← Book details Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 33 OF 90

Sashe 33

Kwarya Tabi Kwarya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Gani nayi tana 'boye wani abu a cikin zaninta sai na nuna kamar banganta ba na bude firji kayan marmari na shiga fitowa dasu, ina kallonta ta goge hannunta da tissue ta dauki tire din ta fita dashi.

Jingina nayi jikin firjin ina tunanin yanda zanyi na hanashi cin abincin nan nasan wani mugun abun ta zuba a abincin ganina yasa ta tsorata, ajiyar zuciya na sauke na cigaba da aikina, fruit salad na had'a masa nasa 'kankara a ciki yay sanyi daidai misali kana na shirya a kan tire........Inda yake zaman cin abinci na same shi a zaune yau 'yan wulakanci ne a kusa dan da gashi sai treequtar ko vest bai sanya ba, tire din ne ya kusa fad'uwa daga hannuna, tunda nake banta'ba ganin zahirin namiji ba sai yau sunkuyar da kaina kasa nayi dan ba zan iya kallon kirjinsa ba, tire din na ajiye kusa dashi da fadin"Ranka ya dade ga fruit salad din."
"Dauke kayan ki bana so" Da sauri na kalleshi. gira ya daga min nace"Naga duk dare kana sawa na hada maka ne." cikin tsawa yace."Bana bukatar naki.'' Gabadaya naji gwiwata tayi sanyi da irin wulakancin da yake min a sanyaye nace"Dan Allah kada kaci komai na Suwaiba wallahi tasa maka maganin cutarwa kada ka mance abinda ya faru da kai kwanakin baya." Wani irin kallon banza yake min....raina ya 'baci mikewa nayi nace"Kai na gaji wallahi! zanje na samu mahaifiyarka na fad'a mata ka'ki bani had'in kai bazan iya ba."! hanya na kama zan fita.
"Sumayya ranki sai ya 'baci mutukar kika je kika fadawa mahaifiyata wata magana."
Nace"To shikkenan idan baka so na fada mata kar kaci komai na Suwaiba."
"Sai naci dama nagaji da duniyar gwara na mutu sai kowa ya huta." Nace"Dan Allah kada kayi haka ka tausayawa mahaifiyarka da mahaifinka da masu kaunarka a masarautar nan.''
"Kinga ki daina wannan maganar babu wani mai kaunata a cikin masarautar nan sai iyayena idan kuma akwai sai ki fad'a."

Murya na rawa nace"Wallahi kana da masoya." jajayen idanunsa ya zuba min yace."Suna ina."? ganin yana min kallon tuhuma yasa na sunkuyar da kaina yace."Sumayya nafi bukatar na mutu na bar musu duniyar tunda na tsare musu guri." A sanyaye yayi maganar sai naji zuciyata ta karye na kalleshi idona cike da ruwan hawaye......'Kasa ya tsirawa ido yana kallo kai da kagani kasan yana cikin damuwa mai tsanani fatar saman goshinsa duk tattare saboda tashin hankali....a sanyaye naje na tsuguna gabansa.

*Na kudi ne*
Kika karanta baki biya ba Allah ya isa! idan kina so ki biya kudin littafin ga yanda abin yake....Vip #600 normal #300 accont...0542382124...Binta umar gtbank.....idan kati zaki turo #400 ne sai kiyi min mgn ta WhatsApp da wannan number
*07084653262*
*BINTA UMAR ABBALE*
2/11/21, 2:26 PM - ???: *SADAUKARWA NE*
*GA*
*HAJIYA SHAFA'ATU S YARI*
(Kainuwa dashan Allah✊�)
61&62
A hankali na kira sunanshi. Ya dago kanshi yana kallona kasa hada ido nayi dashi na sunkuyar da kaina a nutse nace"Dan Allah ka daina fadar wannan maganar Ubangiji baya so ya jarrabi bawansa ya dinga fadar maganar da bata dace ba, ka dauka abubuwan dake faruwa da kai jarrabawa ce daga rabbil izzati insha Allah sai dai suyi su gama amma baza zasuyi tasiri ba."
Idonsa a kafe a kaina har na k'are maganata, jin bece komai ba yasa na kalleshi, ganin kallon da yake min yayi yawa yasa nace"Ranka ya dade ka gafarce ni idan maganata ta 'bata maka rai."
Girgixa kansa yay yana jin sassauci a zuciyarsa a sanyaye yace."Nagode." nayi saurin kallonsa gira ya daga min da alamun sassauci a fuskarsa, wani irin farin ciki ya lullu'be ni naji dadi sosai da ya fara fahintata, nace"Me zan girka maka." "Komai." nace"Kafada dai." a yamutse yace."Bana jin ma zan iya cin komai a yanzu." a marairace nace"Ka daure dai kada ka kwana da yunwa." Kallona naga yanayi, nai mirmushi tare da sunkuyar da kaina kasa, yace."Cikina ciwo yake ba zanci komai ba." nace"To kasha fruit salad din." kai kurrum ya daga min. cike da farin cikin samun nasara na kwashe kayan abincin Suwaiba na fita dasu.
Can inda nake zubarwa na nufa..."Ke Sumayya wallahi tallahi kika zubar da abincin nan sai kin fuskanci hukunci mai tsanani." kallon banza nayi mata nace "ashe kin san kin zuba guba a ciki." ta tsira min ido bakinta na rawa. nace"Wallahi kika sake kika kai maganar gurin uwargida sai na tona muku asiri gurin Maimartaba ke dai kin san makomarki gwara ma kizo mu hada kai mu taimaki Yarima duk sanda suka baki guba kisa masa a abinci ki zubar tun a hanya." Suwaiba gumi ya shigo yanko mata tace"Ta yaya zan aikata hakan Sumayya kin san duk sanda suka gane bana aikata aikin da suka sani sai na fuskanci hukunci." kafadarta na dafa nace"Kada ki bari su gane kullum ki dinga nuna musu cewar kina iyakacin bakin kokarin ki idan ma sun gane ni nayi alkwarin kare ki daga zarginsu."
A sanyaye tace"Shikkenan dama nima cikin fargaba nake gudanar da aikin saboda ina tsoro wani abun ya samu Yarima wallahi tausayi yake bani." Nace"Ai abin tausayi ne duk sun tsane shi gabad'ayansu bayansa suke so su gani insha Allahu sai Allah ya kareshi daga sharrinsu.

Har yanzu yana zaune a inda yake kuma da alama be sha fruit salad din ba. kawai ya tsirawa guri guda ido a sanyaye nace"Ranka ya dade kasha fruit salad din." dago kansa yayi tsorata nayi ganin yanda kwayoyin idanunsa suka sauya, k'asa nayi da kaina ni kam na rasa gane abinda ke sanyawa idanuwan sa nayin ja.

"Sumayya ina bukatar ki rarrashe ni a yanzu bana bukatar komai sai rarrashi zuciyata a k'untacce take ina da damuwa babu abinda zan iya ci ko sha ki taimaka min."!!! Kallonsa nayi dan na kasa fahintar inda maganarsa ta dosa yana bukatar wanda zai rarrashe shi wane irin rarrashi kuma.

" Ranka ya dade bangane maganarka ba." murmushi yayi ya lumshe idonsa ya bude su a kaina "Ba zaki gane rarrashin da nake bukata ba."? kai na daga masa jikina na mutuwa da yanayin kallon da yake min........girgiza kansa yayi ya cigaba da kallon kasa.

Yanke shawarar tafiya nayi saboda na gane abinda yake nufi..." Ranka ya dade ka tashi lafiya." abinda na fada kenan na mike tsaye.

"Kada ki tafi baki rarrashe ni ba zuciyata na dab da tarwatsewa ki taimaka min kinji." kallonsa na dinga yi ina mamakin maganarsa.

"Ranka ya dade wane irin rarrashi zanyi maka kaje kayi alwala kayi nafila ka roki ubangiji zai yaye maka damuwarka nima nayi alkawari idan na koma gurinmu zanyi nafila nayi maka addua Allah ya kare ka."

Shuru yay yana kallona girgiza kaina nayi na cigaba da tafiya ina mamakin fitinarsa.....ina daf da fita ya tari gabana, gabana ya yanke ya fadi yau naga jaraba, sunkuyar da kaina nayi ina adduar rinjaye, hannuna ya rike ya rintse da nashi.

Rai a 'bace na kalleshi! kalar tausayi ya koma yana marairaicewa yace."Ki taimaka min kada ki tafi." naji kamar na kwada masa mari saboda takaici sarai nagane abinda yake nufi

"Ranka ya dade wai kai wane irin mutum ne dan darajar Allah da Annabi ka daina zuwar min da bukatarka tunda kasan ba samu za kayi ba."

Le'buna na naga yana kallo tsaki naja nace"Sakar min hannu na fita tunda baka san mutunci ba."!

"Ni kike fadawa wannan maganar."! rai a bace yayi maganar..." Ranka ya dade ka gafarce ni kai ka janyo.''
"Naji ni na janyo kuma nayi turr da zuciyata data kasa hakura dake banza k'azama kawai.''
" Duk abinda zakace naji na dauka ni dai bani hanya na wuce."'
"Sumayya ba zaki fita ba sai bukatata ta biya tunda na fahimci baki da tausayi to zan gwada miki karfi.''

Gabana na faduwa nace" Me kake nufi." ? "Ban sani ba." ya fada yana hararata, hannuna na fizge na tunkude shi zan fita.
A fusace ya juyo dani mari na yayi hagu da dama! na dinga kallonsa hawaye na zubo min..."Ki shige muje daki."
"Wallahi babu inda zani sai dai duk abinda zakayi min kayi." ina kuka nake maganar.
Matse ni yayi jikin bango yana kiss din fuskata, tureshi nayi ina haki!! yace.'"Ba zaki daina ture ni ba ko."!! takure jikina nayi ina kuka ina mamakin rashin adalcinsa wai duk irin abinda nake masa da abinda zai saka min kenan

Hannuna ya rike ya dinga jana wai lallai sai na bishi, turjewa nayi na tsuguna a gurin, tsugunawa yay ya dago fuskata na fizge ya sake kamo fuskar harshe yasa yana lashe hawayen dake zubowa.

A sanyaye yace."Wai meye abin kuka wannan abunfa taimakon kai da kai ne zakiji dadi nima zanji kuma babu wanda yaji ya gani dan Allah ki daina kuka kinji ko."

Fuskata na fizge nace"Kana cewa taimakon kai da kai ne waye yace maka ina bukatar wani abu!? sannan kana cewa babu wanda yaji ya gani to Ubangiji fa kasan duk abinda zamuyi yana ganinmu saboda haka kama daina wannan maganar idan kana son ka biya bukatarka dani ka aure ni."

"Baki da hankali ko."? a zafafe nace" Gaka nan babban mara hankali mai manta alkairi." kallona yake yana mamakin irin zafafan maganganun da nake masa.

"Ba zan aure ki ba saboda ke ba tsarana bace sha'awata kuma sai na kawar" yana gama maganarsa ya turmushe ni a gurin, kayan jikina ya yayyaga ya 'balle breziyar jikina, a gigice ya shiga wasa da kirjina....dukansa na shigayi ina haurinsa, tunda yasa Brest dina a baki yake sha nayi nayi na 'kwace ya'ki ya rike tam sai tsotsa yake yana lugudar d'ayan, wani irin hali na shiga na tashin hankali da tsananin sha'awa amma ban bari sha'awar tayi tasiri a tare dani ba, tureshi na cigaba dayi ina 'kokarin kwatar kaina.
Chapter 33 · 0% Book details