← Book details Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 8 OF 90

Sashe 8

Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Fulani murmushi tayi tana girgiza kanta cike da tsantsar farin ciki a maganarta tace"Ubana ina alfahari dakai mutuka ina jin dadin yanda kake kula dani da gudun 'bacin raina ina rokon Allah ya azurtaka da zuria masu albarka kamar yanda kake mana ladabi da biyayya kai ma ubangiji Allah yasa 'ya'yanka suyi maka.

Cikin sakin fuska ya amsa da ameen Mammana.! dama nace ina bukatar masu hidima a sashena domin wani sa'in hidima nayi wa Haruna yawa."

Cikin kulawa tace"Ayya ai wannan mai sauki ne ubana dama saboda nasan baka san hayaniya yasa na tura maka Haruna saboda nasan yana da nutsuwa amma insha Allahu zan sake turo maka mutum uku sun isa ko."? Yace."Yace mutum biyu ma sun isa sai su zauna su uku ina ganin hakan yafi" Tace."To shikkenan Ubana kada ka damu insha za'a turo masu hankali da nutsuwa.

***
Washe garin ranar bayan mun fito daga gurin karatu ni da Lahira muna tafe muna magana, Haruna yasha gabanmu yace."Sumayya Lahira kuje can b'angaran Fulani ana bukatar'ku.''

Kallonsa nayi nace"Haruna ina fata dai lafiya ba wani laifin mukayi ba." Yace."Babu komai ku kwantar da hankalinku sannan ba ku kad'ai aka nema ba har da sauran 'yan uwa.'' Ajiyar zuciya na sauke nace"Haruna dan Allah zan duba jikin babana kuje kawai na biyo bayanku daga baya."

Da sauri yace."Wai sumayya mai yasa kike gardama da umarnin masarauta akwai 'ya'ya da yawa da iyayensu suke halin rashin lafiya amma basa irin abinda kikeyi.

Hannu na d'aga masa nace"Haruna abinda yasa kaji nace haka sabida nike bashi magani yanzu haka Tambaya mahafiyata suna d'akin dahuwa(dakin girka abinci) suna aiki girka abinci kuma nasan idan naje bai zama dole a sallame mu da wuri ba shiyasa nace zan fara dubashi na bashi magani tukkuna.

Haruna yace."Ba za'a wani dad'e ba insha Allah kedai kawai ki shige muje." Girgiza kaina nayi na kalli Lahira dake rungume da jaka nace"Muje." Haruna gaba yayi da sauri muka rufa masa ba zuwa b'angaran Fulani.
A jere muka samu 'yan uwanmu bayi maza da mata sunja layi a bakin k'ofa kai tsaye 'bangaran mata muka nufa nida Lahira muka tsaya shi kuma Haruna da sauri ya bude kofar falon ya shiga ciku.....Surutai ne suka shiga tashi a gurin bayan shigar haruna falon dukkanin mu muna mamakin tara mu da Mammah fulani tayi sabida mun san da cewar ita din macace mai mutunci da karamci bata fiye tara mu taci mana mutunci ba kamar sauran 'bangarorin dake gidan, dukkanin mu dai addua mukeyi akan Allah yasa alkairi ne.

Haruna na fitowa muka bishi da kallo ya kalli 'bangaran maza da sauri yace."Ku shigo a nutse." Suka dinga shiga falon a nutse har suka qare, kusan mintina goma sha biyar da shigarsu suka fito kowa ya kama gabansa banda mutum biyu da suka ja gefe suka tsaya.

Haruna ya kallemu da fadin"Ku shigo a nutse." Da sauri muka tu'be takalman mu muka fara shiga daya bayan daya.

Zubewa mukayi a gabanta muna gaisheta.....Amsawa ta dinga yi cikin walwala tana kallonmu fuska a sake babu nuna 'kyama

A nutse ta dinga tambayar sunayenmu muna fad'a mata, ta d'ora idanunta a kaina fuskarta a sake tace"Sumayya ina tsammanin zaki fi 'yan uwanki kuzari da kazar kazar saboda haka ke kad'ai zan dauka a cikin ku zaki kasance daya daga cikin hadiman Magajin Sarki zaki dinga kulawa dashi da duk abunda yake bukata keda sauran 'yan uwanki amma su din maza ne Haruna da Isa da Hamza ke kad'ai ce mace a cikinsu."

Tunda take maganar gabana ke fad'uwa sam banyi farin ciki dajin wannan al'amarin ba ba dan komai ba sai dan sanin da nayi cewar bani da lokacin kaina na farko ina d'awaniyya da mahaifina na biyu ina kula da aikinsa dake cikin gidan ina nufin d'awainiya da dawakai, na uku kuma karatun dana k'wallafawa raina a kansa wanda ba kowane yake da ra'ayin yinsa a cikin masarautar ba, dama Maimartaba ya bude sashen karatu a gidan sabida mu, wanda yake da ra'ayi yaje ya dauki darasi na boko dana arabic wanda kuma baya da ra'ayi yayi zamansa to nida iyayena muna da ra'ayin karatu shiyasa suka goya min baya domun na samu ilimi yanzu haka mun kai izifi talatin a cikin al'kur'ani maigirma, sauran littafan addini kuwa nan ma mun sauke wasu 'bangaran boko ma ina fahinta sosai dan ina jin turanci amma ba sosai ba wannan dalilin ya sanya naji gabad'aya banji dadin a'lamarin ba

Cikin kokarin danne damuwata na kaskantar da kaina cike da ladabi nace"Godiya nake ranki ya dade hakika naji dadi mutuka da kika za'be ni a matsayin wacce zata kula da sashen Yarima ina rokon ubangiji Allah ya bani ikon daukar amanar da kika bani."

Cikin farin ciki Fulani tace."Babu damuwa Sumayya kuna iya tashi ku tafiya Haruna zai jagorance ku zuwa sashen nasa sai ku gabatar masa da kanku a matsayin wanda na turo ku.

A nutse muka mike mukayi mata sallama cike da ladabi muka fita daga falon, Haruna dasu Isa suna tsaye suna magana na kallesu fuskata babu walwala nace"Ku muje ko."? Haruna yace."Ke aka za'ba."? Daga masa kaina nayi na kalli Lahira nace"Dan Allah kafin ki shiga gurin ku ki duba babana ki bashi magani idan kuma Tambaya ta dawo shikkenan." Lahira tace"Kada ki damu insha Allah zan dubashi sai kin shigo.

Lokacin da muka isa b'angaran nasa a kishingid'e muka same shi cikin furanni yana sanye da 'kananun kaya gabansa kayan marmari ne cikin tire wayarsa yake dubawa fuskar nan a had'e! cikin zuciyata nace "Naga sanda zan ga dariyar guy nan kullum fuska babu rahama Allah dai ya kyauta."

Gabansa muka zube gwiwoyinmu a k'asa had'a baki mukayi gurin fad'in "Barka da hutawa Magajin sarki muna fatan mun same ka lafiya."! K'asa mukayi da kanmu bayan mun gama maganar.....

Shuru yayi mana kamar bai san damu a gurin ba, raina ya 'baci sosai aqallah mun kai minti goma a gurfane a gabansa kamar wasu masu neman gafara wannan wace irin rayuwa ce.

Kallonsa nayi a lokacin da yake kokarin gyara zama karaf! muka had'a ido kwarjini yayi min wanda yasa na ma'kale maganar dake raina nayi kasa da kaina gabana na fad'uwa guy ya tara duk abubuwan da ake bukata yana da kyau sosai gashi dogo abinda yafi birgeni a tare dashi manyan idanunsa wanda suke a lumshe k'wayoyin idanunsa basu cika fari ba sun d'an sirka da ja banta'ba ganin kwayar idanunsa tayi haske ba.
muryarsa ce ta katse min nazarin da nake.....
*BINTA UMAR ABBALE*

Shearing 👏🏻
2/11/21, 8:19 AM - ???: *'KWARYA TABI 'KWARYA*
*NA*
_BINTA UMAR ABBALE🍒_ *[email protected]*

*MANAZARTA WRITERS ASSOCIATION📘🖊�*
_'Kungiyar Masu Nazari da Aiki da Ilimi_
_________________________
*Littafin na kudi ne....!*
_#300.....0542382124...Binta Umar gtbank...idan kati zaki turo #400 ne sai ki same ni ta wannan numbers..08089965176 _07084653262 Zanyi miki bayanin yanda zaki turo katin.......... Ga masu bukatar VIP Group 600 ne_
_Mutanan Nijar zaku tura dala dari ta wannan numbers katin airtal ko orange VIP jakka d'aya 90899076_88137740_

*SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA''ATU S YARI*
(Kainuwa dasha Allah✊�)
15&16
Ganin yanda ya tsira mata idanunsa gami da sake tamke fuskarsa ya sanya jikinta yay sanyi tana jin tsoron ya tozarta a gaban wa'inda suke ganin kima da mutuncinta.........Cikin kokarin aro jarumta tace"Tunda nake a cikin gidan nan babu wanda ya ta'ba yi min musu akan umarnin da zan bashi sai wannan ba'kar yarinyar mai fuska irinta ba'kar akuya ta raina ni sosai sai kace ni din abokiyar adawarta ce, gabad'aya mutane suna gaisheni suna bani girma da mutuncina amma ita kokarin ratse ni take ta wuce ina ganin ko wane irin hukunci nasa ayi mata ya dace da ita sabida ta kasa mutunta ni."

Wani irin kallo yake min tamkar yana kallon abu mai muni! koda yake ban sani ba ko shima ya hango munin nawa da mutane suke fad'arsa wannan dalilin yasa da sauri na sunkuyar da kaina kasa zuciyata tana wani irin zafi! ta k'asan idona nake kallonsa sai ya mutsa fuska yake yana kare min kallo.

A dan sace na dago kaina muka had'a ido dashi! da sauri na kalli inda ya k'urawa ido a jikina.....Cikakken kirjina dake cike dana shanu naga yana satar kallon inda rigata ta yage, nasa hannuna da sauri na sake rufe gurin ina jin wani mugun haushinsa ni ban san meye a jikina ba da maza suke lalacewa gurin kallona, ni dai nasan bani da wani cikakken kyau ga shegen baqi sai kace me? ban sani ba ko nonowa na da suka rinjayi kirjina ne ke d'aukar hankalinsu ko kuma mazaunai na wanda suka cika bayana tamkar suyi magana ni kaina na san a fiska ban cika kyau ba amma na amince da cewar a jiki na cika cikakkiyar macan da kowane namiji yake bukata.

Da sauri na dago kaina ina kallonsa jin kamar yana magana cikin 'bacin rai! Aikuwa fad'a sosai yakewa Gimbiya Lawisa gami da nuna mata muhimancin mutun komai lalacewar dan adam tunda Allah ya karramashi to kaima sai ka mutuntashi." Gimbiya Lawisa cikin takaici take kallonsa sam bata dauka zai goyi da bayan yarinyar ba, ranta a 'bace ta bar gurin yaranta suka bi bayanta da sauri.......A nutse yace."Kowa ya koma bakin akinsa." Minti uku gurin ya watse kowa ya nufi inda yake....Hannuwansa na goye a baya ya tsirawa kasa ido yana kallo, cikin zuciyata nace"Anya kuwa wannan guy yana da lafiya gaskiya da matsala a tare dashi duba da yanda yake nacin kallon 'kasa sai kace wani makaho.
Rigata na dafe na yunk'ura da kyar na mike tsaye. nayi nufin shiga kofar dawakai naji maganarsa.
"Koma ki tsuguna inaso nayi magana dake." Da sauri na tsuguna tare da sunkuyar da kaina kasa.......sai da yaja dogon lokaci sannan yace.''Me yasa bakya mutunta Lawisa ko mahaifinki nada rawani a masarauta shiyasa kike gani tamkar daidai kike da kowa."
Chapter 8 · 0% Book details