← Book details Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 86 OF 90

Sashe 86

Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hawaye na share nace"Wallahi Mamma abinda nake taso ya fahimta kenan ba kowa Allah kewa baiwa irin wannan ba amma idanunsa sun rufe ya kasa fahimtata Mamma idan kinga irin rigimar da mukayi dashi akan wannan cikin dake tare dani sai kinyi mamaki! hakuri nai tayi ina masa addua kullum ina nuna masa gaskiya Alhamdulillahi kafin yayi wannan tafiyar naga fa'idar adduar da nake masa da kansa ya dawo kan hanya ya cigaba da nuna kulawarsa akaina da cikin da nake dauke dashi Mamma kema don Allah kiyi hakuri kiyi masa uziri akan abinda ya aikata na rashin kyautawa."

Shuru tayi tana girgiza kanta, nace"Mamma kada kiyi fushi dashi don Allah insha Allahu Allah ya ganar dashi gaskiya." Kallona tayi tace"Shikkenan Sumayya saboda ke zan yafe masa amma dai duk da haka sai nayi masa fada akan abinda yayi saboda ya kiyaye anan gaba." nace" To Mamma amma dan Allah kada ki fadawa Maimartaba maganar nan bana so hankalinsa ya tashi kuma bana so jama'a suyi masa wani irin kallo."

Murmushi tayi tace."Sumayya babana ku yayi wa laifi amma bakyaso ya tozarta a yau na tabbatar da cewa ke matar rufin asirinsa ce insha Allahu zan bar maganar nan a tsakaninmu kamar yanda kika nemi alfarma ina rokon Allah ya tabbatar da alkairi a tsakaninku.

Cikin farin ciki na amsa da "ameeen Mamma nagode kwarai da gaske."

Dr Sadiya ce ta shigo dakin, ganina a zaune muna magana yasa tayi murmushi tace"Alhamdulillahi jiki yayi kyau ko."? Mamma tace"Aikuwa jiki yayi kyau Allah ne abin godiya." Tace."Yanzu Dr ya kira ni a waya yake tambayata ya yanayin jikin naki dalilin da yasa ma kenan na shigo na duba na gani amma naji dadin ganinki a haka ina fatan babu abinda yake miki ciwo." ? ina kokarin magana kira ya shigo wayarta murmushi tayi ta daga wayar cikin ladabi tace"Eh gani ma a dakin muna tare da ita alhamdulillahi jikinta yayi sauki Dr baby kuma na cikin koshin lafiya." shuru tayi tana sauraransa kafin tace"Okey to bari na bata wayar." da sauri ta miko min na kar'ba a nutse na gaisheshi, ya amsa cikin kulawa yana tambayata nace"Babu abinda ke damuna baby lafiya lau kamar yanda Dr Sadiya ta fada maka.'' Shuru nai ina sauraransa, nace"Eh yana motsi sosai." Hamdala yayi ga Allah yace."Sumayya nasan Mamma tana cikin 'bacin rai dan Allah ki tayani bata hakuri kafin na dawo."

Cikin tausasawa nace"Kada ka damu insha Allah zanyi maka kokari Allah ya dawo daku lafiya." ajiyar zuciya mai sanyi ya sauke yace."my lov banda kamarki a duniya." da sauri na kalli Mamma ina jin tsoron kada taji abinda yace...... ya cigaba da cewa'' Tun dana sauka a america nake cikin kad'aici banta'ba tsammanin ina sonki da gaske ba sai da nayi nesa dake." ajiyar zuciya na sauke sosai nake jin dadin kalamansa yace."Idan na dawo koni ko Lauratu ko hajiya Karima dan ba zan barsu sukai labari ba.''' Da sauri nace"Kayi hakuri komai ya wuce insha Allahu dama nace maka Allah ba zai barsu su cimma manufarsu ba kada kayi saurin yanke hukunci." Yace." wancan karon haka kikace nayi hakuri na kuma hakura wannan karon kam ba zanyi ba sai na dauki mataki." shuru nai ina sauraransa yace."Yanzu Dr Sadiya zata sallameku kuje gida ki kwanta ki huta kisha maganguna kinji ko." nace"To shikkenan." Shuru yayi na minti biyu kafin yace."Me kike so nazo miki dashi."? dan murmushi nai wanda yasa Mamma barin gurin kunya ta kamani nace"Komai ka siyo min inaso. " kawai sai na kashe wayar da sauri na mika mata ta kar'ba a nutse tace"Zakuje gida yanzu zan kawo miki magunguna insha Allahu duk sati zan dinga zuwa har gida ina dubaki." nace."To shikkenan nagode." Murmushi tayi tana kokarin fita tace"Ranki ya dade kinfi karfin komai a wannan asibitin."

Lokacin da muka shiga masarautar a hargitse muka sameta jama'a sun cika a bangaran Ciroma sai surutai ne ke tashi yayinda kowa ke fadar albarkacin bakinsa akan abinda ya faru da Hajiya Karima da Kanwarta Lauratu.

Kai tsaye Mamma ta umarci Direba daya wuce damu gurinta ko zama bamuyi ba jakadiya ta shigo hankali a tashe! Mamma ta kalleta cikin alhini tace"Jakadiya wai shin me yake faruwa ne a masarautar nan ko'ina ya hargitse shin ina Maimartaba da 'Yan uwansa." ?

Jakadiya jiki a mace! tace"Ranki ya dade Allah ne ya saukar da ikonsa akan Hajiya Karima da kanwarta Lauratu........Tun sanda da Lauratu ta gane cewa asirinta ya tonu sai tayi yunk'urin 'barin gari tare da kayanta Allah cikin ikonsa sai ya saukar mata da tsautsayi mai munin gaske! a titin Zaria tayi mummunan had'ari! motar da take ciki ta 'kone k'urmus! ita kanta ta gama 'konewa labarin faruwar al'amarin yasa Hajiya Karima ta yanke jiki ta fad'i a gurin gabadaya dai yanzu an rasa yanda za'ayi da ita dan gabadaya ta sandare babu abinda yake amfani a jikinta sai numfashinta dake fita sama-sama! Khalisat itace ke kuka tana farfad'ar irin sharrin da iyayenta suka dinga k'ullawa gashi tun ba'aje ko'ina ba ya koma kansu......Yanzu haka Maimartaba da sauran 'yan uwansa suna tare da Maigirma Ciroma domin shi kansa a lokacin rud'ewa yayi ya dinga hawaye yana nadamar abinda ya aikata a baya da kyar aka kamashi aka shiga dashi daki ana tausar zuciyarsa.

Jikina a sanyaye na nemi kujera na zauna ina mamakin hukuncin ubangiji na yarda da cewa Allah baya bacci kuma baya barin hakkin wani akan wani tun aduniya yake fitar dashi Hajiya Karima da 'kanwarta sun nufe ni da sharri sai gashi Allah ya mayar dashi kansu babu abinda zance da Ubangiji akan sakayyar da yayi min.

Mamma kuwa cewa "Tayi dama ai alhaki kyukoyo ne sukenan kullum cikin shirya mugunta gashinan Allah ya mayar dashi kansu Allah ya karemu yasa mufi karfin zuciyoyinmu." a tare muka amsa da ameen nida Jakadiya, Tace."Ki had'awa Sumayya ruwan wanka tayi ta samu karfin jikinta." Jakadiya da sauri tace"To ranki ya dad'e." ta kalleni a nutse tace"Kinga yanda Allah yayi musu ko." ? nace" na gani Mamma wallahi jikina duk yayi sanyi na rasa me yasa mutane suke shagala da duniya suke mantawa da Allah da ranar lahira wannan al'amarin da faru ya kamata ya zama izina ga masu irin halinsu."

A sanyaye tace" Sumayya kin san ita shiriya ta Allah ce sai yaso zaisa mutum ya shiryu amma idan ba hakaba ai yaci ace hajiya Karima ta gane gaskiya a lokacin da hukuncin rataya ya sauka akan d'anta Muddibo amma da yake beso ba sai ya rabu da ita ta cigaba da tafiya akan rashin gaskiya watakila wannan abu da ya faru da ita shine zai zama sanadiyar shiriyarta." A sanyaye nace"To ubangiji Allah ya shiryeta da dukkanin masu hali irin nata." Ta amsa da ameeen ya rabbi kije kiyi wanka sai kici abinci kisha magani." Nace."To mamma nagode da kulawarki akaina." murmushi tayi tace."Sumayya babu kalmar godiya a tsakanina dake dukkaninn abinda nayi miki kaina nayiwa.'' murmushi nayi na mike a nutse na kama hanyar dakin da nake, ina kokarin shiga jakadiya ta fito tace"Ranki ya dade na hada miki ruwan wankan na kuma fito miki da kayan da zaki sanya.'' nace"Sannu jakadiya nagode da kulawa." murmushi tayi ta wuce ni kuma na shiga dakin ina jin wani irin farin ciki a cikin raina insha Allahu karshen matsalata yazo zan cigaba da samun nutsuwa da kwanciyar hankali na har abadah.

*Na kudi ne*
Koda zaki ganshi a groups na sata ne idan kina bukatar ki biya kudin karatu ga yanda abin yake....Vip gruop#600 normal gruop#300 account.... 0542382124....Binta umar gtbank....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:28 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊�)
108

*Sumayya Allah ya baki lafiya👏🏻*

Bugun kofar da akeyi ne yasa na shiga tureshi daga jikina murya na rawa nace"Dan Allah ka saurara min haka kana ji fa ana bugu nasan Jakadiya ce tazo tayi aikinta dan Allah ka dagani kada Mamma ta fito.

Yana cigaba da abinda yake yace."Sumayya bazan iya ba ki barni kawai." kirjinsa na ture hawaye na kokarin zubo min nace" Dan Allah ka sauks." hannu yasa ya rufe min bakina ya kalleni da jajayen idanunsa kansa ya girgiza min alamun nayi shuru. kallonsa kawai nake ya mayar da kansa kirjina ya cigaba da sha'aninsa..........Jakadiya dai sai hakura tayi da bugun ta bar gurin, tana tsaka da gyare-gyare a falon Mamma ta fito daga dakinta ta shirya tsaf sai kamshi take, ta kalli Jakadiya a nutse tace" Sumayya bata fito bane."?

Jakadiya tace"Eh ranki ya dade na jima ina bugun kofar bata bude ba watakila bacci take." Mamma tace" To babu damuwa zuwa anjima sai a tasheta ta karya." Jakadiya tace"To ranki ya dade a kawo miki kayan karin nan gurin ko zaki hau daining din."

Tace."Kawo min nan jakadiya bana san hawa daining din saboda kafafuna." Jakadiya da sauri ta nufi gurin cin abincin ta shiryo komai a tire ta kawo gabanta ta ajiye.
A nutse ta hada mata tea kana ta zuba mata sinasir da miyar taushe wacce taji tantakwashi da man shanu! Mamma tace"Ikon Allah Jakadiya aiki baya miki wahala yanxu tashinki har kinyi wannan girgikin."? Jakadiya tai murmushi tace."Ranki ya dade ai jiki ya riga ya saba shiyasa aiki baya min wahala tunda na fahimci Sumayya tana san wainar shinkafa da sinasir yasa yau na shirya yi muku a matsayin abin karyawa.".

Mamma tace"Aikuwa kin kyauta Jakadiya mungode yau kam sai ki huta kada kiyi abincin rana wannan ma ya ishemu."

Jakadiya tace"To ranki ya dade godiya nake." gurin ta bari taje ta cigaba da ayyukanta.

Mamma ta gama karyawa jakadiya ta gyara gurin tsaf ta kunna tiraran wuta ta dawo ta zauna kusa da ita suka cigaba da hira.

Lawisa ce tayi sallama ta shigo tayi ado sosai tai kyau.! cikin sakin fuska Mamma ta amsa mata tace"Lawisa kece a tafe."?

Lawisa cikin ladabi ta samu guri ta zauna da fadin"Eh wallahi Mamma nice ina fatan na sameku lafiya."?

Mamma tace"Lafiya lau alhamdullilahi." Jakadiya ta gaisheta ta tashi ta basu guri.

Gurin ne yayi shuru na minti uku Mamma tace"Ina maigidan naki ne nasan yau dai baya fita da wuri."
Chapter 86 · 0% Book details