tsaida suka tafi har suka iso cikin wani plate house mai part uku ga alama ma akwai wasu cikin gidan sauran part din 2n, sai day'an shine nasu wanda suka shiga cikinsa ynxun. suna shiga qaton falon gidan nan ma ummu hani daina sosai kwanduwar kanta da tasha daga garesa tayi tahau kallon tsarin falon,, tana nan tsaye gun har mahabeer ya hau sama ya fito ya dawo qasa ya zauna bisa kujera tareda dafe kansa dan wata sabuwan damuwarce fal cikin ransa a yanzun wanda yasameta a gidan , a hankali ya furta "oh my god!!! room one only??? daki day'a zamuyi kowane movement namu da wannan village girl din knn?! da sauri kuwa ya fiddo phone dinsa, number dady ya kira ba bata lokaci dady mua'zzam ya d'aga kuwa yace "yaya dai sojana kun sauka lpia knn dan naga number tazo da + nasan kunkai ko?" kamar zai yi kuka yace "eh dady mun iso amman dady akwai matsala fa? dady mua'zzam yace "subhanalla Innalillahe miya faru kuma? badai wani abun ya faru daku ba? "a'a dady bawani abu bane gidan da muka sauka din ne naga daki day'a ne shiyasa...!,, sauke ajiyar zuciya dady mua'zzam yayi yace "kaii sojana wlh ba qaramin tayar mun da hankali kai ba nazata wani abunne yafaru daku ma, dan kuma daki day'a ne to miye?? naga ai kai day'a ne kaida matarka miye na damuwa kuma anan? "dady nidai bazan wala ba gskia yanda nike buqata kuma daki day'a ai ina tunanin yai mana kad'an nidai zan nemi wani gidan dady sai muk... katsesa din dady mua'zzam yayi yace "noo sojana in kai mun hakan ai nikam bazanji dad'i ba, dan mr johson abokin kasuwancina dake zaune nan qasar London din shi nabawa cigiyar gidan da zaku zauna nadan tsawon lokacin da zakuyi a garin shine yace indai wannan ne babu matsala shi zai baku day'a daga part din cikin gidansa dayake zaune da family nasa sai ku zauna kuma mafarin knn ya bani address din gidan nabaka kauma to sai kuma yanzun sojana yaji an canza magana kana ganin zaiji dad'i kuwa? zai gafa kamar an raina masa ne kuma babu dad'i irin hakan"! shiru mahabeer yayi ya kasa magana yabi ummu hani da kallon harara kawai wanda dud itace yake ganin ta sashi wannan qangin quncin da yake ciki. ita kuwa sam bata sanma yanayi ba dan hankalin ta gaba day'a ma bayya garesa, jiyowa dady mua'zzam yayi yace "nasan ka da haquri sojana dan haka nike son ka daure ku zauna a hakan inda bawani dogon lokaci ne zaku dauka ba acan din zaku dawo gida kuma uhm.? babu yanda